Showing 102001 words to 105000 words out of 155081 words

Chapter 35 - TAKUN SAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

25 Dec 2025

658

  Ya faɗa a yanda yasan dole zataji tsoro. aiko zumbur ta miƙe, ta ƙudundune bargon har kanta tana sauka a gadon da gudu tai toilet. Saurin riƙota yay, dan yasan tana shiga da bargon toilet ya gama yawo. “K miyasa sam mai bai wadaci kanki ba?”. Yay maganar fuska a tsuke. Jikinta taso fisgewa ya zuba mata ranƙwashi tare da fisgota ta dawo jikinsa. Zata fashe masa da kuka yace, “Karma ki soma”.
     Dolenta ta haɗiyesa kuwa. Jallabiyar sa daya cire mata jiya da daddare ya ɗakko mata. Yana ajiyewa a kan gadon ya juya ya fice a ɗakin yana danne dariyar dake taso masa. Raka bayansa tai da harara kafin taja jallabiyar ta saka. Koda ta shiga toilet ɗin saita yanke shawarar yin wanka. A gurguje tai wankan tayo alwala ta fito.
        Salla ta fara gabatarwa kafin ta kimtsa cikin kayan da aka kawo mata.   Har lokacin master bai dawo ɗakin ba. Dan haka ta fara gyara ɗakin. Tana gab da kammalawa Habib yazo yay kiranta. Sai da ta saka Hijjab sannan ta fito tana ta faman ɓata fuska. Duk zaune ta samesu a dining har uban gayyar daya canja kaya alamar yay wanka a inda bata sani ba. A kallo ɗaya zaka fahimci baida lafiya. dan idanunsa jajur suke ga wata ƙatuwar rigar sanyi daya ɗora. Gaisuwar da su Musbahu sukai mata ta amsa cikin ƙara ɓata fuska tana hararsu. Su dai murmushi kawai sukai dan babu damar magana boss na a wajen. Habib yaja mata kujerar kusa da Master dake karyawa, koda suka fito baiko ɗago ya kallesu ba abincinsa yake tsakura fuska a ɗaure, dan sam baya masa daɗi saboda mura. Dan ma yasa sun masa mai ɗan yaji da kayan ƙamshi ne.
       “Nifa na ƙoshi”.
Ta faɗa kanta a ƙasa dan gani take kamar duk suna kallon abinda ya faru jiya da daddare a fuskar tata. A karon farko ya ɗago ya kalleta da jajayen idanunsa. Babu shiri takai zaune dan kallo ne na gargaɗi da babu alamar wasa a cikinsa. Kofi ya ɗauka da kansa ya haɗa mata shayi tare da zuba mata soyayyan doyan ya tura gabanta. Kallon juna su Habib sukayi cike da iya shegensu. Adam ya dafe saitin zuciyarsa yana wani lumshe ido irin dai ƙauna takai ƙauna kenan.
      Hibbah kam kamar zatai kuka murya ƙasa-ƙasa ta ce, “Dan ALLAH a rage yamin yawa”.
      Bai ma nuna yajita ba, balle tasaka ran zai karɓi ƙorafinta. Sai ƙaramin bowl ɗin daya sha farfesun ya ture yana warwarar tissue ya goge bakinsa. Baya ya ɗanyi da kujerar yana ɗaukar wayarsa yabar dining ɗin. Su Idris na ganin haka sukai azamar cigaba da cin abincinsu dan sunsan yau akwai aiki tunda basu sami damar yi a daren jiyan ba saboda abinda ya faru. Ɓata lokaci kuma yana nufin amsar hukunci a wajen babban yaya.
       Khalid ne da yaga Hibbah na tsakurar abincin yace, “Aunty Queen ALLAH ki maza dan yana kallonki”. Hararsa tai tana tusa doya cikin baki. “To shikenan ashe da rabon ai miki ɗura ko”.
     Cokali ta ɗauka zata jefesa yay saurin mikewa yana dariya sauran ma na tayasa. Tashinsu a dining ɗin ya bata damar cigaba da cin abincin, sai dai kunnenta na jiyo mata bayanin da yake musu wanda bata fahimta ba cikin muryarsa da ke tabbatar da mura ta shakesa bana wasa ba. Har ya gama jawabinsa duk suka mike bata kammala ba. Sai da Habib ya fito yana sanar mata tayi maza ta kammala ita yake jira sannan ta mike. Ganin yana tattara kwanikan ta tayasa suka kai kitchen. Fitowarsu yayi dai-dai da fitowar su Salis cikin sabon shiri. Da kallon mamaki ta bisu ganin kowanne ya canja kamanni zuwa na daban. Zatai magana Master ya fito, dole ta haɗiye tata ta dauke kanta dan bata son koda wasa su haɗa ido.
       Cikin dakewarsa da ƙasaita ya fara magana cike da gargaɗi. “Ku kula, komai kanƙantar matsala ku sanar dani. Khalid kai da Salis zaku tafi a napep. Idris da Musbahu ku hau mashina. Idan komai ya dai-daita ku sanar dani muma zamu taho. Musbahu ka tabbatar duk layin da zaka shiga ya zamto mai tsayi ne, kamar na masu amsar ATM ko Customers care ”.
       “Insha ALLAH sir”.
Musbahu ya amsa cike da girmamawa. Kallonsu kawai Hibbah take tamkar ta samu television. Mamaki bai nema halakataba sai da taga sunkai zaune a falo sunyi addu'a nema nasara ga UBANGIJI kafin su Salis duk su fice a barta ita da sauran sai shi. Batare da ya kallesu ba yace. “Ku kuma ku biyo ni”
_______________________________

          ☀️🔴☀️🟠☀️🔴☀️🟠☀️🔴☀️🟠☀️🔴☀️🟠☀️🔴☀️🟠☀️🔴☀️🟠
*_K'AMSHI,K'AMSHI RAHAMA NE MATAN DA SUKA AMSA SUNANSU MATA SU SUKA SAN MUHIMMANCIN DA K'AMSHI YAKE DASHI MUSAMMAN A WAJAN MAI GIDA ,_*💃🏻💃🏻
*_Zafafan turarruka masu zazzafan k'amshi hade da wasu irin manyan sirrika na mallaka cikin sauki ba boka ba malam hajiya , Zaki jefe tsuntsu biyu da dutse d'aya , domin zamowa star azuciyar mijinki_*🌟🌟🔥

*_nasan dai kunada labarin mashahuriyar Mai Saida kayan k'amshin Nan Wanda akafi sani da *HUMKAM GIDAN K'AMSHI* *_a wannan karon ma ta sake kawo maku da sabbin kayanta masu abun al'ajabi Wanda da kud'i k'alilan zaku more zafafan turarruka Kuma ki shiga jerin Mata masu aji_*


*IDAN SARI KIKE BUKATA INA BADAWA SANNAN INAGYARAN JIKI CIKI DA WAJE SHIN KINA FAMA DA INFECTION INA HADA MAGANIN SA DA IZININ ALLAH KISHA KI WARKE*
*Kadan daga cikin kayan da muke dasu*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*BLACK KAJII*
shin kina bukatar turaren da Zaki turara gidanki ya dauke maki warin sanyi ya kwana biyu Yana k'amshi ,?ki saye black kajiji Zaki Gane banbancinsa da sauran wannan ba k'amshi kawai yake ba idan kina turara. Jiki dashi Yana maki maganin kala kala ciki kuwa har da na sanyi , nemi naki Kar ayi Babu ke☀️🟢☀️🟠🌟08132506044 HUMKAMINCENSE

*ANA WA HABIBY* Wannan harkan na oza room ne special turare Dan matan aure kadai yana dauke da abubuwa Wanda bazan fadesu anan ba sannan bashi kadai bane akwai Crazy powder da na ke hadawa dashi zakisha garin sannan kishafa turaren hmm


*SUDANESE HUMRA* Turare dake dauke da sirrika Mai DAUKAR hankali kamshin ya banbanta da sauran turare Hajiya babbar sirrine Wannan hadin manyan Mata  08132506044 HUMKAMINCENSE

*GLOWING OIL*
Wannan yasha bam bam da irin Wanda kuka Saba gani ,Yana kashe kuraje Yana cire tabo Yana maganin kezbi da duk wani matsalan fata ,stretch marks duk Yana ciresu ....

*MOWAR MACE*
turaren mowar mace turare ne da larabawa suke amfani dashi Wanda da yawa mutanenmu Basu San da wannan iccen ba Mai dauke da magani k'amshi da sauran abubuwan masu matukar amfani ga fata ba
Shi wannan iccen yanasa hasken fata yanasa fata tayi laushi da santsi sannan d'an alk'awari ne matuk'ar kina amfani dashi zai tsirga maki cikin fata ta yadda ko Bakiyi amfani dashi ba zakiji k'amshin shi na fita  ta cikin fatar ki ,ke amfanin iccen mowar mace yanada yawa jaraba ko don gyaran fatarki , 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Muna gyaran jiki na amarya da uwargida zakizo har gida ayi maki gyaran jiki irin na Mata masu aji zakiyi kyau kiyi fresh ga kamshin da zai Kama jikinki💃🏻💃🏻💃🏻

Munada 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*JAS OUD* (hatsabibin turare kenan )

*AL'AJAB* ( Mai abun mamaki kenan )AL'AJAB Turaren tsuguno mai abubuwan Al'ajabi  Yana maganin sanyi (infection) Yana matse HQ (Tightening)sosai 08132506044 yasa HQ dumi yasa jikinki da hq kamshi lokacin da kike AMFANI dashi idan Yana shiga gabanki zakiji wani Dadi na ratsaki Yana k'ara Dadi da Yana ciko gaba ya rikita oga🙈

*FIRST LADY*   na Mata masu aji turaren Kaya Dana daki
HAWII
KAJIJI
HALUT
👸🏻 *_PRINCESS_*
_Sabon turare Dana hada na shafawa ajiki da gashi *PRINCESS* Yana da Dadi cool kamshi gare shi babu hayaniya na fad'a muku sabbin turaruka na Nan tafe princess na daya daga ciki kisayi *PRINCESS* kiji sabon Hadi me sanyin kamshi babu kosarwa da ace zan iya zabi tabbas zan zabi princess a matsayin turaren gashina zan dauki princess ya zama shi zan farawa shafawa jikina idan zan kwanta zan dauki *PRINCESS* sbd yara na Dan kamshi bamai hayaniya bane musamman zan rika yi musu amfani dashi *PRINCESS* salon na daban kamshin daban dadin na daban *PRINCESS*  Zabin ku ne Zabin Humkam shine farin cikin ku Masoya *PRINCESS* gidan kowa_

Duk wad'an Nan turarruka ne hatsabibai masu rikita mazaje masu wani irin k'amshi Mai shiga zuciyar masoya 💃🏻💃🏻💃🏻

*SHU'UMAR HUMRA*
ke daga jin sunan kinsan ta dabance mashahuriyar humra ce ta tayi shuhura wajan birkita tunanin Yan maza , humra ce da indai namiji yajita a jikinki to komai muskilancinshi sai ya susuce maki tana tado da sha'awa shauk'i sirrin mallaka, cikin kankanin lokaci ki rikita maigidanki da daddadan k'amshin ki😍😍😍🥰


*HUMKAM GIDAN K'AMSHI INA NAN ZAUNE A KANO GA MASU BUK'ATAR ZAFAFAN KAYANA INA AIKAWA KOWANE GARI DAKE NIGERIA HAR MA DA K'ASASHEN K'ETARE , KARKU MANTA A DADE ANAYI SAI GASKIYA* 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

________________________________
    
      Duk mikewa sukai sukabi bayansa. Ganin Hibbah batako motsaba Habib yay mata alamar ta taho. Da ga can table ɗin da aka ajiye computers suka nufa. Kowa ya zauna ɗaya Hibbah dai na tsaye. jerarrun atishawa ya saki a cikin tissue ɗin daya warwara kafin ya dubeta da idanunsa dake jazur. “K zauna nan”.
     Yay maganar yana nuna mata kujerar dake kusa da inda yake tsaye. Idanu taɗan waro waje zatai magana ya tsatstsareta da nashi cikin gargaɗi. Tarasa miyasa take jin yau gaba ɗaya bazata iya masa tsiwa ba. Haka kawai wani irin shegen kwarjini yay mata ga kunyarsa da takeji matuƙa. Zuwa tai ta zauna a kujerar da ya ɗan ja mata baya.
          “Zaidu! Ka tabbatar ka dakatar da number Alhajin Mande daga shigar kira ko fita na tsahon awa guda shi da A.G. Adam! Accaunt na Engineer da Dr Sufi ka karasa aikinka na jiya a kansu, duk sauran kuɗaɗen dake a sauran bankunansu ka maida kuɗin a accaunt ɗinsa da na baka. Zakuyi da sauri. dan su Salis na gab da kaiwa, a yanzu haka suna cikin holdup ne”. Ya ƙare maganar idonsa akan agogon dake a tsintsiyar hannunsa alamar tanan yake bibiyarsu.
         Gaba ɗaya Hibbah tama rasa kalar tunanin da zatai, dan duk sun wani daburta mata ƙwaƙwalwa. Taja numfashi da sauri jin ya ranƙwafo ta bayansa, tare da ziro duka hannayensa biyu ta gefe da gefenta ya dafe table ɗin. A sarƙe taja numfashi tsigar jikinta na tashi, “Zaki fara aikinki da ga yanzun madam”.
         Yanda yay maganar a hankali saitin kunenta ne ya sata ɗan janye kanta, sai hakan ya bata damar jingina da kafaɗarsa ta gefen haggu, da sauri ta sake gyara zamanta a yanda take tana cigaba da shaƙar mayen turarensa dajin hucin zazzaɓinsa. Master da ke daƙilar keyboard ɗin Computern gabanta ya cigaba da mata bayanin abinda zatayi da nuna mata.
       “Shi aikin akan minene?”.
Ta faɗa cikin rawar murya.
“Babu ruwanki da ko na minene. Ke dai kiyi kawai”. Yay maganar yana ɗaukar hannunta ya ɗaura bisa mouse ɗin. Yatsansa manuniya ya ɗaura akan nata dake dai-dai kan ƴar tayar tsakkiyar mouse ɗin. Tai ƙoƙarin janyewa ya matse hannun. “Ki nutsu bana son shirme fa ok!".
         “Amma ai ya kamata a sanarmin aikin kafin nayi”.
     “Ashe baki son komawa wajen Ummi kuwa”.
     Amsar tasace ta sata sake ƙwaɓe fuska tamkar zata fasa ihu. Ga a yanda suke duk kunya ya dabaibayeta. Badan kujera data shiga tsakanin bayanta da ƙirjinsa ba a yanda suken tamkar ya rungumeta ne. Sai da ya gama nuna mata duk yanda yake bukatar tayi kafin ya janye jikinsa da ga nata. Wani wawuyan ajiyar zuciya ta saki lokacin da yake mikewa. Har sai da su Habib suka ɗan kalleta. Dan tunda ya duƙo kanta basu sake yarda sun kalli sashen da suke ba. Wata ajiyar zuciyar ta sake saki ganin ya nufi hanyar bedroom ɗin da suka kwana. Badan yace idan ta ƙiyi bazai kaita wajen Ummi ba da tabbas bazatayi ɗin ba, amma tana buƙatar ganin ahalinta zata iya komai dominsu. Kusan mintuna goma sha uku da shigarsa sai gashi ya fito. Badan ta tabbatar da bayan shi ɗin babu wanda ya shiga ɗakin ba da babu yanda za'ai ta yarda shine. Ya canja kayansa zuwa manyan kaya irin na tsoffin dattijan Alhazan kauyen nan harda rawani, ga uban farin sajen da ke akan sabuwar fuskar daya canzo sak wani dattijon ƙwarai irin wanda basuko damu da duniya ba. Sai sanda a hannunsa da dogon carbi. Hannunsa kansa sun canja da ga nasa zuwa kalar fuskar zam. Ya zaro ƴar karamar wayar nokia ɗin data sha wani shegen farin salatap da har ya fara komawa brown dan tsufa. Kunnensa ya kai alamar kira ya amsa. Yana sauke wayar a kunne yana duban su Adam da suka mike.
      “Done”.
Suka faɗa a tare shi da Zaidu. Kai ya jinjina musu yana maida dubansa ga Habib. “Ka kula da komai, abinda bata gane ba ka nuna mata, aikinta ne na tsakkiya samun matsala daga gareta yana nufin komai zai ɓaci”.
      Kai Habib ya jinjina masa da faɗin, “Insha ALLAH mune da nasara. ALLAH ya dawo daku lafiya”.
     Amin ya faɗa yana duban ɗakin da su Zaidu suka nufa, sai kuma ya kalli agogon hanunsa irin na sarƙa ɗin nan da yaci duniya ya koɗe matuƙa duk da Silver ne dama. Dai-dai nan su Zaidu suka fito da sauri cikin sabuwar shiga suma. Daka kalli Adam bashi da maraba da driver. Zaidu kam tamkar irin yaran alhazan kauyen nan da bakinsu bai rabo da tsugudidi. Ga jikka ya riƙe wadda ko ba'a faɗaba kasan ta alaramma Muhammad Shuraim Master ce dai.
     “Ga kuɗin an shirya Master”.
Zaidu ya faɗa yana buɗe jakkar hannun nasa mai kama da karamin akwatin maza na tafiya. Shiryayyun kuɗi ne a ciki ƴan ɗari biyar-biyar da ɗari bibbiyu. Kai ya jinjina masa kawai alamar komai yayi.
      Inhar ana mutuwa a zaune to yau dai da alama Hibbah ta mutu. Dan harsu Master suka fice a falon bata gama dawowa hayyacinta ba sai da Habib ya fargar da ita. Cikin alamar ruɗani tace, “Ina zasuje wai?”.
    Murmushi Habib yayi yana ɗan matso da kujerarsa kusa da tata kaɗan. “Aiki zasuje mana.”
      “Aiki?”.
Hibbah ta faɗa cikin sigar tambaya. “Babu lokacin tambaya aunty Queen mu cigaba da namu aikin dan mune tamkar ƴan jagorarsu. “Gaskiya indai satar kudaɗen mutanene bazanyi ba”.
    Tai maganar tana ƙoƙarin mikewa. Kamar daga sama taji muryarsa yana faɗin, “Ashe kuwa ke da Ummi har abada. Na kuma gama aiki nace yayunki sukayisa”.
    Waige-waige ta shigayi cikin falon sai dai babu alamarsa. Sautin muryar tasane kawai data kasa fahimtar da ga ina yake fitowa. Kuka ta fashe dashi tana komawa ta zauna a kujerar. Lallai ta tabbatar yau tana a tsaka mai wuya. Abinda takeji a labari yau shi hannunta zai aikata.
      “Kuka bazaiyi magani ba aunty Queen, duk wani motsinki dake anan tamkar akan idonsa ne garama kiyi kawai".
     Habib yay maganar cike da lallashi. Kamar ta makesa shima takeji, shiyyasa taki tanka masa ta cigaba da abinda takeyi zuciyarta na kawo mata wani shawara acan gefe. Yarda da shawaran yasata share hawayenta ta maida hankalinta ga aiki kamar yanda Habib ke nuna mata shima yanayi.

      A ɓangaren Master kuwa sun isa banki a tsohuwar motar da Adam ya tuƙasu. Adam ne ya taimaka masa ya fito a motar shi a dole ga dattijon da yaci duniya jiki yay laushi. Yana gaba Zaidu na biye da shi yana zuga surutu da kyalƙyala dariya irin dai garorin nan yan bani na iya na gefen alhaji. Shiko Master sai wani gaftarar goro yake yana ƴar dariya da bama Zaidun amsar wasu zantukan nasa.
     Gaba ɗaya kallon garori securitys ɗin bank ɗin sukai musu. Bayan an dubasu babu alamar wani abun ashha tare da su aka basu damar shiga. Yanda Zaidu ke zabga surutu Master na dariya yasa mafi yawan mutanen dake akan layin tura kuɗi da amsa kallonsu, wasu na musu dariya wasu na musu kallon ƙauyawa ne. Master dake lure da motsin kowa ya yafito wani gaye da ya tsuƙe cikin shigar manyan yara yanata bada iska. “Yaro yaka nan ka taimakeni, dan wannan mai bakin kamar bututun mai yanda bansan a ba shima ba bihim ya sani ba. Garama ni nayi yaki da jahilci lokacin da nake zuwa sarin atamfofi na manta wasu abubuwanne kawai.
     Gayen da gaba ɗaya ya gama ƙiyastama ransa tsuntsu da ga sama gasashshe ya karaso yana wani taɓe baki. Wata cimirmiɗaɗɗiyar takarda Master ya fiddo a aljihu ya mikama gayen. “Yarona duba mini nan, ƴan kuɗaɗena na kayan amfanin gona dana noma na sayar zan buɗe akawun na zuba. Nima jikana dake can kudu ya bani shawara amma yace na nema wannan daya rubuta min anan zai taimaka mini aimin komai na buɗe akawun din na zuba kuɗaɗena a ciki naje gida nai barci babu ruwana da takadarai”.
     A karon farko gayen ya dashare baki da faɗin, “Ai babu damuwa baba koni ma na maka. Kaga zomuje can sama acan ake buɗewa.”
    Babu musu Master ya amince. Suka nufi saman bene Zaidu na biye da su. Gaye da gaba ɗaya hankalinsa nakan jakar hannun Zaidu ya sami ma'aikaci guda sukayi magana. Form aka basu da zasu cike suka koma can gefe inda babu yawan mutane.
     A ɓangaren master tun shigowarsu wajen yaga Musbahu, shima kuma ya gansa dan cike da ƙwarewa sukaima juna alama da ido. Kafin Master ya ɗauka ƴar nokia ɗinsa ya fara magana da ƙarfi har hankalin mutane na dawowa kansa. Wasu na dariya wasu na tsaki wasu taɓe baki. Dan kuwa dai garanci zam Master ke zubawa abinsa Zaidu na tayasa cikin kwakwazo shima.
     Da wannan damar gaye yay amfani wajen saƙala hannunsa a hankali ta ƙasan teble ya zuge jakkar hannun Zaidu. Rafar yan dari biyar ya jawo har sau uku ya tura aljihu, yayinda a gefe tuni Zaidu ya sane wayar gaye daya ajiye akan table shi kuma. A dai-dai nan Musbahu yazo a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login