Showing 24001 words to 27000 words out of 155081 words
ma yanzu ne wasan zai fara😂👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Chapter Eleven_*
..........Cikin gaggawa aka amshi Ummi a asibiti. Dan da ƙyar take fitar da numfashi, ga jinin da yake fita mata ta hanci da tayo tari da ya harmutsa dukkan zukatan su Yaya Muhammad. Hibbah kam ai tama koma musu tamkar zararriya. Dan koda za'a shige da Ummi sai da Yaya Umar ya riƙota shima hawaye masu ɗaci na cika masa idanu.
Yaya Muhammad kam da baida wahalar zubda hawaye gefe kawai ya maida kansa yana sharewa. Umminsu itace duniyarsu. Itace farin cikinsu. Itace ta maye musu dukkan gurbi na dangin mahaifinsu da giɓin mahaifin nasu da suka rasa tsahon shekaru goma sha tara. Tayi haƙuri da damuwoyi kala-kala domin taga sunyi farin ciki. A kullum ƙoƙarin ta su zama mutanen kirki. Su zama masu haƙuri, su zama masu juriya. Su zama.... Su zama... Da yawa. To sukam idan akace sun rasata ina zasu saka kansu da rayuwarsu. Idan suna a gabanta sam basa tuna sun girma. Ganin kansu suke tamkar ƴan shekaru goma-goma. Bazasu so Ummi ta tafi ta barsu batare da sun cika mata burinta na ganin sunyi aure ba. Kamar yanda take addu'ar ganin zuri'arsu suma hakan shine fatansu a yanzun. Suna son yawan ganin dariya a saman fuskarta kamar yanda mahaifinsu yay sanda yana raye. Amma hakan duk bazata tabbataba sai tana a kusa da su........
“Ya ALLAH ka bama Ummi lafiya ka tashi kafaɗunta. ALLAH yasa ni na mutu a madadinta”.
Furucin Muhibbat da ke kuka ya katsema Yaya Muhammad da su Yaya Abubakar tunaninsu. Gaba ɗayansu suka zuba mata idanu na ɗunbin tausayinta da ƙaunarta. Yarinya ce ita mai yawan walwala, kazarkazar, wauta, tsiwa, rawan kai, surutu duk a dalilin gata da kulawar da take samu da ga garesu. Tana matuƙar son Ummi, suma haka. Batasan mahaifinsu ba, shiyyasa suketa ƙoƙarin ganin sun cike mata gurbinsa.
A hankali Yaya Abubakar ya taka inda take durƙushe gaban Yaya Umar da rauni ya cika zuciyarsa na tausayin kansu da autar ta su. Hannu biyu yasa ya kamota ya ɗaga tsaye. “Haba Muhibbat, maimakon kima Ummi addu'ar samun lafiya sai ki dinga ma kanki addu'ar mutuwa a madadinta?. Insha ALLAH Umminmu zata tashi da lafiyarta kinji. Ki mata addu'a da fatan alkairi, ALLAH ya na tare da ita kinji”.
Kanta ta jinjina masa wasu zafafan hawayen na rige-rigen sakko mata. Yasa hannu ya share mata yana murmushin ƙarfin hali.
“Ƙyaƙyƙyawa mai kama da Umminta a komai, sai dai raguwa ce bata kai Ummi jarumta ba”.
Yaya Abubakar ya faɗa cikin ƙarfin hali yana ɗan ja mata kumatu. Maimakon tai dariya da tsalle kamar yanda ta saba idan ya faɗa mata hakan, sai ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka. Kusan atare duk suka rumtse idanunsu, dan kukanta na matuƙar sake tada musu hankali.
Kusan mintoci arba'in da biyu likitoci suka ɗauka tare da Ummi. Kafin ALLAH ya basu ikon fitowa. A kusan tare su Yaya Umar suka miƙe a zabure harda Hibbah dake jingine jikin Yaya Umar barcin wahala ya ɗauketa.
Kusan a tare suka furta “Doctor ya jikin Ummin mu?”.
Kallonsu yayi cikin furzar da numfashi yana cire norsemask ɗin fuskarsa. “Inason yin magana da ku a office”. Ya faɗa yana ƙoƙarin wucesu. A take suka rufa masa baya har Muhhibat da Yaya Umar ke riƙe da hannunta. Kusan tare suka shiga da doctor cikin office ɗin. Hakan da sukai sai tausayinsu ya sake kamashi. Dan a kallo ɗaya zakai musu ka hango ɗunbin so da ƙaunar da sukema mahaifiyar tasu. Bai wani tsaya ja musu rai ba yay musu bayani akan matsalar da ke tare da Ummi a ƙasan zuciya da hanjinta. Bincikensu ya nuna kuma ta jima da ciwon yana ta cinta a hankali, sai dai yafi nuna kansane a duk lokacin da wani ɓacin rai ko tashin hankali ya sameta. Amma zasu mata aiki insha ALLAH suna mata fatan samun lafiya.
Duk da maganarsa ta ƙarshe taɗan sakasu jin sanyi hakan bai hana zukatansu shiga cikin matuƙar rauni ba. Ya ɗan ƙara faɗaɗa musu bayanai akan abinda za'a iya buƙata akan aikin da magungunanta. Tare da basu tabbacin inhar sun shirya a yau ɗin nan ma za'a iya mata aikin. A take sukace sun amince, duk da kuwa kuɗaɗen da ya ambata da wuya a iya samunsu kai tsaye da ga garesu. Badan suna da yawa bane sosai, kawai dai suɗin masu tasowa ne ba wasu ɗumbin kuɗaɗe suka tara ba. Amma dai tunda ya ce zasu iya bada rabi idan an kammala aikin su cika zasuyi ƙoƙarin su insha ALLAH.
Take ya basu takarda Yaya Muhammad ya saka hannu. Daga haka suka fito domin tattaunawa akan zancen kuɗin. Dan doctor yace sai sun tura zaiyi ƙoƙarin haɗa wasu da ga kayan aikin insha ALLAH.
Su dukansu suna aiki, Ammar ne kawai da Hibbah ƴan makaranta a cikinsu. Sai Yaya Umar da ke ɗan harkar kasuwanci saboda matsalar rashin samun aiki da matasa ke fama da shi a ƙasar nan. Sai ma yazam a yanzu yafi nutsuwa da kasuwancin sama da aikin da yay karatu akansa. Dama kuma su Yaya Muhammad ɗin nata son ganin sun ƙara masa ƙarfin jari tunda ALLAH yayma kasuwar tasa nasibi.
Sun ɗan tattauna wajen ganin sun haɗa kuɗaɗen, cikin amincin ALLAH ma sai gashi an samu kusan rabin a hannunsu su uku. Idan Yaya Usman yazo shima zasuji mi za'a samu daga garesa. Abba dai basa saka rai game da shi sam.
Basuyi zaman ɓata lokaci ba wajen fita su tattaro kuɗaɗaɗen har Yaya Usman da ya iso asibitin a yanzu shima, dan ya kasa jure zama acan saboda ya gwada ƙoƙarinsa na ganin an bashi Ammar amma hakan ya gagara saboda mugun ƙulli da Abba yaje yayi a station ɗin. Ya tahone kawai dan yasan insha ALLAH Yaya Abubakar zai fiddosa da zaran hankali ya kwanta. Kafin su dawo kuwa an gama shirya komai na shiga theater ɗin. Cikin amincin ALLAH zuwa ƙarfe takwas na dare aka shiga da Ummi. Sun bita da ƙyaƙyƙyawar addu'a da fatan dacewa a zahiri da baɗini.
Yaya Muhammad ne ya fara fahimtar akwai yunwa tattare da Hibbah. Dan gaba ɗaya jikinta ya saki tamkar mara laka. Yana lura da ita ko salla a zaune ta dinga yinta. Hannu yasa ya kamo nata cike da kulawa yana faɗin, “Auta yaushe rabonki da abinci”.
“Tun breakfast ɗin safe Yayanmu, amma kuma banajin yunwa”. Ta faɗa cikin sanyin da basu santa da shi ba.
Su dukansu sai da suka dubeta cike da tausayi. Yaya Usman yay saurin barin wajen batare da yayi magana ba. Cikin lokaci ƙanƙani sai gashi ya dawo da teakaway.
Zama yay da kansa zai bata amma sai tace ta ƙoshi. Dukansu babu wanda bai lallasheta ba amma tace ta ƙoshi. Sai da taga duk sun ɓata rai sanann ta amsa ta ci wanda ya saka mata a baki. Amsar cokali tayi ta ɗiba da kanta shima ta bashi. Ta sake ɗebowa ta bama Yaya Umar. Shima Yaya Abubakar haka. Sannan ta bama Yaya Muhammad shima. Dukansu murmushi suke mata a karon farko tun bayan shigowarsu asibitin da duk rayukansu suke a jagule. Amsa Yaya Usman ɗin yay ya cigaba da bata. Kusan lauma uku ta kauda kanta idanunta na cikowa da ƙwalla.
“Miya faru kuma?”. Yaya Abubakar dake miƙa mata ruwa ya faɗa. Hawayen data matso suka silalo saman kumatunta. Muryarta na rawa tace, “Yayanmu Yaya Ammar fa?”.
Shiru suka ɗanyi duk suna kallonta. Kafin Yaya Abubakar ya shafa kanta fuskarsa ɗauke da murmushin ƙarfin hali. “Karki damu shima zai dawo, insha ALLAH bazai kwana acan ba. Ƙarasa cin abincinki ina zuwa”. Ya ƙare maganar yana mikewa. Tashi Yaya Usman yay yabi bayansa.
Police station ɗin da aka kai Ammar suka nufa. Tun shigowar su Yaya Abubakar wasu a cikin ƴan sanda suka shaidashi saboda aiki ya taɓa haɗashi da wasu a cikinsu. Amma duk da haka sai ya nuna musu i'd card ɗinsa. A zabure sauran ma suka shiga gaishesa. Aka kuma masa iso ofishin ogan wajan.
Tun a shigowarsu ya shaida Yaya Abubakar ɗin. Amma sai ya maze abinsa. Yaya Abubakar ya cije lip ɗinsa dan akwai ƴar tsama a tsakani. Sai dai yana sama da shi. Cikin nuna bai damu da basarwar tasa ba yay masa bayanin kansa. Tare da buƙatar a bashi Ammar.
Cikin yatsine fuska ɗan sandan yace, “To yallaɓai idan ku matsayinku na manya kuna haka su kuma wanda basu da dangi ƴan sanda kuma fa? Laifi ƙaninka yay aka kawosa nan, sai kuyi haƙuri mu gama tattara bayanai akansa mukai maganar kotu kamar zaifi”.
Sosai Yaya Abubakar ya kafesa da ido. Sai kuma ya saki wani lalataccen murmushi yana miƙewa dan yasan wannan tsarin da ga Abba yake. “Wanann basirar ba taka bace. Amma ga saƙo ka bama wanda ya tsara maka ya kuma biyaka. Ya kiyayi ranar maida murtani dan zata kasance mai ɗaci da tsauri. Ya kuma bar raina allura dan itama ƙarfe ce. Duk randa zuri'ar Aliyu Hamza gwarzo sukaji a ransu zasu maida murtani TAKUN SAAƘAR bazai masa ƙyau ba. Wannan hanunka mai sanda ne”. Yaya Abubakar ya ƙare maganar cike da gargaɗi.
Murmushi Yaya Usman yayi. Dan bai taɓa zato da tunanin yaya Abubakar ɗin nasu ya iya zaro zance haka na. Koda suka fito da kansa yasa a kaisa cell ɗin da Ammar yake. Shine ya amshi key tun daga kanta ya buɗesa da kansa.
Wani irin kallo ya tsaya yanama Ammar da yaci uban duka. Da alama ma ba'a jima da dukan nasa ba, dan duk sabbin raunuka ne a jikinsa dake fidda jini. Komai baiceba a lokacin sai kama hannun Ammar ɗin daya taso da sauri yana tambayarsa “Ina Ummi take?” yayi. Bai amsa masa tambayarsa ba sai da suka iso kantar. Ya duba ƴan sandan wajen da sukai tsuru-tsuru cikin kaushin murya yace, “Su waye sukai wannan aikin?”.
Kallon kallo aka shigayi. A matuƙar tsawace yace, “Ba magana nake ba ne?!!”.
Zabura duk sukayi har tsirarun mutane da sukazo belin ƴan uwansu da masu kawo abinci. Cikin rawar murya wani ɗan sanda yace, “Yallabai wlhy ba laifinmu bane sakamu akayi”. Ya ƙare maganar a hankali cike da raɗa saboda fitowar ogansu da ga office dan jin tsawar da Yaya Abubakar yayi.
Takarda Yaya Abubakar ya fisga ya jefama ɗan sandan da yay maganar. “Ina son duka sunayen members na ƴan sandan dake a station ɗin nan. Wanda sukai wannan dukan kuma sunayensu su kasance a ware”.
Wani busashshen yawu ya haɗiye da ƙyar yana ɗaukar takardar. Jikinsa sai tsuma yake ya shiga zano sunayensu ɗaya bayan ɗaya. Bayan ya kammala cikin girmamawa ya mikama Yaya Abubakar ɗin. Uffan baice masaba ya amsa tare da jan hannun Ammar da Yaya Usman ya riƙe ta ɗayan gefen suka fice da ga station ɗin.
Ko a mota ma babu wanda yay magana dan zuciyar Yaya Abubakar takai ƙololuwar ɓaci game da lamarin Abba. Asibitin suka wuce da Ammar shima. Ba ƙaramin tashi hankalin su Yaya Muhammad yay ba ganin dukan da akaima Ammar. Hibbah kuwa kuka ta fashe musu da shi tare da zuwa ta rungume Ammar ɗin.
“Wash ALLAH auta zafi”.
Ya faɗa cike da shagwaɓa saboda jin ta ƙankame masa hannunsa da yake da tabbacin ƴan sandan sun ji masa ciwo. Saurin sakin hanun nasa tai tana sake fashewa da kuka. Ya kai hannu bisa kanta ya dafa yana murmushin ƙarfin hali. “K karki maidani kamar ba namijiba mana. Bakisan dukan ƙarfi ya ƙara min ba ma”.
A yanda yay maganar ya saka su Yaya Umar yin murmushi suna girgiza kansu. Hibbah kuwa kukan ne ya sake kufce mata.
Yaya Umar ne ya kaisa akai treatment ɗinsa da bashi magunguna. Sauran abincin da Hibbah taki ci suka matsa masa yaci da ƙyar shima. Dan sai da Hibbah ta dinga basa a baki yau babu faɗa. Bayan ya kammala yasha magungunan da aka bashi. Duk yanda sukaso yaje gida ya huta yaƙi, yace shima sai yaga fitowar Ummi.
Sha'awa yanda suke ƙaunar junansu ya bama doctor Bilal. dan haka ya bama Ammar ɗin shawarar yazo office ɗinsa ya kwanta to har komai ya kammala sai a tashe sa. Nanma da ƙyar ya amince bisa umarnin yaya Muhammad. Haka dai ya miƙe yana tura baki Hibbah na masa gwalo.
_____________★★★_____________
Duk yanda yaso yin shirin barci ya kwanta hakan ya gagara. Sai fama kai kawo yake a cikin ɗakin, abubuwa da yawa zuciyarsa ke raya masa game da matakin da ya kamata ya ɗauka a kanta. Inhar zata iya kai masa hari ta samesa a ƙanƙanin lokaci. To wane irin shiri kenan zatai a gaba dominsa? Lallai dole ne yasan ita ɗin wacece? Mi kuma ta taka ne haka?. Shin sakata akai? Kokuwa yin kanta ne?.
Waɗanan jerin tambayoyi suketa faman masa kai kawo a zuciya da hanashi nutsuwa. Shiri ya canja saɓanin pyjamas da ya kamata ya saka sai yasa wasu kayan daban.
Yaransa na falon zaune har yanzu suna sha'aninsu sai ganinsa sukai ya fito. Mamakine ya kamasu dan duk zatonsu ya kwanta.
“Boss da matsala ne?”.
Salisu ya faɗa cike da girmamawa.
Kansa ya girgiza masa yana ƙoƙarin ɗaura agogonsa. Sai da yaje gab da fita a falon yace, “Zanje wani waje ne, wani yazo ya rufe gidan”.
Saurin miƙewa Khalid yayi duk da tambayoyine fal bakunansu amma babu damar yi, dan ya nuna baya buƙatarsu. Su ko saboda trianing da suka samu da ga garesa da kowanne irin yare yay magana ko yay nuni suna fahimtar kayansu.
Koda ya wuce Khalid ya dawo zaman tattaunawa sukai, amma sai basu gano komaiba, dan haka sukai jigum-jigum......
________________________________
Alhmdllhi ƙarfe goma aka fiddo Ummi da ga ɗakin theatre cike da nasara. Bayyana muku irin farin cikin da su Yaya Muhammad suke ciki ɓata lokaci ne. Basu sami damar ganinta ba dan an miƙata ɗakin hutu ne. Sai dai bayanin da Dr Sageer yay musu na narar aikin ya saka zukatansu nutsuwa. Har suka amince da shawararsa ta tafiya gida dan ba'a bukatar kowa tare da Ummin sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu.
Basuyi wani zaman ɓata lokaci ba suka tattara suka wuce bayan an tado Ammar da zazzaɓi mai zafi yayma ligif saboda dukan da yaci. Sosai tausayinsa ya bayyana bisa fiskokinsu. Sai dai komai basuce ba bayan Hibbah da ke ta jera masa sannu kamar zatai kuka. Kaɗan-kaɗan ta ɗaura hannunta a goshinsa.
Suna gab da zuwa gida ya bige hannunta data ɗora masa a karo na babu adadi. “K dalla kin isheni, ga hannunki da sanyi”.
Baki Hibbah ta tura gaba. Cike da tsiwa ta murguɗa masa baki da faɗin, “Oh dama ka samu na damu da kai zaka min wani iyayi”.
“To waya aikeki? Uwar iya mai cinikin iya”. Ya faɗa yana gyara kwanciyarsa jikin kujera.
Murmushi Yaya Usman da ke kusa da su yayi yana girgiza kansa kawai. Dan inda sabo sun saba gani. Anjima kaɗan kuma kaga sun koma hirar arziƙi. Kafin awa ɗaya ta rufa sunyi faɗa sau biyu.
Cikin jin haushi Hibbah tace, “Idanma kaga na sake kulaka dan ALLAH ka tsine min Yaya Ammar”.
Baki Ammar ya taɓe da faɗin “ALLAH na gode maka na jefar da ƙwallon mangwaro na huta da ƙuda”.
“Yaya Usman ka ganshi ko?”. Ta faɗa kamar zatai kuka.
“Ya isa manta da lamarinsa auta. Ko sannu karki sake masa har ya warke”.
“Ai baran masa ba ko Yayanmu”. Tai maganar da dungurin wajen ciwon da ke a hannunsa. Ƙaramar ƙara ya saki yana bige mata hannu dan yaji zafi. Ta ƙyalƙyale da dariyar mugunta. Ranƙwashi mai shegen zafi ya bata wanda ya saka bakinta rufewa ruf, sai kuma ta fashe da kuka.
Yaya Abubakar da duk yake jinsu da ga gaba ko kallo basu ishesa ba. Sai ma waya da ya ɗauka yay kiran maigadi ya buɗe musu gate. Koda suka shiga cikin gidan tsitt yake alamar jama'ar cikinsa harsun ƙwanta. Kusa da inda Yaya Muhammad yay parking shima yayi gab da sashensu.
Hibbah da ke kukan ranƙwashin da Ammar yay mata ta fara fita domin kaima Yaya Muhammad ƙara tunda