Showing 135001 words to 138000 words out of 214110 words
a fara komai da ni, sannan ni ce zan mata k'unshi da kitso.
Babah sai ina ka saka take yi da ni. Yadda ta ga na murje na yi kyau ba karamin da'di ta ji ba. Na sani kuma da a ce da goyo na je mata da tafi haka murna.
Shi da kansa ya kai ni. Washagari ya tafi akan sai nan da kwanaki ka'dan zai juyo. Komai sai da na bar masa, hatta miya sai da na soya masa, na yi masa cincin. Kawai tafasa farar taliya ko shinkafa zai yi sai kuwa shayi.
Ana gobe biki y'an Toro suka iso. Aka yi hidima cikin rufin asiri taro ya tashi lafiya.
Kwanaki biyu a tsakani ya zo muka tafi shake da kayan biki masu yawa.
Tunda muka yi aure bamu ta'ba nisa da juna ba sai wannan karon.
Duk da dai a Bulkachuwan ma ranar biki sai da ya faki ido ya jani muka je wani waje ya yi abin da zai yi sannan ya dawo da ni.
Amma muna isa gida ko hutawa bamu yi ba. Daki ya ja ni bamu fito ba sai da ya samu nutsuwa.
Da daddare ina zaune a cinyarsa sai ce mini ya yi "Little baki da nauyi, shafal ban ji kin danne ni ba".
Na zabura na kalle shi, gabana ya fa'di sosai. Da rawar murya na ce "Sai yau ka fahimci haka? Wa ka d'ora a cinyar da yanzu baka ji yadda kake so ba?"
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Ya daburce ya ce "Wallahi babu kowa Yabi".
Fa'din Yabi da rudun da ya shiga sai yasa na kasa gasgata shi amma kuma na danne na ha'diye saboda babu kyau zargi.
Duk yadda na so na bar maganar amma a zuciyata sai wasi-wasi nake yi. Na kasa samun nutsuwa. Hakan ya fara shafar walwalata. Ban sauya masa ba, ba kuma na bijire masa amma kuma babu shiriritar da nake yi masa a baya.
Rannan na ce masa ina son na je gida na yini. Da rawar baki ya ce "To, yaushe zaki je?"
Domin ya takura da rashin walwalata.
Na ce "Duk ranar da ka ce".
Ya ce "To gobe sai na kai ki"
Haka kuwa da kansa ya kai ni, muka fara isa k'ofar Dada muka gaisa. Tana ta barkwancinta da karatunta. Ban wani jima ba na tashi na nufi k'ofarmu."
Ya shigo suka gaisa ya ce mini zai tafi da yaushe zai zo ya d'auke ni?
Na ce "ko yaushe ma".
A k'ok"arinsa na son ya kyautata mini sai ya ce "Tom idan an idar da Isha zan zo".
Na ce "Allah ya kai mu".
Ya tafi. Na yini cikin iyayena cikin nutsuwa da walwala.
Da yamma lis Gwaggo da Inna zasu je duba yar kanwar Mama da ta haihu kusa da unguwarmu ne.
Dan haka Baban Marina ya ce "Asiya sai ku je tare ki rakasu idan kin dawo sai ki shige gidanki".
Na amsa da ce wa "To Babanmu, domin idam Gwaggo ta fita ba jin da'din zaman zan yi a dakin ni ka'dai ba, tunda Ikilima ta tafi Islamiya, shima kuma Baban fita zai yi. Mama kuwa babu wata ma'amala mai yawa a tsakaninmu.
Dan haka muka tafi tare. Da muka dawo na yi lungun da zai sada ni da gidana, su kuwa suka mik'e suka koma nasu gidan.
Haka kawai nake jin nauyin jiki na saukar mini. Wani irin b'acin rai ya ziyar ce ni da na karyo kwanar da na fara hangen gidanmu. Haka nake tafe ina ta jin fargaba. Ina kuma ayyana abubuwa marasa da'di a zuciyata.
Nan da nan na fara ta'awizi ina kore shaid'anin da yake son yin wasan kura da zuciyata. Har cikin zuciyata ina son Tijjani, ina son na rayu da shi. Domin a zaman da muka yi na shekara daya da kusan rabi na tabbatar yana da kyawawan dabi'u. Na farko shi mutum ne mai mutunta sallar farillah. Sannan mai yawan tsayuwar dare ne na shaida hakan. Domin duk lokacin da zai shafe yana tiritiri da ni da daddare, to da zarar k'arfe uku ta yi kuma zai tashi ya yi wanka. Ya yi ta yin munajati da Ubangijinsa, wani lokacin ya matsa mini na tashi, wani zubin kuma ya k'yale ni na yi barcina. Sau tari kuma idan ban tashi ba, da asuba idan ya tashe ni sai ya ce "Tashi ki yi sallar farillah akan lokaci, na raba dare ina roka miki alherin duniya da lahira my little".
Bayan hakan na karance shi yana da matu'kar son ya kiyaye ka'idojin da shari'a ta d'ora masa mussaman na ri'ke gida da kula da tarbiyata. Sannan ba shi da mugunta ko ka'dan har yau din nan Tijjani bai ta'ba saka mini ido akan ku'dina ba. Asalima kullum cikin k'ara k'auwame kansa yake yi da abin hannuna.
Sannan ya iya Soyayyar da duk taurin zuciyar mace sai ya dargaza ta. Ga kuma girmama iyaye, yana mutuntata manya kwarai da gaske. Wadannan dabi'un da ya siffantu da su ya sanya nake hakuri da inda yake kuskure mini, hakan ne kuma dalilin da yasa na k'i yarda na k'arfafa wa kaina zargin ko ya koma Bak'ar Ta'adar sa ta baya.
Na shiga zauren na ga kofar tamu a rufe ruf. Na fara tunanin ai ban fito da mukulli ba, tunda mun yi shi zai zo ya dauke ni.
Na zaro waya da nufin na k'ira shi ya zo ya bu'de mini, sannan na wuce k'ofar Maman Safiyanu na jira shi. Sai na jingina da k'yauren k'ofar ga mamakina sai na ga ta bud'u.
Na tura a hankali na ga sakata a ture tabbacin an saka bata shiga ba ne.
Na shigo a hankali. Amma sai na ci birki na tsaya cikin tsananin tu'ajjibi da mastanancin mamaki mai yawa.
Jikina ya d'auki b'ari, zuciyata ta yi nauyi ainun. Amma idona ya bushe k'amas.
Na saka hannuna na murtsike idanuwana da tunanin gizo yake yi mini, tare da fatan ace sak'e sak'en zuciyata ne da wasi-wasi irin na shaid'an.
Amma ina zahiri nake ganinsu. Tijjani zaune akan baranda yayin da Rafi'a take kan cinyoyinsa da manyan mazaunanta. Ta kwanta luf a kirjinsa, shi kuma idonsa na kan k'irjinta yana kallonsu. A zahiri iya abin da na gani ke nan amma zuciyata sai ta shiga wassafo mini cewar yanzu ma suka sanya tufafinsu.
Na ki'dima ainun, amma na kasa yin kwakkwaran motsi, na tsaya cak ina kallonsu tamkar mutum mutumi
K'arar faduwar wayata ne ya ankarar da shi.
Ya d'ago da fuskarsa ai yana ganina ya yi wani irin zabura ya wancakalar da ita, ta hantsilo ta fa'do kan guiwowinta.
A matu'kar rude ya k'araso gare ni.
Ya rasa mai zai ce, sai kawai ya zube a gabana guiwa bibbiyu. Ya ru'ko hannuna na kalle shi na ce "Tijjani gizo idona yake yi, ko mafarki nake yi?".
A ki'dime ya ce "Zan so a ce mafarkin kike yi Asiya".
Daidai lokacin Rafi'a ta zo ta shige sum sum tamkar k'wai ya fashe mata a ciki.
Na dinga jin tukukin ba'kin ciki da tashin hankali. Amma kuma idona a soye duk yadda nake son hawaye ya zubo mini abu ya ci tura.
Na sunkuya na d'auki waya ta na k'wace hannuna na yi d'akina ina jin jiri na katantanwa da ni.
Kai tsaye na hau cire rigar cikina domin zafin da nake ji a zuciyata har jikina yake kutso wa. Zufa sai yanko mini take yi.
Na cire komai na d'aura zani. Na zauna amma ban daina jin zafin jiki ba.
Na fita har lokacin yana durk'ushe a inda na bar shi.
Na dauki botiki na nufi rijiya. Da azama ya tare ni, ya ce " Bana hana ki jan ruwa da kan ki ba?".
Ban ce komai ba na matsa gefe ya janyo mini ruwan. Ya kinkima ya kai mini band'akin.
Na shiga na yi wanka. Amma dana fito ina goge jikina da tawul, zufar na sake keto mini.
Na dauki rigar barci marar nauyi na saka, bayan na saka gajeran wando ta ciki. Na d'aure kaina da dan kwali mai taushi.
Kicin na fa'da na hau girki, ina yi ina hailala. Gaba'daya jina nake yi tamkar ba ni ba. Na yi matu'kar kad'uwa da abin da na ga ni a cikin gidan aurena.
Ban san falalar kuka ba sai a yau, domin gaba'daya hawayen ya k'i zuba.
Shi kuma ya takure, a gefe tamkar ka ce k'yat ya zura a guje. Cikin lokaci k'alilan nadama mai tsananin gaske ta bayyana a dukkan jikinsa. Ya kasa sukuni, da alamu kunya ce ta hana shi sukuni. Tunda ni dai ban bu'de baki na ce masa komai ba.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
✍️
[10/4, 5:26 PM] +234 806 878 8989: 67&68.
Na daskare a zaune, wato duk tantirancin namiji shi kamila yake so.
Duk yadda zaki sadaukar masa da komai da sunan soyayya shi fa a zuciyarsa ba haka ba ne.
A yau na k'ara fahimtar darasin rayuwa. Na kuma k'ara gode wa Allah da na tsallake sirad'in yanmatanci lafiya.
Na kalle shi cikin tu'ajjibi na ce "To ka sani Wallahi bazan zauna a cikin gidan nan ba. Matu'kar kana son kwanciyar hankali da walwala to kuwa bana son gidan, ba kuma zan zauna a cikinsa ba."
A rikice ya ce "Asiya kin san dai da yadda aka biya ku'din rabin shekara yanzu wata guda tal muka yi, ta ina zan fara neman wani gidan?"
Ido cikin ido na ce "koma ta ina ne, na baka nan da sati if not Bilhiillazi bazan ha'kura ba. Sai dai ka nemi ni ka rasa shike nan sai ta tattaro ta maye maka gurbina."
Ya yi muk'us ya kasa zaburo mini.
Ya nisa ya ce "Haba little nan da sati me zan yi na samo ku'di? Kin san dai ba dawo mini da kudin zasu yi ba, bare na kama wani".
Na ce "Sai na baka aro, ka karbi zobena ko dan kunne ka siyar, sai ka biya ni idan ka samu hali".
Ban san ya aka yi ba kawai ya fara nuna ni da yatsansa cikin sababi yana fa'din "Nafi karfin ki kama gida na zauna a ciki Asiya. Ba zan yi wannan lalacewar ba, har abada da ikon Allah."
Na kafe shi da ido tsawon lokaci har ya fara kame kame. Na nisa na ce "Tijjani ni kake yiwa wannnan shouting din?".
Na girgiza kai na ce "Ba laifin ka ba ne. Laifina ne da na yarda da afuwar da Malam ya yi maka ba tare da na bayyana tozarta ni da ka yi ba. Afuwar da aka tilasta ni na yi maka ne ya baka kuzarin yi mini sababi irin haka ko?
To Wallahi bazan zauna a gidan nan ba. Komai za'a yi da ni kuwa".
Na mik'e na bar shi, ya yi shiru tamkar ruwa ya cinye shi. Domin ya ga na koma Yabin Marina marar sassauci.
Ban jima da shiga d'akin ba sai ga shi ya biyo ni jikinsa a sanyaye. Ya zauna kusa da ni ya tausasa harshe ya ce "Ke little ba ki fahimce ni ba ne. Ki yi hakuri, zamu tashi, amma pls ba nan da sati daya ba dan Allah."
Na ce "To".
Ai kuwa nan da nan ya hau fa'din "Na rok'e ki fa Little. Ban son irin wannan to din na ki".
Na share shi. Ya dinga jaye-jayen magana amma ban tanka masa ba.
Sai kuma ya bani tausayi yadda ya yi shiru ya rasa abin yi.
A zuciyata sai hango girman gatan da Ubangiji ya yiwa mazaje nake yi. Domin duk girman laifin da zasu yi wa mace sai Ubangiji ya sanya hakuri da sassauci had'i da rauni a zukatan mataye. Nan da nan mace zata yafe ta kuma manta musganwar miji.
Na tuna ranar da ya rufe mini gida dan kawai na je na na yi sana'ar da zan samo masa ku'din da zamu rufa asirinmu. Amma har washagari yana sababin sai na tafi gida.
Amma ni na fita unguwa na dawo na tarar yana shek'a ayarsa. Na girgiza kai domin nasan da ace ni ya ga ni a cinyar Yaya J sai ya masa dukan mutuwa tunda ba k'arfinsu daya ba. Ni kuwa zai yi wahalar gaske idan bai sallama ni ba.
Na kalle shi na ce "Na tambaye ka?"
Ya d'aga mini kai tabbacin eh.
A hankali na ce "Idan ni ka ga ni a cinyar wanin ka ya zaka ji?"
Ya ce "Wata'kila zuciyata bugawa zata yi, wata'kila kuma na had'u da mummunan hawan jinin da zai kanannad'e ni."
Na sake zuba masa ido na ce "Amma me yasa baka yi zaton nima sakamakon hakan zai iya samu na a dalilin ganin wata a jikin ka ba?"
Ya fara sosa k'eya. Da k'yar ya ce "Ban san ya aka yi hakan ta faru ba. Ni gaba'daya am upset ma".
Na girgiza kai na ce "Hmmm".
Muka yi shiru sai kuma na ce "Kuma zaka zauna da ni idan ka gan ni a irin yanayin da na gan ka?"
Ba ja in ja ya ce "Ba zan iya ba".
Na zuba masa ido ina masa kallo mai tsananin gaske.
Na kaurara murya na ce "Amma kuwa son zuciyar ka azimin ne Tijjani."
Bai yi inkari ba. Bai ce komai ba, na kuma tabbatar da dukkan zuciyarsa ya bani amsar.
Kamar daga sama sai na ji ya ce "Mace daraja ne da ita sai wacce ta wula'kanta kanta. Duk matar auren da zata bada k'ofar da wani namijin zai mata waya, ko doguwar gaisuwa dama ai ba kamammiya ba ce. Ba kuma yadda za'a yi mijinta ya gasgata ta. Bare kuma a ce har ya ga ni da idanuwansa, tabbas ba zai zauna da ita ba, ko kuma idan ya ri'ke ta din ma bisa wani dalilin to fa har abada ba zata ji dadinsa ba."
Na sassauta na ce "Amma shi namiji idan yana sharholiyarsa ko da kuwa a cikin gidan aurensa ne dole ne matar ta yi hakuri ta zauna da shi ko?"
Ya kasa amsa mini.
Na zarce da ce wa "Ana rudarku da cewa duk abin da namiji ya yi ado ne, na mace ne kaico. To ka saurare ni da kyau abin da zan fa'da ka sani sai dai zan sake yi maka matashiya ne na kuma kafa maka hujja tunda yanzu ka sanya an tursasa ni na yafe maka.
Laifin namiji baligi da na mace baliga a banagaren barna duk daya ne a fuskar addini tunda duk hukunci iri d'aya Ubangiji ya zartar.
Al'amari irin wannan kuma bashi ne in ji Annabin Rahma. Idan mutum ya bata y'ar wani, shima za'a bata tasa. Idan ka yi da matar wani, kai ma za'a yi da taka.!
Na kaurara murya na ce "Na yarda baka yi zina ba Tijjani. Amma kana kusantar ta. Kana bin hanyar da ta bi. Ka sani kuma Allah da kansa ce wa ya yi kada mu kusance ta, ba wai kada a aika ta ba. Ina ro'kon ka, ka daina kusantar ta bare tsautsayi ya sanya ka fa'da yin ta da auren ka. Ina jin tsoro da zullumin kada na fara haihuwa a b'ata mini yara. Ina cikin fargaba kada laifin ka ya jefa ni cikin had'arin a lalata ni da aurena".
Ya zabura ya ce "To y'ar sarkin mugun fata da jawo bak'in alkaba'i."
Na kalle shi na ga ya shiga rud'u a dalilin furucina sosai. Kishinsa ya bani mamaki ainun.
Ban ji d'ar ba na ce "Gaskiya na fa'da maka, wacce Annabi ne ya fad'a tun gabannin kakaninmu su iso duniyar.
Bayan haka kuma ina son ka sani laifin da ka yi tabbas na ha'kura. Amma ina tabbatar maka idan na sake kama ka da irin wannan laifin to fa ka sani ka kuma ri'ke a zuciyar ka ba zan sake zama da kai ba Wallahi".
Ya matso kusa da ni ya rungume ni sosai yana fa'din "Da ikon Ubangiji bazan sake ba Asiya. Ki taya ni addu'a. Ina kuma ro'kon ki sake hakuri, ki shafe wannan al'amarin a zuciyar ki. Wallahi summa Tallahi iya abin da ya faru ke nan, kuma a wannan ranar na ta'ba yin hakan, kada shaidan ya rinjayar miki ce war na saba yi din ne.
Na kuma fahimci Ubangiji ya so ni da alheri ne shi yasa ma asirina ya tonu."
Na saki ajiyar zuciya mai nauyi na ce "Shike nan Allah ya yafe mana gaba'daya."
Ya sake ri'ke ni sosai yana fa'din "Na gode sosai, Allah ya sanya ki cikin bayinsa da yake kar'ba daga gare su."
Hawayen da ban san dalilinsa ba ya dinga zuba mini.
A hankali na ce "Ameen".
Shike nan muka rufe maganar. A ranar ma mutum uku suka zo lalle amma hakuri na basu da gabatar da uzzirin ban warware ba. Domin gaba'daya na rasa karfin zuciyata. Rauni mai yawa nake jin yana bina. Sannan wata irin karaya da al'amarin Tijjani ya haifar mini da gajiya da kasala masu nauyi a zuciyata wanda gangar jikin ta rasa k'arfi da kuzari.
Bai ce komai ba. Amma jikinsa shima ya mutu domin ya fahimci k'arfin halin da nake yi iya gangar jikina ne kawai.
Da daddare ya ri'ke ni, ya dinga rarrashi, da ban baki irin wanda sai masanin falsafa ne zai dinga harhada kalaman masu nauyi a mizanin masalaha.
Na amsa da ce wa "Na ha'kura da gaske."
Ya ce "To me yasa ba zaki y lalle ba Asiya? Na sani kuma ke ma kin sani, rufin asiri ne mai yawa sana'ar taki take yiwa jama'a."
Murya na rawa na ce "Zuciyata ta karye, jikina babu k'wari."
Sai kuma na ke ce da kuka fiye da wadda na yi a gabansu Malam.
Ya kasa ce wa komai tsawon lokaci mai yawa ina kukan, shi kuma yana shafata tamkar jinjira.
Na jima ina kuka bai hana ni ba. Har sai da kukan ya tsaya cak dan kansa. Na koma ina ajiyar zuciya mai d'auke da shesshek'a.
Ya sassauta murya ya ce "Kin