Showing 78001 words to 81000 words out of 189977 words

Chapter 27 - BUZU BOOK1 COMPLETE HAUSA NOVEL

18 Jan 2026

967

ne, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, wannan banzan yaron ashe ba alkhairi ne a gare ki ba, shiyasa aka yi uwar watsi da shi" ci gaba da kallonsa kawai Nana ta yi, tana jiran ya kai ƙarshen bayanan.

"Yanzu dai wani bawan Allah ne ya zo neman auren ki, kuma na ce na ba shi, na yi masa bayanin halin da ake ciki da wancan matsiyacin yaron, ya ce kar na damu, dubu ɗari biyu ya bayar a biya Saleh kuɗinsa, ke kuma ya ce nan da sati biyu zai aure ki, ɗaurin aure kawai za a yi baya son kowa ya sani, kawai zai zo ya ɗauki matarsa shikenan Allah ya dube mu Nana"

Idanun Nana suka kaɗa su ka yi ja, ta ce "Baba wani irin aure ne za a yi shi na sirri? Da ba a so kowa ya sani? Waye ma tukuna, sannan mece ce sana'ar sa?"

A take Baba ya fusata ya ce "To dan ubanki zan yi miki zaɓen tumun dare ne? Koma wane ne za ki gani ai"

"Baba na san ko waye, kuma wallahi muddin ka dage sai ka aura mini shi, wallahi zan iya kashe kaina, ko na bar gidan nan"

Baki buɗe Baba ya kalli Nana, "Ni ki ke gaya wa za ki kashe kan ki, ko ki bar gidan nan?"

Tuni hawaye ya wanke mata fuska ta ce "Baba wane irin aure ne, mutum zai ce, ba ya so a sani. Alhaji Zailani ne, mutumin da nake aiki a gidansa na sani." Ta yinƙura ta tashi, ta bar wa Baba gurin tana kuka.

Bil haƙƙi da gaske, zuciyarta ta din ga raya mata ta kashe kanta har lahira, kawai ta huta da wannan masifar. Gani take kamar gaba ɗaya babu wanda duniya ta juya wa baya, ba ta yi da shi tamkar ita. Duk inda ta juya babu daɗi.

Mama kuwa tun da Baba ya zo mata da maganar nan, ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta rasa abun da yake yi mata daɗi. Wani abu mai masifar zafi ya tsaya mata tun daga ƙirjinta zuwa bakinta. Tana ganin ya za ayi a ce, ga su Jamila a zaune, Nana ta samu hamshaƙin mai kuɗi haka.
Ana yin sallar magariba Baba ya fita masallaci, ita ma ta yafa mayafinta ta fice.

*****

Jamila ce a zaune a gaban Hajiya Sa'a, fuskarta ɗauke da matsanancin tsoro take kallonta.
Ta dafa kafaɗar Jamila ta ce "Kin tabatta ta sha maganin da aka ba ta a kunun ayar?"

"Ta ce mini ta sha, amma ba a gabana ta sha ba"

"Shikenan kar ki damu, ki kwantar da hankalinki. Za mu ci gaba da ƙoƙari har zuwa lokacin da zamu samu abin da muke so. Abin da nake so da ke shi ne ki zamo mai riƙe mana sirri, za ki samu kuɗi Jamila, irin wanda ba ki taɓa zaton riƙe su, ba za ki yi rayuwar ƙunci da talauci irin na gidanku ba. Nana ita kawai muke buƙata idan ba haka ba, ba zaki zama abin da nake hangen ki zama ba" ta yi maganar cikin bawa Jamila ƙwarin gwiwa.

Mama ce zaune a cikin wata rumfa, tare da wani mutum, ta tattara masa hankalinta gaba ɗaya.

"Ai na gaya miki Rabi, muddin ba ki yi da gaske ba, wallahi ki na ji kina gani, sai dai ke da yaranki ku yi mata biyayya. Tasirin taurarinta ba za su bari na yaranki su haska ba."

Cikin damuwa ta ce "Ai na ga alama, 'yar shegiya kwatsam mutum ya fito wai aurenta zai yi, a zuwa ɗaya ba ka ga uban kuɗin da ya bawa ubanta ba, bai gaya mini nawa ba ne ba, amma wallahi na san da yawa. Kalli aikin raino take yi, amma albashin dubu talatin aka bata, ta bawa ubanta. Wallahi ko buɗe ido ba na ƙaunar na yi na ganta. Ni dai dan Allah ka wargaza maganar nan, kar a yi auren nan. Duk da na ji tana cewa uban ba ta so"

Ya yi murmushi ya ce "Ta kwana gidan sauƙi, yau zan kwana aikin, da ni da almajiraina, za a yi farraƙu mai zafi. Ki zube kuɗi kawai abin da yake hannunki a fara"

Haka ta buɗe jakarta, ta ciro kuɗi ta ajiye masa.

****
Tinkis-tinkis yake tafiya, kamar wani bujimin sa, ya nufi motar da zai hau ya fita, sai dai yana ƙarasawa Nana ta miƙe tsaye. Sai da ya ɗan tsorata da ganinta.

Ya ce "Lafiya dai ko?"

"Wani dalilin ne ya sanya ka je ka samu mahaifina, ka ce masa zaka aure ni?"

Yayi dariya tare da shafa tumbinsa ya ce "Dalilin da yasa ki ka ƙi amincewa da buƙata ta, ya sanya na biyo ta in da dolen ki ki yarda. Amma na yi mamakin yadda ƙwaƙwalwarki take aiki da har ki ka yi saurin gano ni ne. Sai daga baya na gane ba iya taurarinki nake buƙata ba. Ina buƙatar aljanin da yake tare da ke ma. Kuma wannan ƙwaƙwalwar ta ki ma ina buƙatar ta"

Cike da ƙwarin gwiwa Nana ta ce "Ni na yi maka kala da wadda za ta auri fasiƙi ne? Mazinaci baya auren kowa face 'yar uwassa mazinaciya, ni ba irinka ba ce ba, kuma Ubangiji mai adalci ne, ba zai yi mini wannan jarrabawar ba"

Ya sake yin dariya ya ce "Akwai abin da ba a kuskurewa ƙaddara. Nima zinar da nake yi ta neman duniya ce, kafin na mutu zan tuba. Kuma tun da babanki uban kwaɗayi ne da son abin duniya, zan ta ba shi abin da yake so, domin buƙata ta biya. Tun da ke ba ki da wayo, ba ki san inda duniyar ta sanya a gaba ba." Ya buɗe motarsa ya shiga ya zauna, Nana ta bi shi da kallo cikin ɗacin rai.
Ya sauke gilashin motar ya kalle ta ya ce "Ki kwantar da hankalinki, na ga kina da abubuwan da zan iya mora da yawa a jikinki, dan haka ko na aure ki zan iya zama da ke na ɗan lokaci" ya fara jan motarsa ya baro parking space ɗin.

Ƙaisar ta gani ya bayyana, ya sha gaban motar, yana kallonta, babu tsammani sai ga wannan tsohon da take gani, mai kama da shi, ya keto ƙasa ya fito ya yi jifa da ƙaisar gefe.

Gabanta ne ya faɗi, sai da ta dafe ƙirjinta ta ja da baya, ta ɗaga kanta ta ga har Alhaji Zailani ya bar harabar gidan, sai dai idanunta suka sauka a cikin nasa da ya ƙure ta da ido ko ƙiftawa ba ya yi. Kamar wadda ya yi wa dabaibayi ta kasa motsi.

"Antyn Haidar, yau ma karen ne, na ganki a nan a tsaye" kamar wadda ta tashi daga bacci, ta kalli Yusuf ta ƙaƙalo murmushi ta ce "A'a ba karen bane, yanzu zan shiga ciki"

"Ai kuwa ki yi sauri, dan mutumin naki ya tashi yana ta bin Mummy yana tambayarta ki na ina"

Nana ta ce "To bari na shiga, a dawo lafiya" ya amsa mata da Allah ya sa.

Ta wuce ta shiga.

Hajiya Amina ce take yi wa Nana faɗa, ganin ta zubo abinci za ta ci, amma ta bar wa Haidar sai ci yake yi, ita kuma ta zuba uban tagumi.

"Nana babu wanda ba shi da damuwa a rayuwar nan, kowa haƙuri yake yi, kalli 'yan kwanakin nan duk kin rame, haba Nana me yake damun ki ne" ta kalli yadda Hajiya Amina take damuwa idan ta ganta cikin damuwa, yaya za ta ji idan ta ji ta auri mijinta, sun yi auren sirri. Wasu hawaye ne masu raɗaɗi ke ƙoƙarin zubo mata, amma ta haɗiye ta ce "Rayuwa ce sai Alhamdilillah Hajiya, amma in sha Allah na daina"

"Ko kefa, amma a ce da ƙanan shekarun ki, ki na damuwa tun ba ki yi aure kin tara iyali ba, ai sai wani ciwon ya kama ki"

****
"Rabi ni fa ban ga Nana ba, ina ta shiga ne?"

Mama ta kwaɓe baki ta ce "Ina na sani, ajiyarta ka bani ne? Tun farar safiya ta fice"

"Ta fice da farar safiya? Kar fa ta aikata abin da ta ce, dan yarinyar nan ba hankali ne da ita ba"

Mama ta kalle shi ta ce "Au me ta ce?"

"Cewa ta yi wai ba zata auri mutumin nan ba, idan na matsa kuma guduwa za ta yi ta bar gidan"

"Hmm baban su Jamila kenan, ai na daɗe da gaya maka Nana ba aljanu ne suke hana ta aure ba, tsagwaron iskanci ne wallahi. Idan Saleh talaka ne ta ƙi aurensa, yanzu ga mai kuɗi shi ma ta ce ba ta so, tana maka baƙin cikin fita daga wannan ƙangin wahalar. Kawai ka nuna mata kai ne ubanta, kai ka haife ta ba ita ta haife ka ba"

Ya ja numfashi ya jinjina kai, cike da gamsuwa.

"Amma ka gaya masa ciwonta?"

Baba ya ce "A'a ba zan gaya masa ba, kar ya gudu, daga baya a yi wadda za a yi."

Nana kuwa da taho gida, ta nemi dakalin wani gida ta yi zamanta, dan ko tinkarar gidansu ba ta son yi. Har a ka yi sallar magariba ta daidaici Baba yana masallaci, sannan ta shiga gida.

Bayan ta yi sallar isha'i ta ɗaukko Alqur'ani ta ajiye a gabanta, tana so ta karanta, sai dai ta buɗe ta kasa karanta komai, ta lula duniyar tunani, ƙwaƙwalwarta ta din ga tariyo mata ƙira'ar malam Auwal. Har yanzu tana jin kewarsa, yana cikin mutanen da ba za ta manta da su a rayuwarta ba. Ko kuɗin nan da ta karɓa na albashi sai da ta yi masa sadaka.

Ji ta yi ana nishi a gefenta, ga wani irin huci da yake dukan fatarta, ta buɗe idonta ta kalli gefenta, ta ga Ƙaisar a kwance, hannunsa ɗaya ya yi baƙi ƙirin, sai numfarfashi yake yi.

Da sauri Nana ta nufe shi ta ce "Me ya same ka haka?"

Ya ɗago hannunsa da ya yi baƙi ya ce "Ba a gaban ki a ka yi jifa da ni ba, garin in ɗauki fansar abin da a ka yi miki?"

Ta ɗan waro ido ta ce "Dama akwai wanda ya fi ka ƙarfi?" Ya ja jikinsa ya tashi zaune da kyar, sai a lokacin ta ga ya ji raunuka sosai, duk gurin da ya ji rauni shi ne ya yi baƙi sosai.

"Ina ƙara nanata miki, halin da muka shiga, muddin ki ka ci gaba da zama a gidan nan, amma baƙin taurin kanki ya sanya kin nace"

"Wasu lokutan, ba na gane in da ka dosa, wasu lokutan kamar ka damu da ni, amma cutarwar da ka ke yi mini ya sanya a duniya babu wanda na tsana sama da kai. Duk ka kashe mutanen da nake ƙauna, kuma alamu sun nuna da gaske haukata ni ka ke so ka yi"

Ya miƙe dogwayen ƙafafuwan sa ya ce "Ni ban kashe kowa ba, duk wanda ya mutu lokacinsa ne ya yi, ni ban kashe kowa ba. Amma muddin babanki ya aura miki wannan mutumin dukkansu zan haɗa, jininsu ne zai zama jinin bil adama na farko da zan sha"

"Baban nawa?" Nana ta yi magana cikin zare ido.

"Shi ɗin"

"Amma kuwa da...

"Au ki na ji na ma ina ta baloƙoƙo ki ka yi mini banza ko?" Nana ta ɗaga kai ta kalli Baba.

"Gidan uban wa ki ka je yau ba ki dawo da wuri ba?"

Ta girgiza kai ta ce "Babu ko ina"

"To daga yau kar ki sake zuwa gidan aikin, tun da mai abu abinsa ne ya ce ya ji ya gani yana sonki. Ya ce mini ya rage daga sati biyun nan, juma'ar nan ta jibi za a ɗaura muku aure kowa ya huta!"

Ayshercool
08081012143
Page 24

"Baba dan zatin Allah, ka duba lamarin nan, wallahi ba na son mutumin nan, ba shi da kirki dan Allah Baba ka yi mini rai"

"Nana duk rashin kirkinsa, bai kai talauci rashin mutunci ba, idan ki ka ga ba a yi auren nan ba, to sai dai idan wani mijin ki ka kawo, ke ko wani ki ka kawo ɗin wallahi ga dai mai rufin asiri ba zan bawa wani ke ba, gara ma ki yi haƙuri, ki tattara komatsan ki"

"Ya Allah, Ya Allah Astagfirullah" ta faɗa duk a jejjere."

"Mahaifinki ba zai taɓa canza hali ba, sam ta kansa kawai yake yi"

Nana ta ɗaga kai a karo na biyu, da ta sake ganinta a gurin ƙaisar ta ce "Koma mene ne kai ne sila, kana ɗaya daga cikin dalilan da ya sanya Baba son rabuwa da ni ko ta halin ƙaƙa."

Ƙaisar ya ce "Kar ki ga laifina, tun da na baki zaɓi tuntuni, ki ka tsaya wahalar da kan ki" ya yi maganar yana rubutu da hannunsa ɗaya mara ciwon.

Ya ɗora da cewa "Matar babanku ta je gurin Malamin da ya zane ki rannan, a kan a wargaza maganar auren nan, dama ya kan yi mata aiki ire-iren waɗannan, idan Allah ya taimake ki aikin ya ci, sai ki ga an fasa, kalli abin da aka yi" mudubin da ya saba nuna mata, ya nuna mata.

An raba wata 'yar tsana gida biyu, an rubuta sunan Nana a jikin ɓari ɗaya, ɓari ɗaya kuma Alhaji Zailani, ana ta wani surkulle.

Ya ɗora da cewa "Abin da ba su sani ba su duka su ne, shi wannan mutumin ya kai matakin ƙololuwa a ƙungiyar asiri, to wani asiri ne kuma zai kama shi?"

Nana cikin kuka ta ce "Wannan malamin shi ne ya zane ni rannan"

Ƙaisar ya kwashe da dariya, ya ci gaba da rubutun sa.

Cikin kuka ta ce "Kuma duk saboda kai, Allah ne gatana, kowa nice ba ya so kawai" ta yi magana tana ƙarewa malam Ɗayyabu kallo a jikin mudubin.
Sai kuma ta daina ganin malam Ɗayyabu, sai Jamila tare da Hajiya Sa'a da kuma maman khairat.

Da sauri ta kalli Ƙaisar ta ce "Wannan matar ba ita ka ce mini ta bayar da jinin Muhsin a ƙungiyar asiri ba? Amma me yasa da na tashi na manta, na ganta na kasa tunawa?"

"Ashe kin san ainihin abin da ya faru, ki ke cewa na kashe wanda ki ke ƙauna?" Ta yi shiru tana satar kallonsa.

"Shi ma wannan yaron na yanzu, idan ba ki yi wasa ba, ana daf da shafe tarihinsa a duniya, akwai yiwuwar 'yan ƙungiya su nemi a ba su jininsa"

Cikin matsanancin tsoro Nana ta kalli Ƙaisar ta ce "A'a kar mu yi haka da kai Ƙaisar, dan Allah yaro ne fa bai san komai ba."

Ya ce "Ni babu abin da zan yi da shi, kawai dai na gaya miki ne. Hatta ɗan da babarsa za ta haifa a nan gaba kaɗan, an gama shirya yadda za a yi da shi" A razane Nana ta tashi tsaye, amma sai ta ganta a tsakar ɗakinsu. Gigicewa ta yi ta nufo tsakar gida, ta ga tsakar gidan baƙi ƙirin, dare ya tsala.
Sai kuma ta fara ƙoƙarin tuna abin da ya razanata, har ta fito tsakar gida, amma ta kasa tuna komai.
Ta koma ta zauna jikinta yana tsuma, ta rasa ma wace addu'a za ta yi. Zuwa yanzu idan da sabo ta saba da matsanancin bugun zuciya saboda yawan razana da take yi.

Ta haɗa kanta da gwiwarta, ta rasa ma wani tunanin za ta yi, kasancewar bacci ɓarawo ne, ya sanya ya yi nasarar yin awon gaba da ita.

Sai dai ta din ga ganin Haidar, yana ta kuka tana ƙoƙarin rarrashin sa, amma ya ƙi yin shiru sai tsala ihu take yi. A wani ɓangaren kuma na mafarkin, ta ga Shukura a dokar daji, tana ta uban gudu da tsohon cikin nan, jikinta babu suturar kirki, duk jikinta raunika, kanta babu ko ɗan kwali, ga hannunta riƙe da Haidar sai gudu take tana kururuwa. Bayanta wani mutum ne ya rufe fuskarsa da baƙin ƙyalle yake bin ta, hannunsa riƙe da wuƙa ga jikinsa sai ɗigar da jini yake yi.
Kukan Hidar sai amsa kuwwa yake yi, yana kiran sunan Nana.

A wannan karon ma a razane ta tashi, da "Innalillahi wa innalillahi raji'un" daidai lokacin aka tayar da sallar asuba a masallaci.

Gudu-gudu sauri-sauri, ta fita ta yi alwala, ta gabatar da raka'atanul fajar, sanan ta yi sallar asuba. Ta zauna tana tasbihi ta din ga tunanin 'yan kwanakin nan ba ta iya karanta Alqur'ani. Azkar ɗin ma sai ta shafe kwanaki ba ta yi ba, ganin ko ta yi babu abin da yake canzawa. Sai kuma ta tafi tunani, wataran a islamiyya da ta farka ta ga malam Auwal a kanta, yana ta raira karatun Alqur'ani, hakan ya tabattar mata da ƙaisar ya ziyarceta.
Bayan ya sanya ta tashi, ta yi alwala ta dawo ta zauna, ya dube ta ya ce "Nana idan kin je gida kina azkar kuwa? Kuma kina karanta Alqur'ani?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.

"To me yasa?"

Cikin rauni da karaya ta ce "Ko na yi Allah ba ya kare ni, na fi shan wahala ma idan na yi" da sauri ya tari numfashinta ya ce "A'uzbillahi, waye ya gaya miki Allah ba ya kare ki? Da ba ya kare ki da Allah kaɗai ya san abin da zai faru da ke. Addu'oin da ki ke yi, da larurar da ki ke fama da ita, ba ya nufin karatun Alqur'ani da azkar da ki ke yi ba sa yi miki amfani, jarrabawa ce, daga Allah. Ke kina ganin Aljani na bibiyar marasa ji? Sun fi bibiyar nutsatsu masu addini, hakan na nufin jarrabawa ce, mai imani ba a barin shi haka babu jarrabawa. Kuma burinsu kenan ki daina ibada, su sake samu su miƙe ƙafa a jikinki, su ci gaba da azabtar da ke. Musulma ce ke, ki zama mai kyautatawa Allah zato".

Ko da ta zo nan a tunaninta, sai ta ce "Astagfirullah, wa a tubu ilaihi"

Ƙarfe tara da rabi na safe, Baba ya fito tsakar gida yana neman Nana. Mama ta ce "Ba fa ta nan"

"Ban gane ba ta nan ba, ina ta tafi? Ba na kafa mata dokar kar ta sake fita ba, ana daf da ɗaura mata aure?"
"To ka isa da ita ne? Ai ba ka isa ka gaya mata ta ji ba, ka yi kaɗan"

Ƙwafa ya yi ya ce "Za ta dawo ta same ni, zan ci ubanta a cikin gidan nan wallahi" Bayan ya gama bambaminsa ya fita, Mama ta koma ɗakinta ta ɗauki wayarta ta kira Malam ɗayyabu.

Sai da ta kusa tsinkewa ya ɗaga, "Malam yaya a ke ciki? An gama aikin ne?"

"Eh a kan aikin muka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login