Showing 48001 words to 51000 words out of 214110 words

Chapter 17 - Bakar Ta'ada Complete hausa novel

24 Aug 2024

11100

ya juyar da auren ya zama alheri a gare mu baki daya, Allah ya amintar da mu akan abin da muke ta jin tsoronsa."
Hawaye ya k'wace masa, dukkanmu kowa ya fara kuka domin mun gane shi ma jarumta ce kawai da biyayya da kuma son yar'uwarsa ya sanya shi yin shahadar bawa Bulkachuwa aurena.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
Zaman bai tashi ba sai da aka tattauna yadda za'a yi wa Ubaida siyayyar kayan daki.
Ni kam an gama da ni tunda ya siyi muhimmai ga kuma freezer da tv bango, da bilanda babba, Honarable ya aiko a bani, da kuma kayan abinci da dubu dari biyu a Baba.
Ya ce ba zai samu halartar daurin aure ba tafiya ta taso masa.
A sadda kayan suka zo ba k'aramin murna na yi ba, domin ba karamin haska mini gidan Nura zasu yi ba.
Amma a yanzu me zan yi da su?
Idan na tuna Bulkachuwa zan aura sai na ji zuciyata ta harba da k'arfin gaske.
Ni dai ban fahimci me suka tattauna ba, nasan dai ya ce "Dubu Darin biyun da Kwamishina ya bashi bai ta'ba ko sisi ba hidimar aurenmu zai yi.
Suka gama aka tashi. Nazira ta zauna da ni dakin Gwaggo tana taya ni jimami domin akai akai take d'auke hawayen idon ta cikin dabarar kada na ga ni na sake karaya.
A daren wannan ranar na Kwankwatsa mafarki wai gashi nan an yi auren amma na sake zama y'ar firit na zama y'ar mitsitsiya ciwon yunwa da na zamani ya kwamushe ni.
A gigice na tashi wani abin mamaki jikina a jike na tashi tabbacin zufar da na ga ni a mafarki ce ta jike ni a zahiri.
Na rasa inda zan tsoma raina. Na kasa tashi na yi sallah na nemi zabin Allah.
Kawai na fi yarda na gudu.
Zuciyata ta buga da na tuno shekarar da za'a aurar da Yaya Ummi ta gudu wajen dangin mahaifiyarmu, da kansu suka dawo da ita, tare da bawa Babanmu ha'kuri. Tsananin da Gwaggo ta fuskanta kuma ba mai sau'ki ba ne domin dukkan gidan ce wa aka yi ita ta zuga ta, ita ta ce ta gudu.
Duk da ina yarinya kankanuwa amma ina tuna irin kukan da Gwaggo ta yi, tare da cewa duk abin da ya shafi al'amarinmu kada wanda ya sake, ya tafi danginta mu nemi dangin ubanmu dan sune a hakku akan mu ba danginta ba.
Jikina ya mutu to ina zan tafi ke nan?
Na numfasa ina tunanin gurin wa zani a Lame?
Wanda suka mana saura a can duk matsayin y'ay'a suke a wajen Dada ke nan ba wanda zai tirsasa ta.
Wanda zasu tsaya mini dama su Baban Tsakiya ne to su kuwa ai babu dausayin imani a ransu. Na tabbatar ma sune suka kitsa wananan fitsarin fakon dan kawai sun tsane ni.
Take na tuno Baba ta Bulkachuwa ita ka'dai nake da tabbacin zata fahimce ni, ta taya ni kubuta daga wannan auren da gara babu da shi.
Duk da ita ma bata da wannan isar. Amma dai zan gwada zuwa na roke ta ta zo ta rokar mini Baban Marina ya fasa bani Tijjani ya bani ko waye ni kuma zan kar'ba na zauna lafiya.
Nan da nan na samu salama a raina, gari ya yi haske na fito na yi uzzirina yau har da shan koko dan kuwa na samu sukuni.
Gwaggo ta shiga wanka na janyo bankina na bu'de k'wadon na dauko dubu uku.
Na mayar na rufee.
Na saka kayana kala biyu a leda da undis da hijabi daya.
Na boye a sakaden gado.
Daga haka na yi kwnaciyata ina jin raina fes.
Ba zato Baba ya leko ya ce "Yabi yau ki shirya ki je gidan Nazira".
Na amsa da "To Babanmu na gode".
Ai kuwa da'di ya kama shi domin yadda na amsa ya ji alamun sassauci a raina.
Na fito sanye da doguwar riga tsadaddiya cikin ireir kayan kwamshina.
Na yiwa su Gwaggo sallama na tafi.
Na shiga wajen Dada dan na gaishe ta.
Da Bulkachuwa na tarar da ita, suna zaune akan baranda cikin wani irin yanayi na rashin dadi da alamu suka nuna sa'insa suke yi mai zafi a tsakaninsu.
Ganina ya sanya ya yi shiru. Sai kuma ya mik'e ya ce "Asiya Toro wai da gaske ne Nuran ma ba za'a bari ya aure ki ba?
Kuma da gaske Baban Marina ya sake yarda da wannan almarar?"
Na kafe shi da idona da ya ke a kumbure kuma jawur.
Na tabbatar bai san juyin wainar da aka yi mini ba.
Ganin shirun da na yi, ga alamun tashin hankali shinfide a fuskata.
Ya tabbatar masa da gaske an runguza maganar aurena da manemi na a karo na uku.
Ya lailayo ashariya ya danna ya ce "Tabdi jam ahalin wannan gidan ba zasu ga ma'aiki ba, ba zasu ga dai dai ba."
Dada ta ce "Mai sunan manya ka iya bakinka fa! Kada ka zo ka rasa yadda zaka yi da kalaman ka".
Ya sake sakin wata maganar tare da ce wa "Bani na fa'da ba Dada. Annabi ne ya ce "matu'kar mutumin kirki da aka yarda da addininsa ya zo neman aure a ba shi. Hana shi kuwa yana nufin faruwar al'amura marasa dad'i!
Tunda aka hana Kwamshina aure nasan sai bacin rai ya biyo baya.
Yanzu kuma Allah ya kawo wani nagartacce sai a sake hana wa?
Ni yanzu da nake nema ake hana ni ashe ba kwa jin ciwo?
Akan me zaki zuba ido ahalin gidan nan su zama marasa daddako? Me yasa ba kwa yiwa kowa wannan al'amarin sai Yabi? Me yasa ba kya tirsasa kowa a cikin ya'yanki sai Baban Marina?
Me yasa aka mayar da shi k'arami marar yanci alhalin shine kuma babba?
Ya daga hannunsa duka biyu ya ce "Allah ka bani ku'di masu yawa ko dan na yi daraja a idon mutanan yau.
Wai ace a gidanku ma idan baka da komai sai ka zama wula'kantacce?"
Dada ta fashe da kuka amma ba irin na kururuwa ba.
Tana tafa hannu tana fa'din "Duk gatan da nake yi maka, duk soyayyar da nake yi maka ashe kai baka sona, baka yaba mini?
Me yasa ka raina kawunan ka?
To sune suka bada shawarar ayi hakan dan cigaban ka. Su suna son ka, amma kai kana wula'kanta su, kana kallonsu a bai bai.
Nan da nan ya kalle ni, ya juya ya kalle ta.
Kamar zai yi shiru.
Sai kuma ya ce "Wallahi yau kam sai kin fito kin fa'da mini dalilin ki na fa'din hakan, da kuma dalilin ki na ce wa saboda cigabana ake rashin adalci a gidan nan".
Ta kyabe baki ta ce "Sai dai ka je ka samu iyayen ka. Amma ba zaka zage ni ba, sannan ka ce sai na yi maka yadda kake so."
Ya kalle ta cikin ido ya ce "Na yi rantsuwa fa Dada".
Ita ma ta ce "Wallahi ba zan fa'da ba, sai dai ka dauko bindiga ka bindige ni".
Ya kalle ni ya ce "Asiya Toro kina da masaniya akan wannan shaguben tsohuwar?"
Na galla masa harara tare da tsaki hawaye kuma na kwaranyo wa a dukkan idanuwana.
Jikinsa ya mutu, bala'in da yake cinsa ya yi sanyi.
Na kalli yadda yake sanye da riga cukurkude a wanke amma babu guga.
Kansa ya sha dying ya zama brown.
Ga gajeran wando duk a yayyage wai kuma a hakan mai tsada ne.
Raina ya sake baci ta ya ya zan yi alfahari da wannan bawan a matsayin miji kuma uban ya'yana?
Gashi dai da dukkan zuciyarsa yake taya ni ba'kin cikin yankar bayana da ake yi, amma hakan bai sa na ga farinsa ba.
A hankali na ce "Dada ina kwana?"
Ta amsa da lafiya k'alau Yabi".
Na juya na fice, ina ce wa"Sai anjima".
Ya biyo ni yana ce wa "Asiya Toro tsaya ki fahimtar da ni mana, mene ne yake faruwa? Na yi miki al'kawarin wannan karon zan tsaya miki?"
Na sake jan tsaki na ce "Ni da kaina ne zan tsaya wa kaina. Kai har yaushe ka taimaki kanka, bare ka tsaya wa wata?"
Ya hauro ya ce "Ina matu'kar tausayin halin da kike ciki, amma ke na lura sam, ba ki san mutunci ba, ba ki san mai nufin ki da alheri ba".
Na sake jan tsaki na ce "In dai alherin ta sanadin ka ne bana son sa har abada".
Ya yi sukuri ya ce "Asiya Toro me yake faruwa ne, me ya susuta ki hakan, ba mun riga mun shirya ba?"
A hanzarce na ce "A gidan uwar waye muka shirya din?"
Ba zato kuwa ya kawo mini k'arfaffan mari na goce, amma ya samu gefen kunnena .
Yana huci ya ce "Duk rashin kunyar ki kada ki sake gigin yi mini zagin wula'kanci. Idan ba haka ba na rantse sai na illata ki.
Har cikin zuciyata nake jin damuwar halin da kike ciki, ashe Allah ne yasan manufar jaki da bai ba shi k'aho ba.
Da Honarable din ma ya aure ki irin ku ne masu kunyar nuna ahalinsu saboda tsananin butulci da k'ifadi.
A zafafe na ce "Ka jima baka illata ni ba.
Idan ni butulci da k'ifadi kake mini hasashe, kai kuma ina da tabbacin jahilci na damun ka, sannan kai din bara gurbin k'oyi ne a cikin zuri'a."
Ya sake hassala ya dunfaro ni, ko gezau ban yi ba dan tsananin k'insa da yake cina.
Na bu'de murya na ce "Ban da k'aton jahili wanne kato ne zai dinga d'aga wa mace hannu?
Na dire maganar da tsaki da harara tamkar manyan idanuwana zasu fa'do.
Jikinsa ya yi laushi, idanuwansa suka kad'a, ransa ya baci fiye da farko.
Murya babu amo ya ce"Asiya Toro me ya same ki ne, me na yi miki kike son cin zarafina haka siddan?
Da kinsan yadda muka kwashe da Dada a akan ki, da baki mini ko kallon banza ba, ina jin ki tamkar mun fito ciki guda ne".
Da yake akan tsinin kiyayyar auren sa nake sai ban ji kalaman nasa sun yi tasiri ba.
Na sake watsa masa kallon raini na ce "Ina ma cikinmu guda Tijjani? Ka ga da na kubuta daga bala'in hada ni aure da kai".
Nan da nan na ga ya kad'u. Tsawon sakanni ya zama tamkar mutum mutumi.
Ganin hakan da ya yi, ga shi ya kafe ni da ido babu kifta wa.
Ni kuma na yi tafiyata na bar shi cikin tu'ajjibi mai girma.
Ina tafe, Ina kuka har na isa gidan Nazira.
Ganina ina kuka bai sa ta tambayi dalilin zubar hawayen da nake yi ba.
Sai ita ma ta bar komai ta zauna tana kallon yadda na ke yin kuka mai hade da ajiyar zuciya.
Ina yi ina kallon yadda gaba'daya ta susu ce, alamun kukan zuci take yi da yafi nawa ciwo.
Tsawon lokaci muna haka.
Har mijinta ya fito ya same mu a hakan.
Ya zauna yana fuskanta ta.
Ya ce "Asiya na ji duk abin da yake wakana. Abin da nake so ki fahimta daya ne.
Ki fahimci duk wanda ya girmama sha'anin iyaye ba zai wula'kanta ba.
Duk wanda ya yi damarar yin aure saboda Allah, Ubangiji da kansa ne ya yi al'kawarin taimakon wannan bawan. Ki yi ha'kuri Asiya"
Ya yi shiru alamun alhini a dalilin kukan nawa ya sake tsananta, domin har cikin zuciyata nake tsananin ba'kin cikin a ce mini na yi ha'kuri na karbi Tijjani a matsayin mijin aurena.
Ya yi huci ya ce "Ki daure ki karbi auren nan saboda Allah, da kuma biyayyar aure ki ga yadda Ubangiji zai kawo miki dauki.
Annabi ya ce "idan mutum ya shiryu ta sanadinka yafi a baka daular duniya.
Tijjani mutumina ne, idan har an fahimce shi, an mutunta shi. Wallahi mutumin kirki ne, abu ne mai sau'ki ki sauya shi zuwa yadda kike so. Inda zaku samu matsala ki nuna bai isa ba. To anan ne zaki ga isar sa."
Na yi shiru, amma hawaye bai yanke mini ba, ina jin tamkar na ha'diye zuciya na mutu na huta.
Ta Yaya ban kasance fankashaliya ba, amma a dauke ni a bawa wanda ya saba cud'anya da mata daban daban?.
Ni ba rasa manema na yi ba, ba abin da yake d'aga mini hankali irin a gaban kowa, har a gaban Dada. Baba Maryo ta ce "Ba zata yarda a ba shi Nasiba ba. Duk yadda Dada take sonsa kuma bata matsa a ba shi ita a dole ba.
Sai kuma yanzun zata ce a ba shi ni?
Akan wanne dalilin?
Bansan a fili na yi maganar ba, sai da na ji Nazira ta ce "Saboda ke ba jikarta da y'arta mace ta haifa ba ne.
Saboda kuma ubanmu ba shi da abin duniya shi yasa zata tirsasa shi ko da baya so".
Mijinta ya kalle ta ya ce "Assha! Wacce irin magana kike yi haka ne? Maimakon ki rarrashe ta, ki k'arfafa mata guiwa ki kwantar da hankalinta sai ki sake jefa mata wasi-wasi?"
Cikin fishi mai yawa ta ce "Abin ne akwai tozarci a ciki".
Ya murmusa ya ce "Dukkan ku yara ne ba zaku fahimci muhimmimancin ha'kuri mussaman a fuskar zumunta ba sai a gaba.
Ba zaku gane tagomashin da mai biyayya yake samu ba sai a gaba.
Da ikon Allah watarana zata zo da Asiya zata ce Madallah da auren Tijjini indai ta sa Allah a gaban ta".
Ai kuwa yana rufe baki na takarkare na dinga zunduma ihu, ina fa'din "Ba zan ta'ba alfahari da shi ba, in sha Allah sai Ubangiji ya kawo mini sanadin da zan kubuta daga bala'in auren kazamin namiji kuma lalatacce".
Ya mike ya fita yana ce wa"Allah ya kawo mafita ta alheri Asiya! Ki yi ha'kuri, amma kada ki bari zuciya ta rinjaye ki, ki fa'da ba'kin ciki da ya zarta na auren Bulkachuwa".
Bayan ya fita da k'yar Nazira ta shawo kaina ta hilace ni muka ci abinci tare.
Muna sake tuna wariyar launin fatar da Dada ta dade tana nuna wa a tsakaninmu da jikokinta na wajen mata.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*

Hatta shi kansa Bulkachuwa ya fimu sake wa a gidanmu.
Haka nan akan idonmu zata raba musu abu nasu ya fi namu yawa. Ko kuma ta ce su sammana a hannunmu, ko ta basu ku'di su siyo abin da suke so irin na yara, amma mu ta ce mu tafi wajen iyayenmu mata su bamu.
Da la'asar na bar gidan Nazira na wuce gudan Yaya Ummi.
Da tausayi take ce wa "ki yi ha'kuri, na sani an yi wannan ha'din ne dan bamu da galihu, so ake dole uwarmu ta tabbata a cikin ba'kin ciki, ban da hakan ya'yan wa ake yiwa irin wannan musgunawar?
Haka nima aka yi mini, ina da wanda yake sona amma a ka ha'da ni da wannan tsohon da babu rabon komai a gidansa sai na haihuwa".
Daga karshe ta hakurkurtar da zuciyarta ta ce "Tunda Babanmu ya roki alfarmar ki amince, to kawai ki yi hakuri. Da ikon Allah ba za ki wula'kanta ba."
Na bar gidanta, ba dan na gamsu da shawararta ba, na sani Tijjani mutuminta ne. Ban da haka me yasa zata ce na ha'kura? Dan haka na yanke hukuncin gobe zan bar garin, gara na shiga duniya komai zai same ni, zai fi mini sau'ki akan na auri marar nagarta, wanda ake yi wa kallon biri boko.

Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*



✍️
[9/25, 3:39 PM] Hauwa Galadima: *WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE, BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*Regular 500
Vip 1k via
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.


*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*


Dukkan tunanin Bulkachuwa ya tsaya cak.
Tunda Yabi ta tafi ya kasa sukuni, sai ya koma da baya, cikin nutsuwa ya zauna kusa da Dada.
Ya sassauta murya ya ce "Na ro'ke ki, ki fahimtar da ni abin da ake shirya wa. Jiya na ga su Baba Shehu(k'anin mahaifinsa). Sun zo nan.
Tunanina bai bani komai ba, na yi zaton sun zo wuce wa ne suka tsaya dan su gaishe ki."
Ta ja tsaki ta share shi.
Ya sake lank'awasa harshe cikin ladabi, ya ce "Haba Dada ki yi hakuri mana, na ci alfarmar mai sunana".
Nan da nan kuwa ta ce "Kai din ne kayan kuttun ka yawa gare su. To aure suka zo nema maka, an kuma basu".
Ya dan zabura ya ce "wanne irin aure haka Dada? Wa na ce miki ina so da har zaki aika iyayena su zo, su nema mini?"
Cikin rashin damuwar yananyinsa ta ce "Na sani wacce aka baka din ba zaka yi watsi da ita ba, bata da mukusa, duk da dai guntu wa ce, amma jawur ce tamkar tsada, ga kyawuna ta samu domin kamarta nake sadda nake cikin k'uruciya ta".
Ya gintse ya ce "Dan Allah fahimtar da ni kawai".
Ta muskuta ta ce "Saboda soyayyar da kawunan ka suke yi maka suka yanke shawarar a baka Yabi, ni kuma na goya wa wannan kyakkawan kudirin nasu baya.
Dan haka ranar auren Nasiba za'a ha'da da naku, shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login