Showing 159001 words to 162000 words out of 189977 words

Chapter 54 - BUZU BOOK1 COMPLETE HAUSA NOVEL

18 Jan 2026

965

aka bawa wanda bai dace ba shugabanci, za a karya masu ƙaramin jari"

"Ƙananan 'yan kasuwar, da su suka yi wannan bita da ƙullin, da rubuta takardar lallai a sauke ka daga kan shugabancin nan, su ka ke tausayawa?"

Alhaji Fatuhu ya yi murmushi ya ce "Nima da ƙaramin ɗan kasuwa ne, kafin Allah ya kai ni matsayin da nake a yanzu. Kuma na san ba dukkannin su ne, su ka yi mini haka ba. Ni dai fatana dan Allah ka karɓi tayin riƙon ƙwaryar shugabancin nan da aka yi maka" Alhaji Fatuhu ya ɓata lokaci sosai da sosai, kafin ya shawo kan Alhaji Zailani ya amince zai karɓa.

*****

Gaddafi tuni ya koma gurin neman khɗinsa, saboda takaicin abubuwan suke faruwa a gidansu, ya fara damunsa.
Baba ƙiri-ƙiri haka ya zuba ido ya yi shiru, ba ya iya cewa uffan, sai dai ya zuba ido a kan lamarin gidansa. Sai ma dai idan an dafa a zuba a ba shi ya ci. Sosai al'amuran gidan su Nana, suka fara canzawa kullum sai an ɗora abinci sau uku a rana saboda hidimar da Jamila take yi da su. Ƙarewa ta saka ana ta yi musu gyare-gyare a cikin gidan.

Babban abin da yake damun Hajiya Sa'a da Jamila, shi ne yadda take ta ƙoƙarin janyo ta, cikin ɗaya mummunar ɗabi'ar da suke aikatawa ta lesbian.
Sai dai Jamila ta kafe da kai da fata, taƙi amincewa da hakan.
Sai da Hajiya Sa'a ta yi mamaki, saboda a ƙulumboton da ta yi wa Jamila, babu yadda za a yi ta iya kaucewa duk wata buƙata da ta zo mata da ita, amma ta kasa galaba a kan Jamila.
Duk wani shashashanci da suke yi tana kallo, amma sam ba ta ji abin ya kama hankalinta ba, balle ta yi sha'awar aikatawa.

Ta fito harabar gidan tana shirin tafiya, sai ga Mus'ab ɗa ɗaya tilo ga Hajiya Sa'a. Yana ganin Jamila ya tsaya. Duk da ba shiga harkarsa take yi ba, amma ta yi ƙoƙarin tare shi daga shiga cikin gidan, ya yi mummunan gani.

"Ina wuni?"

"Lafiya ƙalau Jamila. Ya ki ke?"

"Lafiya ƙalau Alhamdilillah. Amm Yaya Mus'ab ko za ka ajiye ni a hanya ne, ba na jin daɗi"

Ya yi murmushi ya ce "Me zai hana? Bari na kai wa Mummy saƙon nan"

Da sauri ta ce "A'a ai bacci take yi, ta ce kuma kar a tashe ta"

"Ok to mu je na ajiye ki" ta yi gaba ya bi ta a baya.

*****

Nana kuwa ita ma a wannan karon, basar da Sayyid ta yi, ta ƙi kula shi sam. Shi ma ya maze ya share ta.

Baccinta ya yi nisa sosai ta ganta a daji ita kaɗai ƙwal. Ta ɗaga kanta ta ga wani ƙaton tsuntsu yana shawagi a saman kanta.
Ba ta tsorata ba, ta ɗan ja numfashi ta ce "Ƙaisar laifin me na yi maka, ka zaɓi ka hukunta ni ta wannan hanyar? Me ya sa za ka zama dalilin zubewar cikina?"

Tsuntsunan nan saukko ƙasa, ya yi girgiza Ƙaisar ya bayyana. Ya zauna yana fuskantar ta ya ce "Komai ma kin yi mini, babu abin da ba ki yi mini ba, abin da ya dace nake yi"

"Ba ka tsoron Allah Ƙaisar, ba ka tsoron Allah ya kama ka da hakkina, abubuwan da ka ke aikata mini na cutarwa.
Kai ka yi mini, wannan tsohon ya yi mana, mijin nawa ma na fara daina gane kansa. Ya fara ƙoƙarin cutar da ni"

Ya ɗan kalli saman bishiya sannan ya ce "Babu abin da ban gaya miki  ba ai. Amm kin tuna abin da na nuna miki, Alhaji Zailani yana yi wa abokinsa? Da gaske ya faru a zahiri. Kuma tsafi gaskiyar mai shi, domin kuwa al'anura sun fara juya wa Alhaji Zailani baya. Nan zuwa wani ɗan lokaci zai rasa komai nasa. Lafiyar sa da dukiyarsa."

Cikin matsananciyar damuwa Nana ta ce "Dan Allah idan ka na dama ka yi wani abu a kai mana. Ka tona abin da aka yi masan"

Ya girgiza kai ya ce "Ba ma shiga abin da babu ruwanmu, ko warware wani abu da aka yi wa wani, muddin ba yarjejeniya aka yi damu, aka bamu damar yin hakan ba. Zan iya taimakonsa ne kawai bisa amincewar ki, da kuma umarnin ki. Zan gaya miki inda abin yake ya saka a je a tone, ko kuma ki je ki tone. Idan ba haka ba nan da kwanaki uku rak za a tono ƙwarangwal ɗin yaron nan, a kuma yin wani tsafin da ita."

Har Nana ta motsa baki za ta yi magana, sai kuma ta fasa, dan tana amincewa a taimaki Alhaji Fatuhu ba ta san me zai biyo bayan hakan ba, ka iya tabbatar da buƙatar Ƙaisar a kanta.

AREWABOOKS

Kasancewar ba ta salla, ya sanya har gari ya waye tana bacci.

Bayan ta yi wanka ta rasa abin yi, ta ɗebo kayan wankin ta, ta shiga banɗaki ta wanke. Nasa dama Habu ne yake zuwa ya ɗauka.

Ta gama, ta saka hijjabinta, ta ɗaukko bokitin, ta fito daga ɗakin. Yana kan kujera a daf da gate ɗin, yana aikin dafa shayi, gefensa ga radio tana yi.

Ba ta kula shi ba, ta zagaya baya, ta yi shanyar kayan nata. Ta fito ta ja ta yi turus tana kallon ikon Allah.

Siyama ce a tsaye, da ɗan ƙaramin flask a hannunta. Nana ba ta san me take ce masa ba, ta ga ya sauke rawanin fuskarsa ya saka hannu ya karɓi flask ɗin, ya yi magana.

Kawai ta shiga ɗaki, a ƙofar banɗakin, ta jefar da bokitin jin wani irin matsanancin ɗaci yana taso mata.

Ta cire hijjabinta kawai ta tsaya ta riƙe ƙugunta, ta tsaya tana jiran ya shigo, amma bai shigo ba, zuciyarta ta din ga raya mata, yana can su na hira da Siyama.
Kawai ta buɗe ƙofa ta shiga banɗaki, sai dai ta rasa uban abin da ya kai ta banɗakin ma. Ta gama tsayuwarta ta fito daga banɗakin.

Tana fitowa ta gan shi a tsaye, da flask ɗin a hannunsa, ya nufo ta zai yi magana, ta riga ta ɓarar da flask ɗin. Farfesun kifi da dankalin ya tarwatse a ƙasa.

Ya kalli gurin ya kalli yadda take huci, zuciya ta yinƙuro shi, sai dai ya ga Ƙaisar a bayan Nana, ya zubo masa ido.

Ya haɗiye wani abu, mai ɗaci. Ya kalli Nana ya ga yadda idonta ya rufe, ta fara ƙoƙarin wuce shi ta fita. Ya riƙe ta yana ci gaba da kallon Ƙaisar.

Ya kwantar da Nana a kan katifa, idanunta a rufe sai hawaye da yake fita, ta gefen idonta.

Ya durƙusa ya gyara gurin ta ɓarar da abincin.

Ya sake kallon yadda Ƙaisar ya jingina da bango, ya tsaya a kan Nana.

"Tun da ka yi abin da ka yi, ya kamata ka bani guri" Ya yi maganar yana kallon inda Ƙaisar yake.

"Gurin ka na zo ne? Idan ba gurin ka na zo ba, sai ka ƙyale ni"

"Ka zubar mini da ciki, kuma saboda rashin kunya, ka zo haɗa fitina a tsakaninmu"

Ƙaisar ya yi murmushi ya ce "Ina mamakin yadda Aljani yake shiga al'amuran bil adama har haka. Kai ka fara lalata cikin, ni kuma na zubar da shi."

Sayyid ya shafi fuskarsa ya ce "Waye Aljanin a tsakanin ni da kai?"

Ƙaisar ya ce "Ba da kai nake ba. Ka san da wanda nake"

Buzu ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Ka gaya mini, wane ne ni? Daga ina nake? Kuma suwaye iyayena? Me ya kawo ni ƙasar nan?"

"Ba ni za ka yi wa wannan tambayar ba, zuwa yanzu na san ka bambance tsakanin ni da shi"

"Haka ne, na banbance, yanzu ka tafi ka bani guri, ka bar ni da matata"

"Ba zan tafi ba"

Buzu ya durƙusa ya kwance rawanin kansa, ya cire rigar jikinsa, ya ɗago Nana da take cikin yanayin gushewar hankali.
Ya fara cire kayan jikinta, tamkar an aiko wa Ƙaisar saƙon mutuwa ya murtuke fuska.
Bai tsinke da lamarin ba, sai da Sayyid ya rungume Nana yana sumbatar bakinta.

Jikin Nana ya din ga rawa, tana fatan ta saka baki a maganganun su, amma ta kasa, tana ganin duk abin da yake faruwa, amma tamkar an ɗaure ta, ta kasa motsa ko da ƙaramin yatsanta.

Da ƙyar ta fizgo numfashi ta tashi a zabure, ta ce "Sayyid" ya taso da sauri daga inda yake zaune ya nufo ta.

Ya kasa magana, ita ma kuma ta kasa cewa komai, sai rarraba ido da take yi, ta yi zaton mafarki ne, amma ta ji ɗakin yana ƙarnin kifi, ga kuma flask ɗin da ya shigo da shi.

Da ƙyar ta ce "Ina wanda ku ke magana da shi?"

Ya kalli ɗakin ya ce "A ina?"

Ta kalli daidai gurin da Ƙaisar ya tsaya, ta ce "Wanda ya tsaya a nan, wani dogo"

"Ban yi magana da kowa ba" ya yi maganar yana girgiza mata kai.

Ta yi ajiyar zuciya ta ja ta zauna, tana jin kanta yana ciwo.

****

"Suwaiba" Alhaji Fatuhu ya kira sunanta.

Ta kalle shi ta ce "Ya dai?"

"Ba na jin daɗin jikina ne, kuma wani abu ne yake damuna"

"Me ke nan?"

"Ƙara ta za a kai kotu"

Ta waro ido ta ce "Kotu kuma? Me ka yi?"

"Kayan nan da suka yi ɓatan dabo, ranar Litinin zamu shiga kotu da 'yan kasuwa. Kujerata ma an sauke ni. Amma bai dame ni ba, kayan mutane nake tunani"

Ta kwaɓe baki ta kaɗa kai ta ce "Ai Alhaji Fatuhu duk ɗan da ya hana uwassa bacci, shi ma ba zai yi ba. Babu irin wahalar da bamu sha tare ba, amma abin Duniya na samuwa, ka auro yarinya ƙarama saboda ka ƙuntata mini, ka ci duniyarka da tsinke. Ai ga shi kai ma Allah ya kama ka" Ya yi zuru da ido yana kallonta.

Ta gama maganganunta ta bar masa ɗakin.

Tana zuwa bedroom ɗin ta, ta rufe ƙofa, hawayen da ta maƙale ta ba su damar gangarowa.

Ta hau nanata "Innalillahi wa innalillahi raji'un"

Ta ɗauki wayarta ta kira Yayanta.

Yana ɗagawa ya ji muryarta wani iri, ya ce "Lafiya kuwa?"

"Yaya Baban su Raudah wai za a kai kotu, 'yan kasuwa su na zargin ya cinye musu kuɗi, dan Allah ka yi wani abu a kai dan Allah"

"To ikon Allah, amma ba sai ki bari sai da Safe ba, kya kira ni. Amma ku kuma kin tabattar bai ci kuɗin ba?"

Suwaiba ta ce "Yaya kai ma ka san shi da gudun Duniya, da abin mutane wallahi zan iya rantsuwa bai ci kuɗin kowa ba"

"Ki bari zan kira ki da Safe" ta ajiye wayar jiki a sanyaye cikin damuwa.

Kasancewar a sashen Fadila yake, ta fahimci damuwa a tattare da shi, sai dai fafur ya ƙi gaya mata, ya lallaɓa ta ta yi bacci.

*****

Da daddare Nana ta kasa karanta Alqur'ani, amma wannan karon ta samu ta saka a wayarta, ta daɗe tana saurara tana jin nutsuwa na ratsa ta.
Kasancewar jini ya ɗauke, ya sanya ta yi sallar Isha'i, ta kwanta karatun Alqur'ani yana tashi ƙasa-ƙasa a wayarta.
Tana kallon Sayyid, ya shirya ya kwanta a ƙasa, gurin da yake kwanciya da. Gaba ɗaya sai ta ji ta damu. Ta daɗe idonta biyu, tana jira ta ga ko zai ta so, amma bai tashi daga gurin ba.
Ta tashi a hankali ta nufe shi, har ta ƙarasa kusa da shi, ta kwanta.

Ba ta ce masa uffan ba, ta caza masa hankali har ya biye mata.
Bayan wani ɗan lokaci ya numfasa ya ce "Kin daina fushin?"

"Ba kai ka saka na yi fushin ba? Amma ka yi haƙuri"

"Me na yi miki?"

"Me yasa za ka yi wannan yarinyar magana, har ta baka abu ka shigo mini da shi ɗaki?"

"Ki na gurin kin san meyafaru?"

Ta tashi daga jikinsa, ta ce "Ni ba na son jin meyafaru kawai babu ruwanta da kai, kar ka sake kula ta. Dan wallahi za ka iya nema ta ka rasa. Idan ka na son ta maye gurbina ba wani abu, ni zan iya tafiya ta na baku guri".

"Ki daina faɗar abin da ba za ki iya aikatawa ba"

"To ka ci gaba, zan baka mamaki kuwa" ta yi maganar tana tashi zaune, da nufin ta bar masa gurin."

Amma ya riƙe ta gam, yana yi mata numfashi a wuya. A gurin suka kwana tare. Sai Asuba bayan ta yi wanka ta yi salla, ta koma kan katifa.

Tana tsaka da bacci, ta ji yana tattaɓa ta, ta buɗe idonta ta kalle shi tana yanutsa fuska, saboda bacci ne a kan ta sosai.
Wayarta ya ajiye mata a daidai kunnenta.
Waƙar Ali jita ce take tashi, ta Aminiya. Shiru ta yi tana sauraren baitukan tana kallon kyakyawar fuskarsa da ya tsare ta da manyan idanunsa yana kallonta yana murmushi.
Ita ma murmushin ta sakar masa, ta yinƙura ta tashi zaune, ita sam ba ta san da waƙar ma a wayar ba, kasancewar ba gwanar jin waƙa ba ce, amma har cikin zuciyarta take jin baitukan, tamkar shi ne yake rairai
mata.
Gaba ɗaya suka manta, da batun saɓanin da ya shiga tsakaninsu.

(BAYAN MAKONNI BIYU)

Gaba ɗaya Fadila ta rasa abin da yake yi mata daɗi, hankalinta ya ƙi kwanciya, tun da aka fara zaman kotu ta ji halin da ake ciki ta rasa abun da yake yi mata daɗi, yanayin yadda shari'ar ke gudana, za ka san da gayya ake yi, kawai shi ake son ya tozarta.
Dan tashin farko Alƙali cewa ya yi a tsare shi, sai an ajiye wasu miliyoyi da kadarori, za a sake shi.
Wasu tuhume-tuhumen ma, bai san da su ba, sai ranar da aka fara zaman kotun, sannan ya san da su. Har wasu maƙudan kuɗin, da ake zarginsa da sama da faɗi da su, a lokacin da yake shugabanci.
Haka aka sayar da wasu daga kadarorinsa, aka bayar sannan aka ba da belinsa.
Kotu ta yi umarnin a yi gwanjon kadarorinsa a sallami mutane kuɗinsu.

*****
Alhaji Zailani, tare da Malam Gambo suka koma gurin da suka binne, jaririn nan, su ka tono ƙwarangwal ɗin sa, duk ya zagwanye. Suka saka a akwati, suka tafi da shi.
Ɗakin da Malam Gambo yake tsaface-tsafacensa su ka je. Ya ɗaukko ƙwarangwal ɗin jaririn, aka babbaka wata irin wuta, aka ɗauki ƙwarangwal ɗin jaririn nan, ya rubuce jikin da sunan Alhaji Fatuhu, ya zana wasu hatimai, ya nannaɗe su a jikin ƙwarangwal ɗin aka saka a cikin wutar nan.
Malam Gambo ya din ga zuba wani magani a cikin wutar, ya kawo wasu irin layoyi da ya zana hatimai daban-daban, ya din ga jefawa a cikin wutar. Alhaji Zailani kuma yana kiran sunan Alhaji Fatuhu.
Sai da ƙwarangwal ɗin nan ya yi baƙi ƙirin, zaren da aka naɗe ƙwarangwal ɗin, ya kama jikin sosai. Ya kuma naɗe shi da wani zaren, sannan ya naɗe da likkafani, su ka je suka samu wata tsohuwar rijiya, suka jefa a ciki.

Alhaji Zailani ya koma gida, kulle kansa a cikin ɗaki, ya din ga ɓaɓɓaka wata irin mahaukaciyar dariya, tamkar zai haukace.

Ya ce "Alhaji Fatuhu ka gama yawo, yanzu sai na ga wanda za ka hura wa hanci, wai ka ga mai kuɗi kuma mai tsoron Allah, mu zuba mu gani. Wannan burin nawa ya cika, saura kuma waccan yarinyar"

Alhaji Fatuhu kuwa, sun dawo daga kotu, Yayan Hajiya Suwaiba, lauyan da ya tsaya masa, yana ta yi masa nasiha a kan ya karɓi ƙaddara.

Alhaji Fatuhu ya ce "Wallahi Barrister, na karɓi ƙaddarata. Na kuma gode wa Allah. Abu ɗaya nake tunani iyalina na saba musu da rayuwar jin daɗi da kwanciyar hankali. Ina jin tausayinsu fiye da abin da ya same ni"

Cikin tausaywa Barrister ya ce "Na sani Alhaji, tabbas kai mutum ne mai kyautatawa iyali. To yanzu ne ranar da za su nuna maka halacci su ma, a yi haƙuri"

Alhaji Fatuhu ya ce "Babu komai, mun gode Allah"

Ji ya yi tamkar ana ƙoƙarin fizgo ƙwaƙwalwarsa. Ya yi wata irin zabura, ya riƙe kansa gam. Barrister ya ce "Alhaji lafiya dai?"

Ya girgiza kai ya ce "Zafi nake ji" kafin ya kuma wata maganar, ya yanke jiki ya faɗi a gurin.

Nana tamkar tana kallon talabijin, haka ta ga komai a cikin mudin da Ƙaisar yake nuna mata.

Yana gefe yana rubutunsa, ita kuma ta zuba uban tagumi tana kallon mudubin.

"Shigen irin wannan sihirin aka yi wa mijinki, shi ne wannan wutar da yake cewa tana ci a jikinsa. Sai dai shi nasa ya sha bambanda wannan ta wasu fannukan"

Nana ta zabura ta kalle shi ta miƙe tsaye ta ce "Ƙaisar ka yi mini bayani, waye ya yi masa asirin? Kuma daga ina yake? Suwaye iyayensa?"

Ya ɗago ya kalle ta ya ce "Kin manta sharaɗin ne?"

Ta yinƙura za ta yi magana, ta yi ido huɗu da Sayyid, yana kusa da ita, ya zuba mata ido.

Ta yi ajiyar zuciya.

"Waye Ƙaisar?" Ya jefo mata tambayar babu zato babu tsammani.

Ayshercool
08081012143.

45

Ganin abun ba na ƙare ba ne, ya sanya Nana yinƙurawa da ƙyar, jikinta babu ƙwari, ga sanyi tana ji.

Ta ɗauki hularta, ta zubo ruwa a kwano, ta zo ta ajiye a gefensa, ta zauna da niyyar karanta abin da ya sauwwaƙa a Alƙur'ani, ta busa a ruwan ta shafa masa. Amma ta ji komai ya ɗauke daga kanta, ta kaɗa ta raya amma ta kasa tuna komai.

Ta janyo wayarta, ta fara laluben folder karatun Alkur'ani, amma wayar ta fara haske tana ɗaukewa tamkar ta ci screen, abin fa ba taɓa yi ba sai yau.

Ta ajiye wayar jikinta yana rawa, ta rasa abin yi, ga shi yana kwance sai tsuma yake yi. Tashi ta yi ta nufi wardrobe, ta buɗe watso kayanta ƙasa. Jakar gurin sarkin baka, ce ta faɗo daga cikin kayan. Nana ta durƙusa ta ɗauka, ta nufi gurin da yake kwance. Ta ɗora masa a ƙirjinsa. Kamar ta ɗora masa wuta, haka ya zabura, ya juya a hankali ya gyara kwanciyar sa, ya daina wannan tsumar ya hau bacci.

Ta saka hannu ta ɗauki jakar, tana ƙare mata kallo. Sam ba ta ga wani abu na musamman a tattare da jakar ba. Ta ajiye ta, ta kwanta a gefe tana jin yadda jikinta yake yi mata ciwo.

Bayan wani ɗan lokaci ya yi juyi a hankali, ya kalli agogon ɗakin, ya kalle ta ya yinƙura ya tashi, ya yi alawala ya yi sallar la'asar. Ya zauna a kan sallayar ya yi shiru, fuskarsa na bayyanar da damuwa.

Nana ta tashi daga gurin da take. Ta ja ta zauna sosai ta gyara zamanta. Ta ce "Sayyid na kasa fahimtar abin da yake faruwa, ban sani ba ko na yi wani abun da na ɓata maka rai ba."

Ya sunkuyar da kai ya yi shiru, na wani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login