Showing 18001 words to 21000 words out of 39506 words
zuwanshi. Har ciki suka shiga can sai gasu tare da wasu nurse harsu biyu suka zo. Buɗe motar yayi suka shiga tare taren kamani dan kar na gudu. D'aga hannuna nayi nace.
"Basai kun tare ni ba." bin bayanshi nayi har ciki ina zubda kwalla, ofishin likitan muka shiga.
Zama mukayi dake baya cikin ofishin, dafa shi nayi muryana na rawa nace.
"Don Allah na fanshi cikina d aurena, ka sakeni wallahi daga nan zan shiga duniya na ɓata baki ɗaya kowa ga huta."
"Karki damu kanki, ciki zaki sake samun wani, banda ma ɗaurawa kai damuwa. Kinga Aneesah sai huɗu tana cire ciki kuma babu abinda ya sameta, balkisu rufe mata bakin mahaifa akayi, Fareeda kan mahaifar aka cire. Kina karama yaushe zaki damu kanki akan cikin da bai da muhalli, ki kwantar da hankalinki a cire nayi miki alkawarin zan baki naira million goma ki fara kasuwanci sannan zan kaiki Sudan ko U.S. ko Dubai kiyi karatunki har ki zama cikakkiyar likita, nd bayan haka zan mallaka miki komi zan mai dake saraun..."
"Bazan fansar da cikina haka ba, bazan karɓi ko sisinka ba..."
Shigowar likitn yasani ɗago kaina wani garjejen inyamuri da shi tare da nurse su biyu, ɗaya tana rike da tire ɗaya da takardu. Mikawa Daddy tayi ya karɓa ya cika komi, me ɗauke da tiren ci ta ajiye ta fasa alluran ta suke a cikin siring. Sannan tasake fasa wani, ta zuke har uku.
Juyawa nayi na kalleshi cikin zubda kwalla masu zafi nace.
"Duk sabida son kai ko?"
Juyar da kai yayi yna kallon gefe, matsowa matar tayi na juya na kalleta, nace.
"Ke mace ce kika zaɓi, saɓawa Allah sabida kici abinci? Nasan cikin zai zuba tunda gani a hannunku saidai kusani kamar yanda na zubda kwalla haka kuma sai kungani akwaryan tuwonku, kai likita ka buɗe inda za'a na zubda rayukan bayin Allah bayan Ubangiji nasane da wanzuwarsu ka zaɓi kaucewa a hanya sabida kuɗi. Insha Allah daga yau kun daina dariya kamar yanda na tsayida sallah, da wasu ibadodin Ya Allah nayi tawwasalida sunayenka kyawawa ka ɓarar da farin cikin duk wanda ya ɓarar da farin cikina, Ya Allah ka kuntatta musu kasasu su kaunaci mutuwa fiyyeda rayuwar duniya, Ya Allah ka ɗaiɗaita Rayuwar wanda suka bada kofar a..."
Fincikoni yayi ya juyar dani tare da janye zanin jikina suka tsikara min allura. Ajiyar zuciya na sauke tare da komawa na zauna bayan sun gama murmushi likitan yayi nima nayi ni masa dariya nace.
"Allah Kana gani kana ji, suka cutar da ni Ubangiji ka hanasu sukuni."
"Alhaji karki damu just five min zaka ga aiki but kace ba se anyi woke ciki ba, zaka keshi asibiti wani."
Mikewa yayi ya ɗagani muka fita har munkai bakin kofa, nace.
"Bazaka sake ganin haske ba a rayuwarka, sai dai duhu hakkin cikina da kuka zubda sai ya hanaku farin ciki, sai mahaukata sunfiku daraja."
Janyoni yayi da karfin tsiya har waje yasakani a mota, sannan ya zaga gefenshi ya ja motar da sauri yana kallon agogon hannunshi.
Kallonshi nayi ynx fuskarshi a sake, kamar bashi ba murmushi nayi sannan nace.
"Tabbas sunanka mai nasara, sai dai daga yau ka zubda duk wata nasarar da kake da ita sonda nake maka dabance da ta kowa, kamar yanda kazubda ciki jikina Insha Allah ka zubda soyayyarka a cikin zuciyata ka lalata duk wani soyayyarka Insha Allah bazaka kum.."
Dafe cikin nayi sabida wani mugun ciwo da kuma zafin da ya ziyarce ni, lokaci guda kuma nayi daukar ruwa mai ɗumi, kallonshi nayi hawaye na zuba a idanuna.
"In Allah ya yarda sai ya bimana hakkinmu da ni da ɗan da ka zubda min, sai kayi nadama mara amfani Allah ya gani na kiyayye hakkinka kai ka shiga namu, amma ba damuwa ni nabarka da Allah shizai bi mana hakki."
"Waini kam maryam duk wannan addu'a dan an zubda cikin jikinkine, kina bani mamaki."
Jiri nake gani, tare da duhu na rike cikina ga wani zufar dake bin jikina kamar ina cikin zafi. Jinine ya tsinke yaje zuba sosai komawa nayi da baya ina runtsa idanuna, duk ilahirim jikina rawa yake, sosai ya taka motar ganin yanda lokaci guda nake sauke haki.
Babbar asibiti yayi dani sannan yakira dr Nafe ya faɗa mata, kwatancen matenity tayi mishi, da gudu ya isa gurin,.
Parking yayi ya fita tare da zagayowa ta gurin da nake ya buɗe, sannan ya cironi ganin yanda jini ya jika min kayana daga kan zanina har hijab ɗin jikina, ga kuma wanda yake zuba.
Cak ya ɗaukeni bai taɓa ganim jini haka ba, sai yau. Yana shiga dani ciki kowa sai binmu yake da ido tsabar tashin hankali.
Gadon marasa lafiya dr nafi da wasu nurse suka turo, ya ɗaurani akai, da sauri suka wucce dani ɗakin yan ɓari, lokacin bansan waye akaina ba, jikinshi duk ya ɓaci, kita yayi ya shiga mota sai gida. Kayan jikinshi yake son sakewa, a falo ya sami Fareeda da Balkisu, ganinshi cikin tashin hankali ga jini na bim jikinshi, kallonshi Fareeda tayi, cikin tashin ɗimauta tace.
"Ka zubda cikin ko? Ka zubda hankalinka ya kwanta, hmmm amma kasani kasayi tashin hankali da hannunka, ka zubda abinda zai hanaka barci, ka zubda namu ka kwana lafiya wannan da ka zubda sai ya zame maka alakakai kaida ganin farin ciki har abada, mi zanyi da azzalumi irinka mugu fasiki, dan shine yake aikata duk abinda Allah ya haramta, ka kuma turo min da sakina dan na gama zama da kai."
Bakin ciki ya hana balkisu magana itama sama ta haye ta ciro kayanta daga wardrob ta shirya a wani babbar jakanta, tare da fashewa da kuka, tabbas duk abinda Yunus ya aikata da sa hannunta, dan da ta zama mace ta gari da babu yanda Yunus zai taɓa zubda cikin wata ba, itace ta fara nuna mishi bazata iya rike huda ba, yau gashi kuskurenta yaja kowa ya rasa farin cikinsa. Da yau ta cire mulki da son jiki da babu wacce zata zubda hawaye da yunus da ta amshi matsayinta na mace da Yunus bai zama abinda ya zama na mugun hali ba, ina zata kai hakkin Maryam. Mi zata cewa Ubangiji sabida kuskurenta Yau Iowa yana Kuka.
Mikewa tayi zuwa d'akinta Fareeda ta take zube a gabansa abin sallah tana Kuka mai con rai. D'agota Balkisu tayi cikin Kuka tace.
"it's my faults, banyi deserve yafiyarku ba, dan nice na nuna mishi yara basu da daraja, haka ma mace tana da lokacin da ta dace ta d'auki ciki, kosa halinshi nice na fara lalata shi, dan dama ance matar fari ce ke lalata miji kuma na yarda da haka Fareeda ku yafemin Dan nasan hakkinku bazai tabari barina na zauna lafiya ba, Ynx a wani hali maryam take ciki."
Mikewa Fareeda tayi daga duken da take ta janyo gyalenta suka fita, duk suka zauna a falo.
Can sai gashi ya fito jikinshi a sanyayye ya fita, bin bayanshi sukayi suka Shiva mortar fareeda.
Juyawa yayi yaga sun shige motarta, jan motar yayi har suka fita, daga gidan suna bin bayanshi.
Koda suka isa asibitin, har inda aka shiga dani.
Koda suka iso kiran Dr Nafi yayi, yace ya dawo.
Dama suna can ana rikici akan karfin alluran da aka min, koda ta fito ba tare da damuwa ba tace.
"Yallaɓai badan ina ganin kimarka ba da babu abinda zan taɓa yiwa matarka. Ka dubi abinda ka janyo min ana ganina da kima kasa an farq zargina da cewa ko nice nayi mata alluran da yafi karfin jininta, kasa manysn.likitoti suna cin mutuncina kimanin shekara goma sha biyar ina nan ban taɓa samun matsala da kowa ba, sai akan case ɗinku ka kaita am mata allura mafi hatsri wanda ba lallai bane tasake ɗaukar ciki. Wallahi baka kyauta min ba ka nemo jini a saka mata dan jininta yayi matukar zuba badan Allah ya takaita cikin ya fita ba a cikin jini da bansan yanda zanyi da wannan tashin hankali."
Tana gama faɗar haka ta juya tabar gurin kowa sai masa kallon Allah wadarai suke, dan da da farko sun tausaya masa jin abinda yayi muka bai musa ba, yasasu, ji haushi har wani mutum yace.
"Wallahi kayi asara, cikin sunnah ba shege ba, ni ynx zuwana asibiti na goma sha ɗaya kenan ina niman ko ɓarine Allah ya bani a cikin gidana kai da kasamu har kana kai matarka wa i gurin aka zubda cikinta kasan kuskuren da ka aikata kuwa, Kai da Allah."
Kuka balkisu take, sosai can wata nurse ta fito akan jinin da za'a karamin, lab suka nufa aka ɗibe jininshi, dake grp (O) jininshi.
Koda aka saka min amadadin jinin ya gwauraya. Kusan awa ɗaya da saka jinin sai ga borin jini, sosai ya feso har kan fuskana dole suka cire jinin, dr Nafi ta fito cikin jin haushi tace.
"Toh jinin yaki, zama dan ya feso mata da borin jini, dan jininta A+ ne kuma da nakan zai mata, amma dole sai an nimo mai irin jininta sak."
Rike kanshi yayi ciki tashin hankali ys laluɓi nomber Yaya hayat ys kirashi dake a cikin asibitin yake, kallon dr Nafi yayi yace.
"Don Allah ki taimaka min kar yasan abinda ya faru, Kanwar Dr Hayat Omer ne."
Zaro ido tayi cike da mamaki, can sai ga Yayan ya iso, faɗa mishi halinda nake ciki Dr Nafi tayi da jinin da ake bukata, lab ya wucce aka ɗabi leda biyu sannan ya kira Hamdiya da shema'u da Suhaima matarshi. Ya faɗa musu,.lokaci kusan guda suks iso asibitin.
Cikin damuwa, har an wanke min mara sannan aka turoni a gadon bayan an sauya min kaya da wani dark green. Aka gunguroni zuwa ɗakin yan ɓari,
Sharaf nake kwance babu alamar numfashi, sai ma wani irin haske da nayi, fuskana a kumbure. Idanuna sun shige ciki, sau uwar karan hanci. Har za'a shiga dani yace.
"Ko zaku maidata aminity ne." karkata gadon sukayi zuwa wani keɓetacciyar shashi daban. Daki na biyu aka sakani a ward B....
Hankalinshi ya gama tashi, a tsorace yake da kowa, musaman matanshi da kuma ni.
Kiran Umma Aunty Shema'u tayi, can sai gasu tare da Mama suka shiga har ɗakin da nake ban sani ba.
Kallon yanda Fareeda ke kuka Umma tayi, cikin murmushi tace.
"Kiyi hakuri mana, Allah da ya amshi wannan shi zai baku wani, cikin ikonshi da buwayarshi, karki manta itama maryam ɗin bata wuci Allah ya amsheta ba, kinga kenan kukan ya kare,kuyi addu'a Allah ya maida muku, wanda suka fi wanda ya tafi Allah ya bata lafiya yasa masu cetone, ya kuma sake baku mai amfani da inganci."
"Amin, Umma Amin." Inji shi, har bakinshi na rawa.
Komawa gida Umma tayi, tunda Mams tace zata zauna. Gurin Azhar sai ga Rahilah da Aman, sunzo har da abinci suka zo dashi. Aunty Hamdiyya da Auntƴ shema duk sun koma gida, sai matar Yaya aka bari da Rahilah.
Balkisu itama ta koma gida, Fareeda kan gidan iyaƴenta ta wucce.
Can bayan La'asar sai ga Mamie, itama Ahmad da Rahimah har zuwa wannan lokacin ban farka ba, sai bin likitoti yake. Suna zuwa suna fita hankalinshi duk ya tashi. Bai taɓa shiga tashin hankali haka ba.
Yakira Hajiya zai faɗa mata tace mishi.
"Nagode ! ka zubda cikin ba? Ai balkisu ta faɗa mana komi."
"Hajiya kuskure aka samu."
"Ba kuskure bane Yunus, son kaine ita yarinyar ka sameta a sauki ba, dan babu sisin kwabonka akanta duk kuɗina ne, sannan ka cire mata cikinta da karfin tsiya, ka sata zubda kwalla. Yunus ni bazan maka baki ba sai dai fatar shirya Amma tabbas hakkin maryam sai ya tambayeka, yarinyar da tunda ta shigo gidanka kake wahalar da ita, bata taɓs faɗawa Iyayenta ba. Tsabar tana ganin zata iya da kai, kasan tulin zalincin da akayi gurin aura maka ita, yarinyar da batafi sha takwas ba, ka ganawa azaba ta hanyar rabata da farin cikinta, zaka ribanci abinda ka aikata, kuma zaka biya shi lokaci na zuwa da zaka ɗanɗana kuɗarka dan wannan bashine hakkin maryam kuma sai ka biya shi."
Tana gama maganar ta kashe wayar.
Dafe goshinsa yayi kaman zai tsage.
Har dare ban farka ba, dole yasashi tafiya gida amma badan yana son haka ba.
....... Koda ya isa gida wanka ya shiga, yana kwance ruwa na ratsa shi, tunanina da kukan da nake yasashi buɗe idonshi a gurguje ya fito ya sauya kayanshi na barci, ya kwanta dake yayi sallah a can masalacin asibitin.
Karfe biyu da hamsin da uku na dare, zaune yake a ɗaki tare da laptop ɗinshi ya nutsu yana, aiki. Kukan jarirai da shashekar kuka yake ji. Sosai kukan ya hanashi sukuni, mikewa yayi ya fito. Har falonshi baiga kowa ba, can sama yaji kukan dan haka ya haura yana bin kukan, har bakin kofar falona saka hannunshi yayi zai murɗa kofar yaji ya taɓa abu kamar ruwa, ɗaga hannunshi yayi yana dubawa, jini ya gani.
Ƙifar ɗakin ce tq buɗu ya kutsa kanshi, kwance ya hangoni cikin jini. Ga jarirai akwance a jikina muna kuka tare dasu. Sai kuka suke, suna kara rikeni tare da shigewa jikina, jikinsu duk jini.
Takowa yayi ya nufi kaina d sauri aka janyeni zuwa cikin duhu. Dariya aka mishi sannan aka ce, "Dole kabiya abinda ka aikata."
Muryan ce ta sauya irin tawa aka ce mishi "daddy karka zubar min da cikina" ta bayanshi juyawa yayi ya sake ganina a duke ina zubda jini, da sauri yayi kaina, aka sake mishi magana.
"Karka zubda min da ɗana."
Lokaci guda ya birkice ga jariran da suka rufa mishi, a jiki suna hayewa jikinshi, tare da zubda jini, ga wani irin kuka da suke mai cika kunne.
Durkushewa yayi yana sin kwance kanshi jinin dake bin jikinshi tare da kiranshi yasashi ɗagowa, yana kirana da gudu ya faɗa cikin ruwa tare da nutsewa kasar ruwan kaman ana janshi......
A firgice ya tashi tare da sake salati, tsabar ya tsorata gumi ke zubo mishi ta ko ina, tashi yayi zuwa ban ɗaki yayi wanka da alola, ya fito.
Sallar nafila yayi da addu'o'i ya kwanta.
Ko minti ɗaya bayi ba, yasake wani mafarkin damu, ina rike da jariran ina kuka sosai duk yanda yaso magana ya kasa dan dole ya shiga binmu dan idan yana kusantoni kamar janye ni ake.
Nan ma cikin ruwa ya faɗa, cikin mugun tashin hankali da firgici ya farka lokacin har ana shirin shiga masalaci, alola yayi fita da sauri dan jin kukanrmu yake kamar zai fasa mishi dodon kunne.
Koda ya shiga masalaci nan yasami nutsuwa yayi sallah bayan fitowarshine, ya koma cikin gidan ya sauya kaya ya nufi asibiti, tun da ya shiga ward ɗin yake jin faɗuwar gaba.
Har ɗakinmu. Murɗa kofar yayi ya shiga, a nutse tare da sallama. Ganin yanda aka kwantar dani tun jiya haka nake yasashi jingina da kofar ɗakin, tare da faɗawa mugun tunani.
Take ya soma jin kamar mafarkin da yayi yana dawo mishi, ɗago kanshi yayi ya zuba min ido dake akwai firgici a ranshi take idanunshi suka shiga nuna mishi abinda ya faru a mafarkin, dafe goshinsa yayi tare da barin ɗakin.
........ Cikin lokaci kalilan daga jiya zuwa yau Yunus ya gigita ya fita hankalinshi dan banda sautin kukana babu abinda ke mishi zarya a kunne.
Koda yaje gurin aiki kasa taɓuka komi yayi, ga wayar da yake akai akai. Kamar zararre haka ya koma ba halin ya runtsa ido toh zai tashi a firgice.
........Hankalin kowa yayi matukar tashi ganin har lokacin ban farka ba, sabida tashin hankali sai da Asthmar Mama Amarya ya tashi, haka muka na sake kwana, anan ne fa aka shiga niman mafita Aman da Ahmad sun bada shawaran a fita dani Jidda, yayinda Umma tace abarni zan farka kar ayi ɓarnan kuɗi.
Sai da nayi kwana uku, wanda a cikin kwanakin nan Yunus yayishine takar mahaukaci dan ko shi ɗaya ne kuka yake ji.
A binka da wanda bai magana sai abin ya shiga taɓa shi sosai dan har ana tunanin ko dan halin da nake cikine.
Hajiyarsu tana nan kaduna dan a gidan shi ta sauka. Mama kilishi ta koma.
Zaune suke kowa ya zubawa gadona ido.
Can na motsa hannuna, mikewa sukayi yana jingine a jikin kofa, ya zuba musu ido.
Sake motsawa nayi tare da bud'e idanuna, wanda duhu ya cika min cikinshi. Rufewa nayi can kasar makoshina nace "Umman !!! Zan sha ruwa."
Ruwan ɗumi ta ɗiba tare da mikawa Shema'u ta ɗaga kaina, ta bani nasha. Har ina kwarewa, maida ni tayi kwance,
Kowa na mamakin irin soyayyar da nakewa Ummanmu ba komi bane yaja haka sai yanda tajani a jikinta. Fiyye da sauran yaranta dan takance duk ciknki nafisu zurfin ciki, shi yasa takee mannani da jikinta, dukda bata koya mana faɗar damuwarmu ba, bawai dan bata son sani ba sai dai Umma tana da riko da saka abu a rai idan da tasan halinda