Showing 27001 words to 30000 words out of 155081 words

Chapter 10 - TAKUN SAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

25 Dec 2025

688

Yaya Abubakar bai bada fuska ba.
      “K zoki wuce ciki ki kwanta”. Yaya Abubakar ya dakatar da ita dan bayasan wani dogon magana a yanzu. Yasan kuma indai Hibbah ce bataƙi su kwana ana shashanci ba. Baki ta tura gaba sim-sim ta nufi sashensu.
     Yaya Muhammad yay ɗan murmushi yana kallon Yaya Abubakar ɗin. “Siddiq yau fa gaba ɗaya ka zama masifaffe. Kasa duk auta ta firgita da kai”.
        “Tana da cika ciki ne wani lokacin”. Yaya Abubakar ya bashi amsa yana kashe motar. Yaya Ammar yace, “Dama hakan kowa ke mata da mun huta da shegen ƙiriniyarta tamkar ƴar mage”.
      Kusan duk sai da sukai ƙaramar dariya. Da ga haka suka shige makwancinsu kowa ya nufi ɗakin barcinsa.
        Hibbah ma da ta shiga tanata zunɓure-zunɓure shirin barcin tai tana kunkunin wai dan anga Ummi bata nan kowa ya tsaneta. Gobe a asibiti zata kwana bazata biyosu su cinye ta ba.
         Da ƙunkunin dai harta kammala shirin barcin ta kwanta bayan tayi addu'a. Sai kuma a lokacin tunanin duk abinda ya faru a wannan yini ya shiga dawo mata. ALLAH dai ya taimaketa barci barawo yaci galaba akanta batare data shirya hakan ba.

*_WASHE GARI_*.

           Yau Yaya Umar ne ya shigo yama Hibbah knocking. Sai da yaji ta tashi sanann ya juya ya fita bayan ya mata gargaɗin karta koma barci ta shiga kitchen idan sun dawo salla zaizo ya tayata haɗa breakfast. Da to kawai ta amsa masa dan harga ALLAH barcin bai isheta ba. Sai dai sanin halin masifarsa yasata bin umarninsa bayan ta idar da sallar tai azkar ta fita kitchen ɗin. Bata jima da fara aikin ba suka dawo. Su dukansu babu wanda bai iya girki ba dan Ummi babu abinda bata sakasu na aikin gida. Shiyyasa bata taɓa damuwa da zama da ƴar aiki ba tun da suka fara tasawa.
     Yaya Umar ne ya tayata sukai breakfast ɗin. Yaya Usman kuma yanata ƙoƙarin gyara gidan shi da Ammar da ya tayasa dan jikin nasa da sauƙi bakamar jiya ba. Magungunan da aka basa sun taimaka masa matuƙa. Cikin kankanin lokaci suka kammala komai tsaf kowa ya tafi dan watsa ruwa. Sabo da fita aiki yasa duk suka hallara akan lokaci bisa dining. Sai uwar latti ce ko motsinta babu sai da Yaya Muhammad ya je da kansa yay mata knocking.
           Koda ta fito masifa Yaya Umar da Usman suka hauta da shi na sakasu yin latti kamar kullum. Cikin son a kareta ta kalla Yaya Abubakar da Muhammad. Duk murmushi sukai mata da nuna mata kujera alamar ta zauna ta rabu da su Umar ɗin. Fuska a kumbure taja kujera ta zauna kuwa. Da ga haka suka fara karyawa.
      Sunyi nisa sosai acin abincin Abba ya shigo fagan-fagan Hajiya Mama biye da shi. A tare duk suka ɗago suka zuba musu ido. Sai wani irin tsoronsu da shakkarsu ya shigi su Abban lokaci guda. Yaya Muhammad ne ya fara ɗaule kansa ya maida ga abincin gabansa. Suma sauran duk sai suka yi kamar yanda yay ko gaishesu basuyi ba.
      Cikin masifa Hajiya mama tace, Kunci ubanku marasa mutunci. mu zaku kalla ku watsar tamkar wasu kashi?”.
     A mamakinsu ko motsi babu wanda yayi, sai ma cigaba da cin abincinsu sukeyi hankali kwance. Hajiya Mama da Abba sukai galala a tsaye kamar gunkuna suna kallon sabon salon iskanci. Suko sunyi tamkarma basusan da zamansu a wajenba.
     Wani irin baƙin cikine ya lulluɓe Abba ya shiga zazzaga tujara musamman akan fiddo Ammar, dan dama tun jiya ɗan sandan ya kirasa ya sanar masa. Ya kuma tabbatar masa da Abubakar yana tare da manyansu sosai, idan ya matsa akan Ammar ɗin tofa wata da tafi wadda suka shirya zata taso. Hakan yasa Abbana ɓam da bakinsa. Ya dai ɗauka alwashin zubarma da Ummi tujara tare da sauke duk fushinsa a kanta. Shiyyasa yana kammala sallar safensa da ya keyi a gida kullum bayan rana ta fito ya nufi sashen hajiya Mama ya sanar mata. Shine fa suka taho yima Ummi taron dangi basu san ma bata gidan ba. A zatonsu kuma su Yaya Abubakar ɗin sun fita.
           Duk iya tujarar da sukeyi babu wanda yay koda motsi balle nuna yasan da zamansu a wajen har suka kammala breakfast ɗinsu Ammar da Hibbah suka kwashe kayan zuwa kitchen. A gurguje suka wanke kwanikan ita da shi su ka fito dauke da basket ɗin abincin da suka shiryama Ummi irin wanda doctor da suka kira ya tabbatar musu zata iya ci tunda ta farfado tun daren jiyan.
     Har yanzu Abba da Hajiya Mama na a sashen suna zubda ruwan tujara. Yayinda kuma babu wanda yay musu koda tari. Hakanne ya sake harzuƙa musu zukata da wanann sabon salon rainin wayon su Yaya Muhammad ɗin. A gabansu kuma suka kulle kowanne ƙofar ɗaki da ke a sashen har kitchen sukai ficewarsu suka barsu a falo. Wannan al'amari yayi matuƙar bakanta ran Abba da Hajiya mama. Kai har ma Momy da ƴaƴanta mata huɗu da duk suka fito saboda hargowar su Abban.
         Motar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar duk suka shiga yau ma suka fice batare da kowannensu ya hau mashin ba.

     Bayan fitarsu tujara ta gidan duniya babu irin wadda Abba da hajiya mama basuyiba a gidan. Ummi ta sha gori da tonon sililin asalinta. Sai da sukayi mai isarsu sukaga babu mai taya musu Sannan sukai shiru. Abba ya shirya fagan-fagan yabar gidan zuwa inda zuciyarsa ke raya masa domin yin maganinsu Yaya Muhammad ɗin baki ɗaya.............✍


*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*







*_Typing📲_*



*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

_________________________


*_Chapter Twelve_*

..............Oho su bama su san sunai ba. Dan koda suka fice a gidan babu wanda yay koda ambatar sunansu Abba ne balle su nuna sun damu da al'amarinsu. Asibiti suka nufa kansu tsaye. Inda sukai tozali da sanyin idaniyarsu da ke zaman jiran isowarsu.
        Cike da ɗunbin farin ciki duk suka baibayeta kowa na jera mata tambayoyi game da jikinta da yanda takeji kuma. Komai bata iya ce musuba. Sai murmushi da take musu hannun Hibbah da Ammar a cikin nata tana kallon ciwukan jikin Ammar din. Da sauri ya ce,
        “Karki damu Ummi naji sauƙi. Kema ALLAH ya baki lafiya ki cigaba da mana tuwon dawarnan naki da bama son ci”.
      A tare suka kyaƙyale da dariya, Murmushin Ummi ma ya sake faɗaɗa ta kai hannu ta shafa fuskarsa. Hannun Hibbah ta kamo ta maida saman tata fuskar. “Ummi nice auta ni zaki shafama fuska ba wannan garjejen mutumin ba”.
     Ranƙwashi Ammar ya bata akai. Ta dafe kan da sauri tana sakin karamar ƙara. Ammar ya mike da ga inda yake zaune yana mata gwalo.
       “Yaya Umar ka ganshi ko?”.
Harar Ammar Yaya Umar yayi. “Kai wai miyasa baka rabo da zalunci ne. Ko wannan rankwashin da kake mata ma ya hana girma ai taita zama kamar ƴar cilikowa tana addabar mutane da ɗaukar magana”.
       Dariya duk suka tuntsure da shi baki ɗaya. Ransu fes da farin cikin tashin Umminsu. gashi doctor ma ya sanar musu nan da kwana uku zasu sallameta taje gida ta cigaba da shan magunguna. Dan dama irin aikin nata mai sauƙi ne inhar an dace da yinsa bisa nasara.
         Su suka taimakawa Ummin ta tashi suka jingina mata filo. a tare suka haɗu su duka suka ringa bata abinci duk da Hibbah na isarsu da rigima da rinto. Dan a layi aka dinga bi har Ummi tai musu nuni data ƙoshi. Sai da tasha maganinta sannan sukai mata sallama domin tafiya wajen aiki aka bar mata Hibba da Ammar. Dan su sai ƙura ta lafa zasu koma school musamman ma Hibbah.
       Kafin su wuce sun biya office ɗin doctor daya bukaci ganinsu. Bayan sun sake gaisuwa da shi da nuna jin daɗinsu akan nasarar jikin na Ummi ya shiga musu bayani akan wani bawan ALLAH yazo ya biya kuɗin aikin Ummi ɗin duka. Dan haka zai dawo musu da nasu kuɗaɗen insha ALLAH.
      Cikin mamaki suke tambyarsa wanene hakan?. Ya sanar musu shima dai bai sani ba kai tsaye. Dan ansha irin wannan taimakon batare da sunsan ainahin wanene ba. Amma kuma bayan hakan ma wani ma ya sake bada kaso ɗaya bisa uku na kuɗin aikin harma ya shiga ya duba Ummi. shima kuma dama yakanyi hakan a wasu lokutan. Yasan kuma zasu gansa suma kafin a sallami Ummi ɗin dan ya fahimci a yau kawai kamar har sabo ya shiga tsakaninsa da Ummi ɗin.
      Sosai abubuwan suka basu mamaki, amma sai suka watsar da mamakin sukacema doctor a maida musu kuɗin su da kansu insha ALLAH zasu biya kuɗin aikin mahaifiyar tasu basa buƙatar kowa. Cikin nasiha ya nuna musu hakan ba daidai bane. Sam babu ƙyau maida alkairi baya musamman irin wannan. Suma bawai sun biya bane domin sunga sun gaza.
      Dole suka hakura suka amsa tare da yin addu'a ga masu biyan. Da ga haka suka fito domin nufar wajen aikinsu........

_________________________________

            A ɓangaren yaran master kam, tun suna zuba idon zaman jiran dawowarsa har suka fidda rai. Dan sun fahimci dai yayi nisan kiwo. Badan sun so ba dole suka tashi sukai shirin barci duk suka kwanta kowa ransa da addu'ar ALLAH ya dawo musu da shi lafiya.
      Sukan damu idan yay fitar dare. Saboda sunsan shi sam bayasan yawon dare. Ko su duk aikin da zai sakasu inhar magrib tayi ya haƙura kenan. Sai ko idan ya zama dolen dole. Amma da anyi sallar isha'i basa ƙara fita sai ta lalura.
      Koda suka tashi sallar asuba ma basuji motsinsa ba, haka sukai alwala suka fita, dan sunsan duk inda massallacin da ya tadasu yake zasu ganosa a layin insha ALLAH. Sai ga shi fitowar tasu ma ta sakasu fahimtar a ina suke. Ashe bayan layin gidan da suka baro jiya ne. Har cikin ransu suna jinjinama boss ɗinsu, saboda matuƙar wayonsa da basirar iya takun rayuwa. Komai babu wanda ya faɗa suka adana a zukatansu har sukaje salla suka dawo. Sanin yace ƙarfe bakwai da rabi zasu bar gidan yasa basu kwanta ba suka tattare abinda suka ɓata.
         Suna tsaka da kimtsawar ne kusan 6:43 sai gashi ya dawo. Kallon mamakin ta inda ya shigo suka shiga masa. Dan sudai basuji alamar buɗe ƙofar gidan ba. Hasalima sakata suka saka mata ta ciki, dole ne sai yayi musu knocking sunzo sun buɗe masa.
       Sarai ya fahimci ma'anar kallon da suke masa, amma sai ya basar abinsa. Hakan yasa suka shiga gaishesa da masa barka da dawowa bayan Musbahu ya tashi ya amshi bag ɗin hannunsa.
            Hannu kawai ya ɗaga musu, kafin ya fara magana a taƙaice yana nuna bag ɗin da ya shigo da ita, “Gaba ɗayanku zakuyi amfani da kayan cikinta ne, dan a wannan gaɓar magana ake ta kuɗin baƙine ango ya kawo ku kwana anan”.
         Cikin girmamawa suka shiga amsa masa suna murmushi. Yayinda shi kuma yay shigewarsa ciki. Zaidu ne ya fara kwashewa da dariya yana faɗin, “Abokan ango waye angon to a cikinku?”.
        Salis ya nuna kansa yana wani buɗe hannaye irin eh😉😂. Hararsa Habib yay da taɓe baki. “Banza. Kana ɗan yahoo ubanwa zai baka ƴarsa, wataran shima ka yashe masa asusunsa”.
      Sanin boss na gidan ya sakasu fara dariya suna tarewa da hannu. Salis da ke harar Habib ya ce, “Da yake ma talle bataima audi gori duk tafiyar ɗaya ce. Ta wani fanninma gwara ni. Kuma tunda kace haka kwanan nan zakaji na zama ango ɗan baƙin ciki yahoo boy”.
         Duka Habib ya kaima Salis ɗin ya kauce yana masa gwalo. Rabi'u yace, “Kai kai ku tsaya kuji. Ni fa da boss yay maganar ɗaurin auren nan sai naji inama irin shine za'a ɗaurama auren. ALLAH na ƙagu naga mai tsaurin idon da zatai wuff da master”.
        Dungure masa ƙeya Musbahu yayi da saurin cewa, “Wanan saɓon naka banajin zai tabbata a gidan nan. Inko ya tabbata to lallai sai mun yashe asusun tsohonta tas inaga abiya sadaki da kuɗin auren nata”.
     Duk yanda sukaso matse dariyarsu hakan ta gagara, tuni suka shiga ƙyalƙyalewa harda masu faɗowa ƙasa da ga kujera. Khalid ne ya fara farga da Master da tun dariyarsu ta farko ya fito. Tsaye yake a jikin ƙofar ya harɗe ƙafafu da hannayensa a ƙirji kawai ya zuba musu idanu. Da sauri Khalid ya zunguri Rabi'u da ke kusa da shi, babu shiri shima ya gimtse tasa dariya yana zungurin Zaid. Shima Zaid da sauri ya haɗiye tasa yana mintsinin kafar Idris da ke kusa da shi. Musbahu da shima idonsa ya kai yay azamar haɗiye tasa yana rarrafawa zai ɓoye bayan kujera. Habib da Salis da basusan anayi ba kam sai ƙara tuntsurawa suke. Salis yace, “Ni why bana tunanin boss zai wani iya soyayya, dan ita tayi yamma shi yayi gabas. Inagama sai munyi karo-karo wajen badashi sadak......”
     Da sauri Musbahu ya rufe masa baki. Hannu Salis ya shiga bige masa yana ƙoƙarin yin magana idonsa ya sauka akan Master da har yanzun yake tsaye yana jinsu. Dan ya wani lumshe idanu tamkar wani mai yin barci a wajen.
     Babu shiri Salis ya ture Musbahu gefe ya miƙe da gudu ya afka bedroom. Ganin haka suma duk sai suka shiga rufa masa baya. Wani silent numfashi master yaja yana buɗe idanunsa akan ƙofar ɗakin da suka shigan harda rufo ƙofa. Uffan bai ceba ya juya ya koma cikin ɗakinsa.

         Koda suka kammala shirin cikin ɗanyun shaddoji iri ɗaya kalar sararin samaniya suka fito, kasa haɗa ido da shi sukayi. Sai satar kallonsa sukeyi ta ƙasan ido, yayinda dariya ke cin ransu a ƙasan zuciya dan shi tashi shigar ta irin marasa jin direbobin nan ce yayi. Da alama da kansa zai tukasu a mota kenan tsabar iya taku. Gaba yay batare da yayi magana ba duk suka rufa masa baya suna ƙoƙarin gimtse dariyarsu.
         Motar bus da zata iya kwashesu ce a waje a fake master nata faman gogewa kai kace driver ɗinne na gaskiya irin wanda suke zuba iya shege a tafa zuwa agege da maraban jos. Dan facemark ɗin dake fuskarsa bata da maraba da ta direbobin da ke tsaka da cin duniya da allura.
          Da kansa ya buɗe musu motar yana harararsu dan ganin kallon da suke masa a munafunce suna murmushi. Sai da suka gama shiga ya rufe yana zagayawa mazaunin driver bayan ya dagama matasan dake zaune a wajen mai shayi anata fira akan abinda ya faru jiya na mayar gwamna hannu. Sai zabga gaddama suke kowa na kare abin son sa. Wasu Master, wasu jami'an tsaro, wasu matar gwamna ɗin. Yayinda wasu ke faman zuba ashariya kai kace faɗa ne ya tashi.
       Murmushi ya saki yana shigewa a motar saboda jin furicin wani da ke faɗin, “Suma jami'an tsaron lusarai ne da zasu zauna mutum ɗaya ya gagaresu. Kawai dai sunyi niyyar barin shegenne kafin suyi ma rayuwarsa walmakalifatu”
     “To ka sani ko aljanine?”.
Wani ya bashi amsa dai-dai master na reverse da motar. Hannu suka ɗago musu wasu na faɗin ALLAH ya sanya alkairi. Dan sun yarda su ɗaurin auren za'aje😂😝.

            Lallai maganar yaran master gaskiya ne. Wannan gida yaji kayan ƙawa da more rayuwa. Shi kansa yana matuƙar son gidan. Dan a cikinsa ne kawai yafi sakewa sosai. Sanann anan ne kawai yake zama da yaransa. Amma duk sauran gidajen ba kullum yake kwana tare da su ba sai yaso.

*_BAYAN KWANAKI UKU_*

           Alhamdulillahi jikin Ummi yayi ƙyau sosai, dan tattali iya tattali take samu da ga iyalanta sanyin idaniyarta. Yayinda wasu a cikin ƴan uwa ke tururwar zuwa dubata da jiki.
      Hibba ce take kwana tare da ita, su kuma su yaya Muhammad da sun taso aiki anan suke tarewa har sai 11 suke wucewa gida. Har zuwa yanzun Abba bai dawo ba da ga tafiyar da yay randa akaima Ummi ai. Itama hajiya mama taɗan lafa da fitinarta saboda ƙafarta data motsa, duk da dai su su yaya Abubakar ɗin sunsan wani abun suke ƙullawa basu nuna sun damu ba.
Junaid ma ya dawo gida bayan kwana biyu da yayi a asibiti. Sai dai kuma tunda ya dawo ɗin ko ƙeyarsa basu gani ba, sai sauran ƴammatan gidan marasa kunya. Su kuma ko kallo basu ishesu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login