Showing 120001 words to 123000 words out of 131968 words
da namiji kyawawan gaske farare tas masu kama da ubansu fari irin na fulanin Yola wai zokuga murna gurin D.S anyi yaya shine yayi musu huduba da Zulaiha da Kabir aka mayarwa da Hajiya chibinar ta sannan yasa wa namijin sunan mahaifinsa aikuwa yaran sunga gata amma shi yayi musu inkiya da Nawwas da Nawwarah ranar suna tazo akasha bidiri abu gwanin sha'awa har kuka Umaimah tayi saboda gatan data samu gurin danginta da dangin mijinta goga Hameed ma da Daddy ya tura masa hoton yaran yayi murna sosai yaji qaunarsu har cikin jininsa ya rinqajin dama shi ta haifawa yaran bayan taro ya watse da kwanaki uku suna kwance da Sulaiman aka kirashi a waya ake fada masa anyi musu rasuwa a Adamawa qanin mahaifinsu ya rasu yaji mutuwar sosai don zaune ya tashi ya hada kai da gwiwa daqyar ta lallabashi suka kwanta da asuba ya tashi ya shirya lkcn har qaninsa Nura yazo daukarsa zasuyi sammako itadai Umaimah hakanan tarinqa jin gabanta na faduwa daqyar ta bari yayi kissing yaran ya rungumeta a jikinsa ya fita har ya fita ya dawo ya kirata ya janyota jikinsa yace “amana nabar miki yarana ki rayu dasu cikin aminci inasonki Umaimatu".........
*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*
[2/3, 8:45 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_*
Duk da faduwar da gabanta yakeyi hakanan ta qwaqulo murmushin qarfafa gwiwa tace dashi “zaka dawo ka samemu cikin amincin Allah" yayi murmushi tare da kissing din bakinta ya fita da sauri suka dauki hanyar Adamawa.
Ta jima a tsaye a gurin daya tafi ya barta tana jera masa addu'ar dawowa lfy kafin ta koma cikin gdan lkcn twins dinta sun tashi dake tanada meyi mata raino ta basu sukasha ta miqa Mata su ita kuma ta kwanta har yanzu ciwon jikin haihuwar bai saketa ba sannan D.S ya kuma tara mata gajiya da D.S da Hameed batasan waye yafi wani jaraba ba sauqinta daya shi baya dadewa kuma penis dinsa batada girman ta Hameed amma jiya ta fada duk da bai shigeta ba saida yasan yanda yayi ya samu gamsuwa da ita sosai.
Wajen qarfe daya taji wayarta tana ring ta shiga dakin da sauri ta daga ta kara a kunnenta tace “Allah ya taimaki mijina badai har kunje Yola ba naga tfyr da nisa sosai” ajiyar zuciya taji anyi gabanta ya yanke ya sake faduwa kafin tayi mgn aka katseta da cewa “matarsa ce ke?" Cikin in...Ina da tashin hankali tace “a...eh ni... Ina matarsa ce" me mgnr ya kuma cewa “sun samu hatsari ne a hanyarsu ta zuwa Adamawa amma yanzu haka suna asibitin qashi na dala shine yace a kiraki a fada miki” wani salati ta saki tace “way... wayyoh Allah... Ni Umaimatu amma dai bai mutu ba ko?"
Bata iya jiran amsar dazai bataba ta kashe wayar cikin tashin hankali ta durqushe a gurin qirjinta yana tsananta bugu jikinta yana wata irin rawa daqyar ta iya sake daukar wayarta ta kira Daddy tana kuka tana cewa “Daddy Abu Nawwas Daddy karya mutu don Allah ya barni ka hanashi mutuwa Daddy..." Saurin katseta yayi da cewa “ya salam waye ya fada miki Umaimatu bafa shi bane qaninsa ne" Allah sarki baiwar Allah sai kuwa ta sauke ajiyar zuciya tace “Allah na gde maka daba mijina bane" hawaye Daddy ya share cikin rawar murya yace “ki... Kiyi hqr haka Allah ya tsara miki ga Hajiya nan zuwa da yayarku Zahrah zasu tayaki zama kafin yaji sauqi a dawo dashi kada kice zaki fita daga gdan nan" yana fadin haka ya kashe wayar bata samu damar yin tunanin komai ba taji shigowar motoci gdan aikuwa batasan sanda ta zabura ta miqe tayi waje a guje ba ambulance tagani da qananun motoci uku tayi wajen ta tsaya tana rarraba idanu kamar mahaukaciya zuciyarta takasa tuna komai Daddy da Abba mahaifin Sulaiman taga sun fito sai wata motar Dawood ne yayan Sulaiman da Nazir qaninsa dayar kuma Hajiya Sa'adatu ce da qannansa mata biyu sai ma'aikatan asibitin da suka fito suka bude ambulance din suka janyo wani dogon abu da mutum kwance akai jini sai diga yake ta qasan gadon daukar gawar.
Daddy yana qoqarin riqeta amma ina da tayi wata alkafura ta dira gabansu kafin su ankara ta janye yadin da aka lullubeshi ta matsa ta qara kallon fuskarsa da gaske ba gizo ba Sulaiman ne kwance babu numfashi a jikinsa fuskarsa wasai da murmushin sa na rahama ta dafe qirjinta tare da furta Innanillahi wa innah ilaihirraji'un tayi baya luuuuuu ta zube a qasa itama qanwar gawa da sauri Daddy da Hajiya sukayo kanta aka dauketa itama aka shiga da ita ciki aka kwantar da ita a gado babu irin ruwan da basu yayyafa Mata ba amma taqi dawowa hayyacinta hakanan aka kimtsa Sulaiman aka daukeshi aka kaishi gdansa na gsky zuciyoyi na kukan rashin managarcin mutum salihin bawa wanda bashi da tamka Hajiya Sa'adatu fadi takeyi.
“Wlh babana da nasan mutuwa zakayi da bazan takura maka kaje gaisuwar nan ba saida ka nunamin bakason tfyr na takura maka dake kaidin dane me biyayya haka ka tafi yanzu ka mutu babana ka mutu kabar matarka abar qaunarka ka mutu kabar yayanka masu kwanaki goma sha daya a duniya ka mutu ka barni kabar yan'uwanka kabar abokanka kabar kowa babana wayyoni kaina wayyoh Umaimatu dole ki suma kinyi rashi Umaimatu wannan mutuwa takice ke akayiwa mutuwa kin rasa miji me sonki da qaunarki kin rasa miji me tausayinki dason farin cikinki Umaimatu Allah ya mayar miki da alkhairi Umaimatu na rasaki yanzu kenan na rasa sukura ta qwarai wadda ta ginamin dana da tsarkakkakiyar soyayyah Allah na gde maka da baka dauki rayuwar Sulaiman ba saida ka cika masa burinsa na ganin yayansa"
Bayan ankai Sulaiman makwancinsa aka dauki Umaimah aka tafi da ita asibiti tashin hankalin dasu Daddy basu taba shiga wannan karon shi suka shiga ba akan Umaimah yau shi suka shiga Umaimah ma da ciwon zuciya wannan wacce irin jarabta ce suke fuskanta ne.
Bata samu kanta ba saida tayi kwanaki bakwai saboda kumburar da zuciyarta tayi twins kuwa sai madara ake basu bayan ta dawo hayyacinta mutuwar mijin nata ta dawo mata sabuwa tayi kuka kamar ranta zai fita tanajin dama ita ta mutu ta huta daqyar Hajiya ta shawo kanta da dadadan kalamai da misalai kwatankwacin nata da kuma irin nasarorin da zata iya riska a rayuwarta da wadannan kalaman Hajiya da Daddy sukayita kwantar mata da hankali amma duk sanda ta kalli Nawwas da Nawwarah sai tayi kuka saboda tunawa da kalmarsa ta qarshe yayana amanane a gareki inasonki Umaimah” wannan dalilin taci alwashin zata tsaya ta riqe masa amanar yayansa koda kuwa zata mutu babu aure ita aurenma ya fita a ranta tama hqr dashi gara ta zauna tayi rayuwarta ita kadai tunda bai karbeta ba.
Haka su Hajiya suka tafi da ita gda aka gyara mata dakinta aka zuba mata komai sabo duk wani abu da zai cire mata kewa saida suka sanya mata ga mai rainon twins dinta ita dakinta guda sannan ga Maliha da Shuraif da suke dauke mata kewa lkcn Allah yasa cikin hutu suke koda aka koma mkrntar ita bata komaba saboda abin na gdane ita daluba ce shi kuma marigayi D.S malami ne da sukeji dashi a Skyline University sunji mutuwarsa sosai hukumar makarantar tayi rawar gani sosai wajen ganin sun yiwa iyalan D.S wani abu aikuwa sunji dadi koda akazo rabon gado da Abba da Hajiya Sa'adatu cewa sukayi sun yafewa Umaimah da yayanta komai.
Rayuwar haka taci gaba da tafiya bason raiba sai bayan wata uku da rasuwar D.S sannan Daddy ya sanar da Hameed ya tausayawa twins tare da jin ninkin qaunarsu a zuciyarsa yasan rabonsu shine ya rabashi da mahaifiyarsu sannan rabonsa dabai qare a jikinta ba shine ya kashe mahaifinsu" da wannan tunanin ya biyo jirgi ya dira a 9ja batare daya fadawa kowa ba suna zaune a parlour da hijjab dinta na masu takaba ya shigo da sallamarsa Maliha da Shuraif sukayi tsalle suka rungumeshi Twince kuwa da suke koyon zama sai bangale masa baki sukeyi murmushi yayi me hade da kwallah yana tuna irin wulaqancin daya rinqa yiwa mahaifinsu lkcn da yana neman auren Umaimah ya sunkuya ya daukesu ya rungumesu a jikinsa wani kuka me qarfi ya kwace masa yayi saurin tashi daga gurin ya shige dakinsa da yaran ko gaisawa da Hajiya bai iya yi ba balle Umaimah tasaran zaiyi mata ta'aziyyar mijinta, itama batasan sanda mikin mutuwar D.S ya dawo Mata sabo.......
*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*
[2/3, 11:53 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_*
Miqewa tayi ta shige dakinta ta kwanta tanajin haushi da tsanar duk wanda ya kasa yi mata gaisuwar rashin mijinta da takejin bazata mayar da kamarsa ba a duniya.
Shima ya jima yana kallon Nawwas da Nawwarah yana kuka yaran sai wasa sukeyi da gashin qirjinsa sunayi masa dariya kamar Nawwas da mahaifinsa har tayi yawa kamar dai shida Shuraif abubuwan da yayiwa D.S suna sake bijiro masa musamman haduwarsu ta qarshe lkcn mutuwar Nihal da Shurafah da yazo daukarta yana ganinsa yana miqa masa hanu ya bige hanunsa ya wucce hakan baisa yaji haushi ba washe gari ma daya dawo karba mawa Umaimah yajin daddawa lkcn da cikin yaran saida ya sake miqa masa hanu da yaqi bashi nasa kawai sai yaga ya share qwallah ya rungumeshi yace.
“Kada ka qullaceni a zuciyarka Yaya banine na rabaka da Umaimah ba qaddara ce kuma nima itace ta hadani da ita wlh da inada ikon halatta maka Umaimah tun kafin muyi aure zan halatta maka ita saboda nasani kaine Umaimah takeso kaima kuma ita kakeso amma Ina banida damar hakan abu dayane zai hanani dawo maka da Umaimah saboda ina burin rayuwarta ta samu farin ciki Hameed ka qaddara idan Umaimah rabonka ce zata dawo gareka amma bayan qasa ta rufe idona saboda a tsarin rayuwata mace ko cutar dani take indai bazata cutar da Umaimah ba zan rayu da ita balle Umaimah da kullum burinta farin cikina Hameed idan na mutu bana fatan kabar Umaimah ta auri wani bakai ba saboda Ina kishinta kuma nasan zaka riqemin dana saboda kanada imani kuma kanason uwarsu"
Yana fadin haka ya sakeshi ya shiga motarsa yaja yana daga masa hannu yanayi masa murmushinsa me tsayawa s zuciya “kyakkyawan namiji me kyakkyawan hali da sanyin zuciya ya mutu" ya fada yana rungume yaran a jikinsa yace “dole Umaimah tayi kuka saboda tayi rashin miji na qwarai amma nasani bazai fini sonta ba kuma zanyi iyakar qoqarina naga na bata farin ciki fiye da wanda yake burin bata zan riqe maka yayanka kamar nawa har qarshan numfashina Sulaiman Allah ya gafarts maka"
Yana mgnr yana kuka da shishi kamar qaramin yaro tunda yake baitabajin mutuwar data girgiza shi kamar ta Sulaiman ba ko mutuwar yayanss biyu batayi masa dukan mutuwar Sulaiman ba musamman idan ya kalli yaran sai yace “yanzu fah yanason rayuwa dasu Allah ya karbi rayuwarsa ko? Meyesa a duniya mutanen kirki basa dadewa?" Ya tambayi kansa tare da kwantar da yaran da sukayi bacci a gefensa ya ja blanket ya rufesu ya tashi ya dauro alwala yayi sallar Isha yayi shafa'i da wuturi yaci gaba da addu'a rabin addu'ar tasa ga Sulaiman ne yana kuka yana roqon Allah ya bashi hqr da kyawawan halaye da kyakkyawar mu'amala irinta Sulaiman.
Bayan ya gama ya fita ya nufi kitchen domin dauko fresh milk sukayi clear da ido ido cikin ido amma sai ta dauke kai duk da ramar da tayi amma kyawunta yananan rabawa tayi ta gefensa ta wucce yabi bayanta da kallo bakinsa ya kulle ya kasa yi mata mgn gaisuwa yakeson yi mata amma ya kasa harta shige dakinta sannan ya juya kamar wanda kwai ya fashewa a ciki ya dauki madarar ya fita ya koma ya zauna gabansa na faduwa yana korar shaidan saboda yanda yake qawata nasa surar qanwar tasa bayan tana cikin halin takaba wanda ko kalma ta so baa so ta shiga tsakinsu hakan wani zunubi ne me girma.
Itama tana shiga ta kwanta badon tayi bacci ba saidon ta bawa zuciyarta hutu da tunanin mijinta Sulaiman daya kasa gogewa a ranta tanason taji yayanta a kusa da ita amma babu dama taso tambayar sa yaranta amma tana tsoron tujararsa don tasan ba mutunci ya cika ba bare yau da take ganinsa duk a firgice da haka dai bacci ya dauketa tunda ba sallah zatayi ba sai asuba ta tashi tayi wankan tsarki tayi sallah sannan ta gyara jikinta ta koma ta kwanta bata fito daga dakin ba sai goma saura ta fito sanye da hijjabin ta har qasa lkcn suna parlourn shida Hajiya da Daddy yanata tura twince din a motocinsu na wasa suna zagaya dakin sunata dariya shima yana tayasu qasan zuciyarsa cunkushe da tunanin ta inda zai fara da uwarsu don baiga alamun sauqi daga gareta ba ya lura tausayin ma nasa da takeji ya goge a idonta yanzj tsanarsa kawai yake hangowa a qwayar idonta zama tayi kusa da Hajiya tace.
“Morning Dad " murmushi yayi yace “Uwata tafi ta kowa kin tash lfy ya kayan lada" qasa tayi da kanta tace “alhmdllh" suka gaisa da Hajiya shima yazo ya zauna shine ya karya billen da cewa “qanwata ba fada meye ya kawo gaba?" Qasa tayi da idonta ya kumayin murmushi ya matsa ya zauna a kujerar dake kusa da ita yace “wlh ba laifina bane bansan Abu Nawwas ya rasu ba sai shekaran jiya Daddy yake fadamin kiyi hqr Allah ya jiqanshi ya gafarta masa Allah ya raya mana twins dinmu cikin imani"
Amsawa sukayi da amin ta daidai lkcn da Nawwas ya turo motarsa yazo ya riqeta ta dagoshi tana dariya tana cewa “Ehhh yarona bature na Ina kuka kwana ne yau Hajiya a gurinki suka kwana?" Dariya Hajiya tayi tace “aa nikam ai bana gayyar fitsari gurin ubansu suka kwana" yayi dariya yace “aikuwa nasha fitsari ta ko ina har gara Little ita nata da sauqi amma wannan fumfumgaron daya rinqa antaya min fitsari saida nayi zaton a swimming pool nake yasin" ba Hajiya da Daddy ba hatta Umaimah saida tayi dariya kyawawan haqoranta suka bayyana da yar siririyar wushiryarta dimples dinta suka lotsa sosai tuni Hameed ya shagala da kallonta rabonsa da ganin dariyar Umaimah haka tun tana gdansa shekara kusan biyu kenan da rabi.
Hajiya ce ta lura da inda hankalinsa yake ta dauki pillow ta jefeshi yayi firgigit ya dawo hayyacinsa yana sauke ajiyar zuciya ya miqe yace “a bawa twins abincinsu susha zasu rakani anguwa” yana fadin haka ya shige dakinsa ya fada gadi yanajin wani farin ciki a ransa yaudai yaga dariyar Umaimatu wanka ya shiga ya fito ya shirya cikin qananun kaya ya taje kwantacciyar sumarsa data qara kwanciya chocolate din fatarsa tayi wani mugun kyau da haske ya zama fari ma zaace saboda hutun California.
Fitowa yayi ya tarar sai Umaimah kadai a parlourn tana riqe da qaramin qur'ani a hanunta ya jima yana kallonta kafin ta dago suka hada ido yace “ina yarana an shirya su?" Daga masa kai kawai tayi taci gaba da karatun ta baiji dadin yanda tayi masa ba amma haka ya danne ya nufi dakin da yake jiyo hayaniyar su ya daukosu suka fice.
Basu dawo gdan ba sai yamma liqis yana zuwa ya tarar da Hajiya Sa'adatu kakar twins da Nazir Sulaiman wanda suke tsananin kama da Sulaiman din suna zaune a parlourn Umaimah na gefe sunata hirarsu da Nazir yana bata lbrn aikin daya samu a Abuja ba qaramin faduwa gabansa yayi ba da ganin Nazir saboda tsananin kamarsa da Sulaiman har tayi yawa jiki kawai Sulaiman zai fishi da kuma shekaru.
Nazir yana ganinsa ya miqe ya miqa masa hanu ya karbi Nawwas da yaketa washe baki yace “oyoyo my son inata missing dinka long time aiki ya boyeni" yana mgn yana miqawa Hameed hannu shima ya miqa masa daqyar ya tsaya suka gaisa da Hajiya Sa'adatu yayi musu ta'aziyya ya shige daki yana kaiwa da komowa yana ayyanawa a ransa “dama Sulaiman yanada qani karfa qanin yace yanason zai auri Umaimah" gabansa ya sake bada wani rasss yace “aa ne bama zai yuwu ba wlh Umaimah tawace wannan karon da yardar Allah” komawa yayi ya zauna zuciyarsa nayi masa zafi a fili yace “Allah kada ka qara jarabtata da rasa bloody a wannan karon Allah kafi kowa sanin halin da nake ciki ka qadarta min rabuwa da ita nace ka kasheni kaqi yanzun kuma ka sake rabani da ita Allah kada kayimin haka idan laifin dana aikata makane na tuba Allah astagfurullah ya Allah” su Uncle manya🤣
Kwanansa tara a garin Kano ya koma California.
Kwanci tashi babu wuya gurin lillahi yau litinin ta kama ranar da Umaimah ta gama takabarta takaba mai tsarki tayiwa Sulaiman ba irin takabar matan zamanin nan ba.
A washe garin ranar kuwa Hameed ya shigo garin cike da farin ciki amma me daga bakin get yayi turus ganin baquwar mota a gdan Umaimah ce tsaye sanye da hijjab dinta har qasa ita da Nazir ya kawo Mata wasu takardun filayen Sulaiman yana tsokanarta kan cewa taba dakai bori ya hau kawai ya taimaketa ya aureta tunda Sulaiman ya wullah takai masa duka tana dariya ya kauce tace “yaron nan ka rainani da yawa kalleni dakyau ka gani ni saarka ce?"
Suna dariya driven ya fito a mota ya bude masa shima ya fito ya zuba idonsa akanta idonsu ya sarqe da juna duk da nasa a cikin glass yake gabanta ya fadi sosai da taga ya nufosu ga mamakinta yana zuwa taga ya miqawa Nazir hanu sunyi musabiha ya cire glass din idonsa ya zuba idonsa akanta sosai yace “barka bloody sister".......
*UMMUH HAIRAN CE...✍🏻*
[2/3, 7:16 PM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_*
Dagowa tayi ya sakar mata mayaudarin murmushinsa yace “muje inason ganawa dake" kawar da kanta tayi tace “kaje Ina zuwa" yanda tayi mgnr ba qaramin bata masa rai yayi ba amma tunda nema yakeyi sai kawai yayi gaba tabi bayansa da kallo tayi qwafa sukaci gaba da hirarsu da Nazir saida ta bata kusan awa guda sannan sukayi sallama ta nufi cikin gdan tun a qofa ta cire hijjab dinta tana cewa “gsky Hajiya weather