Showing 63001 words to 66000 words out of 155081 words
akan sam bata yarda ba wanann shirin Ummi ne da ƴaƴanta. Tabbas sune suka saka Shuraim ɗin yayi haka. Da yawan mutane maganar Hajiya maman tayi tasiri a garesu, musamman da ya kasance alaƙar Hibbah da Shuraim ɗin kawai kowa ke kallo a zahiri da kuma ɗaura auren su Yaya Muhammad da wasu matan daban alhalin su su Hajiya mama basu san da zancen ba sai yanzu da aka ɗaura.
Gidan ya ruɗe sai cece kuce ke tashi ta ko ina. Kowa na faɗin albarkacin bakinsa da hasashen zuciyarsa.
Cikin ƙarfin hali Ummi da tun fara tujarar Hajiya Mama yaranta suka kamata suka shige ciki da ita ganin yanda duk suka tattara kansu gareta ta haɗiye tashin hankalinta da ruɗani tana mai duban su Yaya Usman ɗin da su kansu bawai suna cikin cikakken hankalinsu bane akan al'amarin. Kan Yaya Abubakar da ke kusa da ita ta dafa tana murmushi. “Har yanzu zuciyata ta kasa daina yimasa ƙyaƙyƙyawan zato. Dukkanin cikamakin kamala da mutunci a bayyane suke garesa, shiyyasa nai saurin aminta da aura masa Tanee. Amma ta yaya fari zai koma baƙi a wanan ranar?, bayan har yanzu idanuna da zuciyata sun ƙi kallon komai da baƙin”.
Cikin taraddadi da jan gwauron numfashi Yaya Abubakar yace, “Dama nasan hatsabibin nan bazai ƙyale Hibbah ba. Dan ta masa tabo irin wanda bazai gogu a cikin tarihinsa ba. Hakan yasani yarda da amincewar aima ta aure ko zata kuɓuta daga garesa. Ashe mun riga mun daɗe da kasancewa cikin lissafinsa, ko tantama banayi akan lallai shu'umin nan Master ne yazo mana da fuskar Shuraim. Sai dai ina mamaki matuƙa ta yanda ya kuɓutar da mu daga auren waɗan nan yaran. Mi hakan ke nufi ne?”.
Ammar ya ɗago kansa da ga ɗorawar da yay bisa cinyar Ummi a firgice yana faɗin, “Yayamu Master fa kace? Gawurtaccen ɓarawon da kuke nema ruwa a jallo ko wa? Danni ban gane ba”.
Numfashi yaya Abubakar ya fusga da ƙarfi yana jinjinama Ammar kai alamar tabbatarwa. Tare da bin fuskokin sauran ƴan uwansa da suma ruɗanin ne ƙarara ya bayyana akan fuskokinsu har suka gaza motsawa.
Cikin ɗan rawar jiki Ummi tace, “Abubakar mi kake faɗane haka? Kana nufin yaron kwanaki da ƴan sanda suka sakata tai aiki akansa?”.
Yaya Abubakar da shi kaɗai yasan lissafin da zuciyarsa keyi ya ɗan firzar da numfashi yana ciza lip ɗinsa na ƙasa da duban Ummin tasu cike da kulawa. “Ummi ki kwantar da hankalinki. Babu abinda zai samu Muhibbat da izinin ALLAH.....”
Da sauri Ammar ya amshe zancen da faɗin, “Ummi mugodema ALLAH ma da kafin a kaita gidansa ne komai ya fito. Yanzu kunga ko a kotu ne a raba auren kawai sai a bama Yaya Isma'il dama sunfi dacewa”.
Sosai maganar Ammar ɗin tai tasiri a garesu har Yaya Muhammad ya shafa kansa yana ɗan murmushi.
Yaya Abubakar kam ɗago kai yayi ya kallesa tamkar wanda zancen yayma allura. cikin nazarin furucin na ammar, ya ɗan kaɗa kai yana jujjuyawa, dan baya son faɗar abinda a yanzu zuciyarsa ke hasko masa kai tsaye saboda Ummi. Miƙewa yay yana faɗin, “Komai ma da baƙwa tunani zai iya yi. Sai dai inaji a jikina Muhibbat ce tarkonsa a wannan karon”.
“Yaya Abubakar kana nufin zai cigaba da bibiyar auta?”. Cewar Usman a tsorace yayinda duk suka bisa da kallo har Ummi.
Numfashi Yaya Abubakar ya fesar yana gyaɗa kai dai-dai yana ƙoƙarin kaiwa ƙofar fita. “Bazaka gane lissafinba Umar. Ku dai da ga yanzu dukkanin idanunku su kasance akan Muhibbat ne. Dan duk yanda kuke tunanin wanann shu'umin mutumin yafi ga haka. tabbas bazai taɓa bayyana kansaba bayan bai gama tsara yanda komai zai tafi masa ba.”
Da kallo kawai suka bisa harya fice yana ƙoƙarin kai waya bisa kunnensa. Da alama kira yayi. Kafin Ammar ya miƙe yana faɗin “bara na nemota itama.”
Kai kawai suka iya jinjina masa, dan jikin kowa ya gama sanyi a cikinsu.
★★★★
A ɓangaren su Musbahu kam koda suka iso L.E street. Habib ne ya shiga sanarma ogan nasu isowar tasu, duk da kuwa sarai yasan yaji.
Zaune ya sameshi ƙafa ɗaya kan ɗaya a katafaren falon nasu da yaji kayan more rayuwa yana sarrafa system da ke saman cinyarsa. Duk da yaji shigowar Habib ɗin bai ɗago da ga abinda yake ba, sai dai ya amsa masa sallamar akan laɓɓa.
Habib da ya ɗan kallesa ya risinar da kansa ƙasa da girmamawa yace, “Barka da hutawa Master”.
Uffan baice ba, bai kuma ɗago ya kalli Habib ɗin ba har tsahon wasu sakanni, sai dai ya jinjina kansa alamar amsawa.
Habib da ya fahimci ƴan mulkinne a kusa yau sai kawai ya cigaba da magana. “Aiki ya kammala, itama gata tare da mu”.
Dakatawa yay da ga sarrafa lap-top ɗin, a hankali ya ɗago idanunsa cike da ƙasaitarsa ya saukesu kan Habib ɗin da ya nutsu waje guda saboda tsabar girmamawar da suke bashi.
Kallo daya yay masa ya janye idanunsa ya maida akan system ɗin da faɗin, “Su Salis?”. Yay maganar a taƙaice cikin sigar tambaya”.
“Dukanmu tare muka shigo”. Habib ya bashi amsa.
Lap-top ɗin ya ajiye ya miƙe, batare da ya sake cema Habib ɗin komai ba ya nufi hanyar fita cikin takun da ke nuna cikakkiyar lafiyarsa da nutsuwar da ALLAH ya azurtashi da ita.
Shima Habib bayansa yabi da saurai suka fita a kusan tare. Kallo ɗaya yay ma su Salis da ke ƙoƙarin fitowa a mota ya ɗauke kansa da cigaba da tafiya cikin izza da ƙasaitarsa tamkar wani jinin mulki.
Dai-dai yana isowa inda suke suka haɗa baki wajen faɗin, “Barka da gida Master”.
Hannu kawai ya ɗaga musu yana nufar motar da Habib ya fita da ita. Da sauri Habib ya buɗe masa motar ta sashin da Hibbah ta ke yana matsawa gefe tamkar yanda sauran suka nutsu.
Duk da yasan a sume take hakan bai hanashi sake ɗaure fuska ba kafin ya sauke nutsatstsun idanunsa masu kaifin gani a kanta. Sai kuma ya ɗan kaudasu tare da ƙarasa takawa gaban motar da ƙyau yana yamutse fuska. Dai-dai lokacin da yake ranƙwafawa su Habib suka kalli juna, yana ɗagowa ɗauke da Hibbah suka waro idanu waje da saurin maida kawunansu ƙasa.
Ko kallo basu ishesa ba, sai ma sake tamke fuskar boginsa da yayi ya shiga taku cike da izzarsa da kasaita zuwa cikin gidan ɗauke da Hibbah da batasan wainar da ake toyawa ba.
Idris ya haɗe yatsunsa waje guda alamar love yana wani cije baki. Sauranma idanu suka shiga kashewa da yin alamar nice👌🏼 cike da shaƙiyanci.
Tsaf yaga duk iya shegen nasu ta glasess ɗin windows. Ya ɗan ciji lip ɗinsa na ƙasa da tura ƙofar falon da ƙafa. Hakan ya saka su Khalid saurin mara masa baya gudun yin laifi.
Koda ya shigo falon up stairs ya nufa, anan ma falo ne babba masha ALLAH, wanda babu abinda baijiba na kayan more rayuwa. Sai tashin ƙamshi yake ga sanyin ac mai saka nutsuwa. Kai tsaye ya nufi ɗaya da ga cikin bedroom ɗin da ke a up stairs ɗin. ya shimfiɗeta saman gadon ɗakin yana wani sake ɗaure fuska da yamutseta irin shifa ya gajin nan. Ya ɗan zubamata harara yana janye jikinsa. Wayarsace ta fara tsuwwa alamar shigowar kira.
Sharewa yay tamkar bazai amsa ba. Sai da ta na gab da tsinkewa ya zarota a aljihun wandon baƙin jeans ɗin jikinsa yana jan siririn tsaki da jingina jikin mirror ɗin ɗakin yana kaiwa kunnensa batare da ya ce uffan ba, sai dai shirun nasa na nuna alamun sauraren mai magana ya ke da ga can. Tsawon minti biyu da wasu sakanni ya ce, “Uhmm” da ɗan gyaɗa kai.
Dai-dai nan akai Knocking ƙofar a hankali, kasancewar sun san idan yana a irin wanann yanayin duk wata hayaniya baya buƙatarta.
Cikin ƙosawa da motse-motsen kuwa ya bada izinin shigowa yana janye wayar a kunnensa...........✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
________________________
*_Chapter Twenty two_*
..........Da sallama Habib ya shigo tare da ƙarasa shigowa cikin ɗakin, leda ɗin da ke a hannunsa ya ajiye saman mirror ɗin da yake jingine.
“Minene wannan ɗin?”.
Ya faɗa yana zuba lumsassun idanunsa bisa kan Habib ɗin.
A ladabce Habib ya ce, “Makarin abinda aka shaƙa matane”.
Kallo ɗaya yayma ledar ya ɗauke kansa. Cikin halin ko in kula ya miƙa masa hannu alamar ya bashi. Ɗakko ledar yay ya miƙa masa, ya ɗan janye hannunsa yana girgiza kansa, Habib da ya fahimci mi yake nufi sai ya buɗe ledar ya ciro handkerchief ɗin da ke ciki ya sake miƙa masa. Amsa yay ya zubama handky ɗin ido tamkar mai nazari, kafin yaja numfashi ya fesar yana ɗago agogon da ke a tsintacciyar hannunsa ya kalla. Ganin lokacin sallar la'asar ya gabato sosai ne ya sashi miƙama Habib Handkerchief ɗin. Batare da yayi magana ba ya nufi hanyar fita ɗakin.
Sukan fahimci abubuwa masu yawa da ga garesa koda ta kurma yay musu. Hakan yasa yanzun ma Habib ɗin ya fahimta. Handky ɗin shima ya maida a ledar ya ajiye saman mirror ɗin ya bi bayansa.
Koda ya fito bedroom ɗinsa da ke a saman upstairs ɗin ya nufa, sai dai yana da ga can kusan ƙarshen bangon gabas da falon saman, hakan yasa akwai tazara tsakanin shi da inda ya kai Hibba. Tamkar falukan nan ma komai tsaf, bakajin komai sai tashin ƙamshi da sanyin ac da ya gauraye ko ina. Yanda yake kure sanyin zai tabbatar maka shi ɗin ma'abocin son sanyi ne matuƙa. Dan yanda gaba ɗaya saman upstairs ɗin da ke nuna alamar anan komansa yake ya ɗauki sanyin wani bazai iya jimirin zama cikinsa ba. Shiko ko a jikinsa bai damu ba. Agogon hannunsa ya cire ya ajiye saman mirror ɗin ɗakin, tare da tattare dogon hannun rigar jikinsa sannan ya nufi wani ɗan dogon glass daya ci kusan rabin bangon yana facing ɗin gadon sa. Wani abu ya danna ya zuge kansa, yana shiga kuma ya maida ya rufe.
Baifi mintuna sha biyar ba sai gashi ya fito cikin sabuwar shiga na wandon jeans da t-shirt. Hakama fuskarsa ta canja zuwa wani daban, gaba ɗaya ƙamshinsa ya gauraye ko ina ya danne na fresheners ɗin da ke tashi a sashen.
Cikin yanayin kamar fushi-fushi da yake cikine ya ƙarama tafiyar tasa bayyana cikin izzarsa da ƙasaita ta musamman. Ya shiga sauka a steps ɗin cikin salon zafin nama da ALLAH ya azurtashi da shi.
Daga falon ƙasan yake jiyo hayaniyar su Salis da alamu ya nuna suma shirin massallacin duk sukeyi. Batare da ya ko kalli sashen da suke ba ya zauna a kujerar da ke gab da ƙafar benen idonsa akan wayar sa dake hannunsa.. Saman kunne ya kai wayar tare da ɗaura ƙafarsa ɗa ya kan ɗaya. Ana ɗagawa da ga can cikin bada umarni yace, “Ka sameni kai da baba Saude”. Da ga haka ya ajiye wayar a table ɗin kusa da hannun kujerar ya maida idanunsa ya lumshe.
Mintuna biyu kacal tsakani Khalid ya fito da ga wata ƙofa bakinsa ɗauke da sallama.
A saman laɓɓa ya amsa masa batare da ya buɗe idanun nasa ba. Sai da baba Saude tai sallama a ƙarshe sannan ya buɗesu a hankali.
“Babana an shigo ashe? Sannunku da dawowa”. Dattijuwar tsohuwa mai cikar kamala ta faɗa tana ƙoƙarin kaiwa zaune ƙasan tattausan carpet ɗin dake a tsakkiyar kujerun.
Kujera ya nuna mata yana girgiza kansa cike da bata girma. Kafin ya buɗe baki tamkar bayaso ya fara magana. “Tun ɗazun na shigo ai. Na zata kina barci ne baba”.
Murmushi tayi dai-dai tana kaiwa zaune. Ta ce, “Eh barci ya ɗan figeni kam sanda suka shigo. Nima motsinsu ne ya tadani”.
Kansa kawai ya ɗan jinjina mata, tare da duban baƙin agogon fatar da ke ɗaure a tsintsiyar hannunsa. Cikin rashin son hayaniyarsa ya maida kallonsa ga Khalid da ke tsaye har yanzun. “Tsayuwar zaka cigaba da min a kai. Ko kiransu ku wuce masallaci!”.
“Ayi haƙuri boss”. Khalid ya faɗa yana ɗan shafa ƙeya da komawa ciki domin kiran ƴan uwansa.
Master ya janye idanunsa da ga kallon Khalid da yayi ya maida kan baba Saude. “Baba Saude zaki dawo nan da zama. Akwai yarinya zata kasance da mu anan na wani ɗan lokaci ne, ALLAH yasa bamu takuraki ba”.
Baba Saude ta ɗan wawwaiga falon, dan ita bama ta lura da kowa ba. Amma sai ta ce, “Babu damuwa Babana, sai na dawo nan ɗin tunda ba wani abu nake acan ɗin ba, ba kuma wanine tare da ni ba balle nai tunanin barinsa. Kwana ne dama kawai ke kaini ai. Sai ina neman lamunin tahowa da ƴar marainiyar yarinyar nan dake wajena”.
Kansa ya ɗan jinjina mata, kafin a takaice yace, “Nagode”.
“Ai nice ya kamata nai godiya da karamcinka gareni babana. ALLAH ya saka maka da alkairi ya jiƙan iyaye da rahama. ALLAH ya bani tsahon rai da lafiyar kaiwa ran aurenka”.
Wani ɗan ƙasaitaccen murmushi ya saki da kaɗan ya nuna akan fuskarsa. Batare da ya ce komai ba ya maida dubansa ga su Habib da ke fitowa da shirin tafiya masallaci.
“A gyara mata ɗaki a nan ƙasa”.
Ya faɗa yana miƙewa.
Cikin rashin fahimta Habib ya ce, “Auntyn ko Baba Saude?”..
Wani malalacin harara ya zubama Habib ɗin tare da nufar hanyar fita. Batare da ya amsa masa tambayar ba yace, “Kaje da ita ta duba abinda babu zuwa anjima a faɗa min idan kun dawo salla, dan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nake son ta dawo gaba ɗaya”.
Cike da jin daɗi su Habib suka juyo suna duban baba Saude fuska a washe. “Finally baba Saude zata dawo kusa da mu gaba ɗaya”.
Ƴar dariyar jin daɗi tayi itama cike da so da ƙaunar yaran tana miƙewa domin yin salla. Suma suka fice cike da murna wannan zance na dawowar baba Saude kusa da su saɓanin da da zuwa kawai take tai musu girki ta wuce da yamma.
★★★★★
A can gidan su Hibbah kuwa zuwa yanzu ƴan uwanta sun fara shiga ruɗani, dan kamar wasa babu ita babu alamarta a cikin gidan. Lungu da saƙo sun zagaye har sashen su Hajiya mama da basama tunanin zataje. Tun sunayi su kaɗai har mutane da suka farga suka fara tayasu. Da ga cikin gida takai har an fito waje amma babu ko mai kama da ita. Babu ma wanda yace ya ganta bayan wanda suke a falon Ummi.
Yaya Muhammad ne ya tuno kiran da Shuraim yay mata. Wanda a dalilinsa ya sakata fita waje dan ta amsa. Kuma tabbas daga haka bata dawo ba har suka fita massallaci.
Kansa ya dafe yana ambaton “innalillahi....”
Gaba ɗaya suka maida dubansa gareshi a ruɗe. Ya cigaba da faɗin, “Tabbas Abubakar kayi gaskiya yaron nan hatsabibine na gaske. indai har hasashena yana kan dai-dai tun kafin a ɗaura auren nan ya ɗauke Hibbah.”
“What!?”.
Yaya Abubakar ya faɗa a razane, illahirin jikinsa sai tsuma yake.
Yaya Muhammad da ke jin juwa na kwasar sa cikin raunin murya yace, “Ƙwarai kuwa Abubakar ya ɗauke mana ita. Dan shine ya kirata lokacin da muke ɗaukar hoton nan amma sai taƙi ɗagawa, nine na korata waje akan taje ta ɗaga. Na tabbatar da ga lokacinne ya sace mana ita”.
Saurin riƙosa Isma'il dake a bayansa yayi ganin yayo baya zai faɗi. Yaya Umar kam ai dole ya kai zaune dan ya tabbatar ya cigaba da tsaiwar faɗuwar zaiyi shima. Yayinda tuni idanun Usman da Ammar sun fara kawo ruwan hawaye. Sauran abokansu kam da ke wajen kowa ya shiga halin taraddadi da tausayin su Yaya Muhammad. Dan kallo ɗaya zakai musu ka fahimci tsananin ƙauna da sukema ƙanwar tasu.
Komai ya kwance musu, tunani ma sun gazayi na neman mafita. Ammar da ke kuka ya nufi cikin gida da zummar sanarma Ummi dama tunda suka dawo sallar la'asar basu koma ciki ba. Saurin riƙosa Isma'il yayi yana girgiza