Showing 267001 words to 270000 words out of 296878 words
mashi saboda yadda Jaish ɗin ya zaro ido, amma sai ya danne ya ɗagawa Jaish ɗin gera guda alamar ya ne Jannat ɗin ta yi ko?.
"A'a ba Jannat ba, cewa zaka yi dai ka gaji da kallona da mutunci ne kawai a cikin gidan nan, ai gara ka ja mutuncin nawa a kan titi sai ka fi jin daɗi, please get out from my side ma, am very very angry wlh, I don't want to talk to much, idan ka matsa mun kuma Allah you know the rest, i will make you regret". Yana magana yana banka mashi harara da waɗan nan idanun nasa na gado wadda da ka gansu kasan yes yaran Momma ne ba tambaya, dan ita idanun yaranta sun sha banban da na kowa a gidan, sun fi na kowa dara dara a gidan, saboda ita da King ban san waye za'a ce ya fi wani manyan manyan kyawawan ido ba, da yake dai shi da ita duk tushe ɗaya ne sai suka gaji idon daga wajensu King Badeen.
Harararsa Jawad ɗin ma ya fara yi kafin ya ɗaura da cewa. "I can't go anywhere, wai da kake ce mun baka son yin magana sosai ni zaka yi wa iskanci? Kaga malam ni ka bar dukka wannan zance let's talk serious, bar wasa, what's going on? What's wrong with you? I know ban kyauta maka ba, amma ka sani jiya wlh naso zuwa mu yi magana, amma sai na sha'afa gabaɗaya da zancen kace nazo mu yi magana, am sorry about that..."
Wani irin kallo Jaish ɗin ya wurga mashi kafin ya janyo zip ɗin echolac ɗin ya rufeta tare da cewa. "Bani da mahimmanci a gabanka ne yasa ma zaka sha'afa da zancena".
"Kai bro, ni ban san kalarka ba, gaka da saurin fushi, gaka kuma da balai'n kunya, sannan idan ka yi fushi baka sauƙowa da wuri, ayi ta yin magiya amma duk a banza sai time da ka ga dama kake saukowa, ga zuciyar bala'i, kuma a haka wai baka son haɗa ido da mutane saboda kunya, yanzu na gano ba kunya bane ne yake damunka tsantsar rashin kunya ne yake damunka, ni mu bar wasa please, a ƙage nake da na ji me yake damun ɗan uwana, if not zuciyata zata buga". Ya kai maganarsa ta karshen nan cikin serious babu wasa.
Bayan harara babu abin da Jaish ɗin ya bisa da shi, sannan ya zauna a gefensa. In short ya bashi labarin abin da yake faruwa da kuma tafiyar da zai yi, daga karshe ya rufe mashi da cewa kada ya gayawa kowa ya yi wannan tafiya har da Momma, dan ba zai wuce kwana ɗaya ba, gobe zai dawo.
Sosai Jawad ɗin ya yi mashi fatan alkhari tare da addu'oi masu karfi. Cike da son ɗan uwan nasa ya amsa da amin. Daga haka suka shiga hirar duniya har zuwa lokacin da jirgin Jaish ɗin zai tashi. Kafin ya tafi zuwa airport sai da ya je cikin dabara ya ga Momma, sannan ya je wajen King, daga haka ya nufi in da Auta take, dan ba zai iya tafiya ba tare da ya sanyata a cikin idanunsa ba.
Sosai ya tsareta da idanu kamar wadda yake yi mata kallon bankwana, har sai da ta tambaye shi lafiya? A lokacin kuma Gimbiya Chuchu tana kwance ta shige cikin bargo tana waya da Yah Rizwan, Autar tana kwance tana fuskantar kofar shigowa tana latsa wayar Yah Jawad da ya bari a wajensu.
Lafiya lou ya amsa mata da shi kafin ya buɗe mata hannu a kan ta zo. Da sauri ta diro ƙasa daga saman gadon ta tafi ta faɗa jikinsa tana murmushi, duk wannan bidiri da ake yi Chuchun bata da labari, hira ya yi daɗi ga shi tana ƙule a cikin bargo ne yasa sam bata jiyo komai sai kalman yayan nata da yake zazzaga mata tana kara macewa haɗe da narke mashi.
Sosai ya rungumi Autar a jikinsa yana jin tsantsar kaunar ƴar uwar nan tasa, ita kaɗai suke da shi mace a ɗakinsu, suna ji da ita kamar me, da kyar ya iya raba jikinsa da nata sannan ya wuce ba tare da ya ce mata komai ba. Ta ɗan yi mamakin ganin hakan da ya yi, amma bata kawo komai a ranta ba ta koma cikin ɗakin tare da hayewa gado ta kwanta.
A wannan rana dai Jaish ya bar kasar ba tare da sanin kowa ba sai Jawad ɗin da yake tamkar jinin jikinsa, kun san shakuwar da take a tsakaninsu tun suna yara. Ko airport ma Jawad ɗin ne ya kaisa a sirrance, sun jima sosai a lokacin da suka yi hugged na juna kafin jirgin ya ɗaga, ba yau bane farau na su yi tafiya ba tare da sanin kowa ba, su je su dawo, amma su kansu yau ji suke yi kamar waɗan da zasu yi rabuwa ta har abada.
Jiki ba kwari Jawad ya juya ya dawo gida, duk sai ya ji wani iri, yana tukin mota yana tunanin Jaish ɗin kamar yau suka saba rabuwa.
Yana dawowa gida room ɗinsa ya shige ya yi kwanciyarsa dan ya ɗan huta.
Da misalin karfe 8 na dare gabaɗayansu sun haɗu a saman table a dining room domin cin abinci, Mama dai tana can room nata ta sha allurar barci, saboda azaban da take ji a jikinta na raɗaɗɗin cizon kwarin nan da kuma tsakanin kaikayi da wajen yake yi mata, ga shi babu halin sosawa, hakan yasa da kanta ta buƙaci ayi mata alluran barci ko zata huta da azaban!.
Kasancewar yau Jaish baya nan sai Jawad ya halarci dining room ɗin, ba zai iya cin abinci shi kaɗai ba, dama kun san a tare da Jaish ake kai masu nasu part ɗin ɗaya daga cikinsu, so yau baya nan sai ya ji gara mashi ya fito su haɗu a dining room ɗin ko ya rage kewar ɗan uwan nasa.
Sosai King ya yi mamakin ganinsa a room ɗin, bai yi nauyin bakin tambayarsa yau kuma a nan ya ga damar cin abincin ne? Da e kawai ya amsa mashi. Sosai King ya lura da yadda jikinsa yake a mace, ya yi wani sukuku da shi, nan ma bai yi nauyin bakin tambayarsa ko bashi da lafiya bane yake yi kamar wani mai jin barci?. Sam basu kawo a ransu cewa Jaish baya gidan ba, dan kowa yana da ra'ayin zuwa in da yake so ya ci abinci, sun yi zaton Jaish ɗin yana ɗakinsa.
A'a lafiyarsa lou ya amsa da shi. Shiru King ya kyalesa da nufin idan sun gama cin abinci sai ya tasashi gaba ya gaya mashi me yake damunsa? Dan dai ga damuwa kam nan karara a saman fuskarsa.
Kowa ya hallara a room ɗin ban da Gimbiya Chuchu dake cikin room ɗinta tana ta aikin zuba soyayya da Yah Rizwan, waya suke ta yi ba kakkautawa, ya gaya mata gobe zai biyo su Ramish domin kawai ya zo ya ganta, sai daɗi take ji. Da alama Rizwan ya iya soyayya sosai, sai zuba uban murmushi take yi fuska cike fal da annuri. Allah sarki shi kuma Yah Jawad yana can daning room yana tura abinci kamar dole yana fama da kewarta da kuma tunanin Jaish. Da dai ya gaji sai ya ce da Auta.
"Auta ina Jannat ne?". Ya tambayi in da take ne kuma domin yana da buƙatar ta zo nan ko zai rage kewa da tsananin tunanin ɗan uwan nasa da ya tsaya mashi a rai sosai, bai san meyasa ya damu har haka ba.
"Aunty Chuchu tana ɗakinta". Auta ta bashi amsa.
King ne ya ce. "Meyasa bata fito cin abinci ba?".
Still dai Autar ce ta bashi amsa, domin babu wanda zai iya ce maka yasan halin da Chuchu take ciki a gidan biyun Autar. "Daddy nima ban sani ba, ina ganin kamar bata jin yunwa ne ko kila sai ta yi shirin kwanciya zata sha wani abin mara nauyi kamar shekaran jiya da jiya".
Jawad ne ya ce. "Go and call her for me". Ya yi maganar ba zato ba tsammani yana kawar da kallonsa daga kan Autar suka haɗa ido da King.
Wani irin kallo King ɗin ya jefa mashi wanda ya ɗan sanya shi sakin siririn murmushi. Hannunsa ɗaya ya kai ya ɗan shafa sumar kansa yana cigaba da ɗan murmushi. Hararar wasa King ya wurga mashi yana mai cigaba da kai abinci bakinsa.
Sai kallonsu a sace momma take yi, ta fahimci akwai wani abin dai da King bai gaya mata ba dan gane da Jawad, dan yadda yake binsa da irin wannan kallo akwai wata a ƙasa.
Shi kuma Yah Jawad sai ya kawar da kallonsa daga kan King ɗin ya cigaba da cusa abincinsa cikin baki wanda yake jinsa kamar magani saboda rashin daɗi.
Miƙewa Auta ta yi ta nufi fita daga room ɗin. Ko da ta je manne da waya ta isko Chuchu, sai zuba hira suke yi, tana ta kashe Yah Rizwan da shagwaɓa, soyayya ta yi daɗi tama mance da abinci. Kiranta Autar ta yi sannan ta juya bata tsaya ta jirata ba, dan yunwa take ji Allah ya gani.
"Yah Rizwan daddy na kirana in je in ci abinci, ka bari sai na dawo ko?".
Daga other side ɗin ya amsa mata da. "Bari na zo to na baki a baki ko? Dan bana son ki sha wahala, da akwai yadda zan yi in tauna maki ma sai na tauna maki".
Wani irin sihirtatcen murmushi ta saki kafin ta bashi amsa da. "Kai Yah Rizwan, ai zan ji kunyar su daddy idan ka ce zaka bani abinci a baki, ba zan iya ci ba, har da Akka fa da su Mummy dukka a wajen, kuma sai ka iya bani a baki ba zaka ji kunyarsu ba?".
Nisawa ya ɗan yi. "Wacece kuma Akka? Ina ruwana da ita? Zan dai ɗan ji kunyar Mummy, amma banda daddy".
(Da alama Akka fa dukka jikokinta ne basu kaunarta 😅 kun ji Rizwan da walaƙanci wai wacece kuma Akka😅 ko da yake wannan tsohuwa zama da ita sai irinsu Guyson ne za su iya, wato masu mugu mugun hakuri sosai kenan 😅 babu ruwana dai ni kam kada ace na ce, to ban ce ba.🌝)
Ɗan zaro idanu ta yi na jin ya ce wacece kuma Akka da kuma ba zai ji kunyar daddy ba sai Mummynta.
"Yah Rizwan ni kuma na fi jin kunyar daddy a kan Mummy fa". Ta faɗa tana sauƙowa ƙasa daga saman gadon.
"To bana son gimbiyata ta zauna da yunwa, jeki ki ci abinci ki ƙoshi sosai, hirarmu ba zata kare ba, idan kin dawo zan baki wani labari kin ji ko?".
Da okey ta amsa mashi tana ƙoƙarin katse kirar ta tsinkayo muryar can ƙasa ƙasa yana faɗin. "I love u my sister, ki kula mun da kanki, i will going to miss this your sweet voice wadda idan kina magana yana sanya na rinƙa jin mamar barci zai ɗaukeni, bana........" Dakatawa da yin maganar ya yi sakamakon shigowar Ramish da Bilal cikin room ɗin nasa.
Ita kuwa jin ya dagata yasa ta mayar mashi da kalmar i love u too tare da katse kiran ta nufi waje.
Kai tsaye dining room ta nufa. A saman kujera kusa da Auta ta zauna, ya zama suna fuskantar juna ita da Yah Jawad ɗin, shi kuma daddy da kujerarsa take a gaba yana iya ganin fuskar kowa, a side ɗin kujerarsa ce kawai a wajen.
"Meya hanaki fitowa ki ci abinci?". Jawad ya tareta da wannan tambayar.
Gaisuwa ta fara ɗagawa daddyn nasu, bayan ya amsa ta gaishe Akka sannan su Momma haɗe da Akka, sannan ta bawa Jawad ɗin amsa da tana waya ne, da yake bata iya karya ba, amma bata gaya mashi da waye take yin wayar ba. Bayan ta bashi amsarsa ne ta ɗagawa su Sarina gaisuwa a matsayinsu na sister ɗinta.
Cikin nutsuwa suke cin abinci. Kuyanga Zubaida ta zubawa Chuchun abin da take buƙata. Room ɗin ya yi tsit kamar ba mutane, sai sautin spoon ɗai ɗai zaka ji yana tashi.
A hankali Chuchun ta ɗauki cup mai shake da pina colada zata kai ɗan bakinta, tana jin ra'ayin shansa kaɗan ba dayawa ba.
Bata ƙarisa kai shi bakin nata ba ta ɗan yi ƴar ƙara tare da sakin kofin ya faɗi a saman table ɗin.
A hanzarce gabaɗaya kowa dake saman dining ɗin ya ɗago da kansa tare da kai kallonsa kanta. Auta ta riga kowa tambayarta lafiya me ya sameta?.
Autar bata rufe baki ba King ya jefo nashi tambayar. Nan take kowa ya fara jefo nasa tambayar, sun tsura mata idanu suna jiran amsa.
A hankali ta ɗan ɗago idanunta ta saci kallon Jawad da suke fuskantar juna, ya yi wani yin ƙasa da kai kamar babu shi a room ɗin. Bin in da take kallo da kallo King ya yi, ganin Jawad take kallo yasa ya cigaba da cin abincinsa ya fita shirginsu, dan yasan in ya biye masu ma shi zai ji kunya a banza.
Su Momma sai tambayarta suke yi ta ƙasa yin magana, kowa ya ruɗe yana ta cewa lafiya kuwa? Amma ina ta ƙasa magana.
King ne ya ce. "Wai ku ku rabu da ita mana, Zubaida ki sake zuba mata wani pina colada domin ta sha dan naga shi take ra'ayi".
A hanzarce kuyanga Zubaida ta zo ta fara kwashe wanda ya zube ta gyara wajen, sannan ta zuba mata wani ta turo mata shi gabanta.
Ɗauka ta yi tana ta kallon fuskar yayan nata. Shi kuwa kamar babu shi a wajen.
Tana ƙoƙarin kai cup ɗin bakinta a karo na biyu ya sake yi mata abin da ya yi mata ɗazun yasa ta zubar da wancan pina ɗin, ba tare da ya ɗago ya kalleta ba. Ba komai yake yi mata ba face babbar yatsar kafarsa yake zurowa ta ƙasar table ɗin yana ɗan yi mata kamar tafiyar tsutsa a kafafunta, da yake doguwar riga ce a jikinta, ta ƙasar rigar yake zura kafar tasa yana taɓa mata tata. To da ya yi mata na farko tsoratata ya yi, dan bata yi expect na jin hakan ba, ta tsorata.
Yanzu ma a hankali ya sake zuro kafar tasa ya fara yi mata kamar ɗazun. Still yanzu ma ta tsorita, sai dai bai kai tsoron da ta ji ɗazun ba, ɗan lumshe idanunta ta yi tare da kai cup ɗin ɗan bakinta.
Bata cire cup ɗin daga bakin nata ba ta waro idanun nata a saman fuskarsa, a lokacin shi ma ya zuba mata idanu yana kallonta, wani irin kyau ta yi mashi lokacin da ta lumshe idanun nata, sai ya ji ta gama tafiya da shi mai gabaɗaya, da babu kowa a room ɗin ba abin da zai hana shi rungumota.
Cigaba da yi mata tafiyar tsutsa a kafar tata ya yi yana mai cigaba da kallonta, ita ma tana shan pina ɗinta tana kallonsa tana ɗan murmushi. A hankali ya gangaro da kafar tasa izuwa dai'dai sai tin tata, sannan ya sanya ƴatsun kafafun nasa ya riƙo nata babbar yatsar kafar yana wasa da shi.
Duk abin da suke yi King yana kallonsu, amma ya cigaba da cin abincinsa tamkar bai ga komai ba, tunanin abin da zai yi kawai yake yi a ransa, tunanin kalar hukuncin da zai yanke masu yake yi.
Matse mata babbar yatsar kafar tata ya yi a cikin tsakiyar nashi yatsun. Har sai da ta ɗan yamutse fuska alamar zafi, ɗan turo mashi baki ta yi tare da ajiye cup ɗin pinan nata, kamar zata sanya mashi kukan shagwaɓa.
Ganin hakan yasa ya ɗan sakar mata ƴatsun nata, yana saki ita ma tasa nata wai zata kamo nashin ta matse ya ji idan da daɗi. Amma ina ƴan yatsunta ba za su iya kama na shi ba, ya yi mata girma. Kamar zata yi kuka take binsa da kallo tare da turo baki.
Wani siririn cool murmushi ya sakar mata wanda ya sanyata sauke ajiyar zuciya, sannan ya kashe mata ido ɗaya. Plate ɗin abinci da kuyanga Zubaida ta zuba mata ta jawo ta fara ci tana sakin murmushi, tana jin daɗin kasancewa da Yah Jawad a yanzu, saboda yana sakar mata fuska kuma yana mata wasa sosai, so tana jin daɗin kasancewa a tare da shi sosai da sosai.
Bayan sun kammala cin abincin ne ya janye kafarsa daga kusa da tata, a hankali ya miƙe tsaye. "Jannat ki kawo mun wayata da na baki room ɗina". Yana maganar unexpect again kallonsa ta sauka a kan King, tun ma daddyn nasu bai yi wani yunƙurin ba ya sakar mashi murmushi tare da sa kai da sauri ya wuce.
Sai dai kafin ya fita muryar King ɗin ta daki dodon kunnuwansa da cewa. "Ka sameni a room ɗina yanzu Jawad".
Da okey kawai ya amsa sannan ya fice. Da ɗaiɗai da ɗaiɗai kowa ya watse a room ɗin.
Akka tana shigowa cikin room ɗinta wayarta dake saman bed ya fara ruri. A hanzarce ta ƙarisa ta kai mashi agaji.
Picking ta yi tare da hayewa saman gadon mai gabaɗaya.
Daga can ɓangaren Rizwan ya fara tsantsara mata sallama tare da ɗaga mata gaisuwa.
Sai da ta zage shi kafin ta amsa, wai yau kuma wani munafurcin yasa ya kirata? Dan rabon shi da kiranta tun last year sallah da ya kirata ya yi mata happy sallah, to yanzu kuma gulmar me yasa ya kirata?.
Hakurin ya fara bata tare da rarrashi yana gaya mata aiki ne ya yi mashi yawa. Tatas ta zage shi daga shi har su Ramish ɗin gabaɗaya kafin ta saurare shi, Akka akwai dirama tsohuwar nan.
Cikin zumuɗi ya sanar da ita dalilin kirata, ya kira ne ya sanar da ita ya samu mata kuma ba kowa bace face Chuchu, dan haka ta taya shi kafin ya zo.
Wani irin matuƙa fari tas ɗin farinciki ne ya mamaye mata cikin zuciya. Haƙiƙa ta ji daɗi kuma ta yi murna, amma sai ta ɓoye murnar tata, ta fara zazzaga mashi masifa a kan ai dama tasan yanzu ma buƙatar kansa ne yasa ya kirata, to dan haka ya sani ba zata bashi Chuchu ba, kuma dai yasan ita ce mai zartar da hukuncin a kan komai.
Lallaɓata ya fara yi yana magiya tare da marairace