Showing 54001 words to 57000 words out of 155081 words

Chapter 19 - TAKUN SAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

25 Dec 2025

675

da Ummi. Ayye mama ayye mama, mamaye iye, ayye mama labo labo, mamaye iye. Da aure yana raka aure, mamaye iye, dana biki mun tafi tare. Mamye iye, ko tuƙin tuwo ƙya koya, mamaye iya, har damun fura ƙya koya.........”
      Kuka Hibbah ta fashe da shi da faɗin, “Ummi kin gansa ko. Wlhy nama fasa dan babu inda zanje to”.
     Da farko dariya Ummi da su Yaya Muhammad da suka shigo keyi, sai da sukaga abin nata da gaske ne sai kuma duk jikinsu yay sanyi. Dama su kansu dauriya kawai sukeyi. Dan tun shigowarsu sukaci karo da akwatinan sai zukatansu suka raunana. Suna matukar son Hibbah, gashi aure zai rabasu rana tsaka. Ita kanta Ummi wani lokacin har tambayar kanta take wai miyasa ma ta amince aima Hibbah aure yanzun ne. Itakam bataso a rabata da ɗiyarta. Zuciyarta kan gaya mata su waɗanda ƴayanta maza zasu auro fa? Da ta tuna hakan kuma sai tai shiru ta miƙa wuya.
     Ɗaki Ammar ya wuce yana sharar hawaye, dan dama komai da yakeyi dauriya ce kawai. Da gudu Hibbah ta tashi tabi bayansa ta rungumesa. Sai kawai suka fashe da kuka a tare. Duk yanda su Yaya Usman sukaso daurewa hakan ya gagara, suma sai gasu suna share ƙwallan a kaikaice.  Saurin barin falon Ummi tai, batasan yaya suka ƙare ba sai da ta fito bayan sallar isha'i ta samesu suna kallo ball Hibbah da Ammar na gaddama harda jefama juna filos tamkar basune suka gama shan kuka ba ɗazun.

       Washe gari bayan wucewar su Yaya Muhammad aiki aka miƙa kayan nasu auren gidajen matansu batare da sanin su Abba ba. Dan daga gidan Sheikh Aliy aka ɗauka. Hibbah ce kawai taje aka kai da ita ko ina. Dan haka ranar bataje makaranta ba. Sai da yamma liƙis ta shigo gidan a gajiye, ga ciwon kai. Sama-sama ta gaida Ummi ta shige ɗakinta acewarta zata watsa ruwa.
     Tana fitowa wankan ta tsinkayo muryar Ummi na kwala mata kira.
          “Tanee! Tanee!!”  muryar Ummi dake ƙwala mata kira da ga falo ta cigaba da shiga kunnuwanta. Amsawa tai cikin saka kaya sauri-sauri sanann ta fito. Ganin Ummi zaune tare da Isma'il ya sata ƙalaro fara'ar dole ta yafama kanta. “Uhm su Yaya Isma'il ne yau a gidan namu? Yaushe a gari inji maƙi baƙo?”.
        Guntun murmushi ya saki dai-dai yana ɗagowa ya kalleta. “Auta nifa hausar nan taki cikin hausa na dulmiyar dani da yawa.”
         “Tofa, abinma ƴar zolayace kenan Yaya Isma'il. Ykk ya Abba da Dubai?”.
        “Abba yana lafiya. Nima kuma haka. Dubai kam tana can mun baro musu abinsu, mun dawo ƙasar gado”.
       Dariya Ummi da Hibbah sukai a lokaci guda. Yayinda Ummi ta ɗora da faɗin, “Yau kusan sati kenan inata jajen rashin dawowarka. Ga bikin ƴan uwanka nata matsowa ko faɗa maka ba ai ba”.
      “Biki kuma Ummi? Badai su Yaya Muhammad bane zasu angwance?”.
        “Aiko sune Isma'il, komai yazo ne a ƙurarren lokaci. Su duka huɗun ne insha ALLAH sai Tanee kuma”.
      A take alamar shock ta bayyana saman fuskar Isma'il har Ummi da Hibbah suka lura. Da sauri ya ce, “Ummi Muhibbat kike nufi kowa?”.
        “Eh ita kuwa Isma'il. Muma dai haka abin yazo mana tamkar haɓo”.
         Duk yanda yaso ɓoye ɗacin da ke tattare da muryarsa kasawa yay. “Ummi dama akwai maganar aure akan Muhibbat kenan?”.
          Ummi da yanayin Isma'il ɗin ya raba ma hankali biyu tace, “A'a Isma'il. Cikin kwanakin nan dai aka fara. Da yake kuma ALLAH yasa abin a kusa yake sai gashi har an kammala magana. Dan gaba ɗaya bikin yau saura kwana goma sha uku ne”.
           “A...ALLAH sarki, UBANGIJI ALLAH ya sanya alkairi ya basu zaman lafiya Ummi. Dama zan wuce ne nace bara na leƙoku. Inga bara inje zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zan dawo. Ga tsarabarki nan ke da Muhibbat”.
           A yanda yake maganar ne ya saka wutar kan Ummi da Hibbah ɗaukewa. Sukai tsit a falon harya fice basu iya furta komai ba. Sai kallon juna da sukai suka kuma sake maida dubansu ga ƙofar tamkar zasuga Isma'il ɗin tsaye bai tafi ba.
         “Ummi kamarfa ransa ya ɓaci?”.
“Nima abinda ya bani mamaki kenan Tanee. Ko maganar aurenku ce ta ɓata ransa?”.
        “To Ummi mizai bata masa rai anan? Maybe dai akwai abinda ke damunsa daban ba wannan ba”. Hibbah ta ƙare maganar tana sakkowa da jawo ledar daya ce tasunce. Turarrukane a ciki da make-up box ƙarami mai ƙyau. Sai takalmi da jakka suma masu ƙyau kala biyu. Na Ummi da nata.
         Tana tsaka da ƙoɗa ƙyawun kayan Yaya Muhammad ya shigo. Ummi ce kawai ta samu damar masa sannu, Hibbah kam sam hankalinta baya wajensa. Sai da ya kai zaune yake faɗin, “Ummi lafiya kuwa? Miya faru da Isma'il?”.
          “Wlhy ban saniba Muhammad, nima man mamakin yanayin nasa ne ya sani zaman jugum nan.” (gaba daya ta kwashe yanda sukai ta bashi labari).
       “Tofa, anya kuwa Ummi Isma'il ba son Hibbah yake ba?”
    Da sauri Hibbah ta juyo ta kalli Yayan nata. “Yaya so kuma? Ni?”
       “Tabbas auta. Dama zuciyata ta jima tana rayamin Isma'il dan ke yake tare da mu. Dan take-takensa gaba ɗaya sun nuna akwai soyayyarki a zuciyarsa. Shiyyasa naso ace yana nan maganar nan ta taso na aurenkin nan. Koba komai ni hankalina ma zaifi kwanciya da Isma'il ɗin fiye da shi Shuraim ɗin nan. Duk da shima dai babu wani aibu tare da shi dan yau ɗin nanma sai da na sake samun bayanan binciken da na saka akaimin a kansa bayan waɗan can na baya”.
      Nannauyan numfashi Ummi taja, gaba ɗaya zuciyarta ta dagule. Dan harga ALLAH tana jin son Isma'il matsayin siriki a gareta. Sai dai kuma ƙaddara ta rigada ta riga fata. Dan babu ta yadda za'a gyara abinda tun farko aka ɓata. Shima harda laifinsa da bai fito ya nuna ba, a yanzu kuma basu da hurumin rusa maganar Shuraim inba so suke su kasance ƙananun mutane ba kuma.
     Ita dai Hibbah ko a jikinta. Tama cigaba da harkar gabanta ne dan kallon yaya take masa har cikin zuciya.

★★★

     Kwanaki uku Isma'il bai sake dawowa gidanba. Hakan duk sai yabi ya dami Ummi harta ɗauka waya ta kirasa akan tana son ganinsa. Baiko musa ba sai gashi yazo da hantsi. Lokacin su Hibbah duk sun fice sai ita kaɗai.
        Ummi tanada dabaru sosai na iya sarrafa mutum bisa ƙyaƙyƙyawar hanya. Shiyyasa ta tarbiyanci ƴaƴanta da tarbiya mai ƙyau da ke bama kowa mamaki da yaba ƙoƙarin ta. Duk da Isma'il yazo mata ransa a cinkushe cikin hikima da dabarun da ALLAH ya bata ta bi da shi da nasiha. Cikin ƙankanin lokaci sai gashi yayi laushi, ya kuma gane cewar laifinsa ne da yabar zancem a ransa bai furtaba.
      “Ummi nagode matuƙa da gaske. Kiyi haƙuri ban tashi da uwa ba shiyyasa abubuwa da yawa bana ganesu kai tsaye sai sun ƙure min. Idan kuma ba'an fahimtar dani bane haka zanta kallonsu a yanda na ɗauka. Bazan boye miki ba ina matuƙar jin daɗin kasancewa da ke. Kuma ina miki kallo ne irin na uwa wlhy. Shiyyasa kikaga ko yaushe ina nane da ke. ALLAH ya sanya albarka a auren Hibbah na haƙura. Amma tabbas ina sonta da ƙaunarta. Wasu kuma nagartattun halayenki ne da nata suka jani ga hakan abinda ban taɓa tsintar kaina a ciki ba. Amma dan ALLAH koda wataran inaso ki cigaba da tuna hakan. Kuma kamar yanda kika fahimtar dani wanann bazai zama ƙarshen zumincinmu ba. Zan cigaba da kasancewa da ku a koda yaushe tamkar da. Zanje na nema yan uwana su Yaya Muhammad mu cigaba da hidimar biki”.
        “Alhmdllh naji daɗin hakan Isma'il, ALLAH yay maka albarka. Kaima ALLAH ya baka wadda tafi Tanee ɗin”.
     Murmushi ya saki mai sanyi laɓɓansa na ɗan motsawa alamar amsawa. da ga haka ya saki jiki da Ummi suka cigaba da tattaunawa akan hidimar bikin. Bata ɓoye masa zancen barinsu gidan ba da planning ɗinsu akan rusa auren ƴaƴan Abba da yaranta. Shima kansa yaji daɗin haka. Ya kuma tabbatar mata zai bada muhimmiyar gudun mawa. Da ga haka yay mata sallama ya tafi.

*___________________________*

         Alhamdulillahi, akwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, shirin biki kam da gaske ya ɗau harama. Dan kuwa baƙi harsun fara sauka a gidan musamman na ɓangaren momy matar Abba. Hakama dangin hajiya mama sun fara sauka. A ɓangaren Ummi ne dai babu ko kare da yazo har yanzu. Ko'a jikinta dan dama batasa rai ba. Mutanen arziƙi ma da zata tara anan a cewarta sun wadaceta.
           A ɓangaren amaren su Yaya Umar na ɓoye har sun jajje sunyi jere a sabon gidansu. yayinda suma anan su hajiya mama suna shirin zuwa suyi nasu jeren na ƴaƴansu a gidajen Hayar da Abban ya kama.
          Itama dai Hibbah kayan nata jeren har sun isa gidanta. Dan kuwa yayunta sun haɗa ƙarfi da ƙarfe da taimakon Isma'il sun mata kaya ƴan gaske na ƴar gata. Dan data ga kayan sai kawai ta fashe da kuka dan daɗi. Ita kanta Ummi da ta gani sai da ta koka a ɓoye. Musamman da ƴan jere suka dawo cike da farin cikin tarbar da suka samu da kuma ƙyawun gidan na Hibbah.
      Hibbah Amarya kuwa da su Zahidah amaren su Yaya Usman Ummi da Mama Jiddah ce ke gyaresu da ingantattun magungunan sanyi harda amaryar Yaya Umar. Sai ingantaccen tsumi da duk ta sami iliminsu da ga Sheikh Aliyn ta (karku manta masanin sirrin magunguna ne😹). Dan hatta maganin sanyin ma shine ya haɗama su Hibbah da kansa. Sai Haɗaɗɗun kayan gyaran fata na dilka da ƙamshi da Mama Maimoon uwargidan malam ke gyaresu da su itama. Ta ko ina Ummi dai ta zama ƴar kallo.

       Gaba ɗaya Hibbah ta tattara batun wasu ƴan sanda da wani master can😏 ta watsar, dan kasancewar su waje guda da su Hafsat ya mantar da ita komai. Iyakarsu susha shaftarsu, kowa idan nata angon ya kirata ta koma gefe tasha soyayya. To ita Hibbah ma bazatace soyayyar take sha ba, dan sam Shuraim bai cika damuwa da kiranta a waya ba. Yafi tura mata text massege na sonjin lafiyarta kai tsaye. Ita kuma jan aji yasa itama bata kiran nasa balle nuna damuwarta da hakan garesa. ko sau ɗaya ma bata taɓa ƙorafi ba.

        ★★★

   A yau laraba aka saka dukkan amaren a lalle. Dan kamar yanda aka saka su Ameerah da Hibbah anan gidansu, haka aka saka su Zahidah a nasu gidajen batare da duk wanda ke zagaye da su yasan su waye angunan ba. An dai san ana biki, hatta da Momy da Hajiya mama sunsani tunda anguwa ɗaya ne layi ɗaya. Sai dai basusan anguna ba basu kuma damu da sani ba tunda ba wani mu'amula mai karfi ce a tsakaninsu ba. Hasalima sun tsanesu saboda suna huɗɗa da Ummi. Ko gidan sukazo aka gamu da ƙyar suke amsa gaisuwarsu.

    Yau akai kamu da ya kayatar matuƙa anan harabar gidan. Dan ƙarya sosai momy ta nuna ma ƙawayenta data tara cike da gida da danginta. Sai dai kuma koda anguna sukazo fili bisa gayyatar da akai musu sai suka ƙare da bama autarsu kulawa ta musamman. Dan har liƙeta sukai da kuɗaɗe sanda masu kiɗan ƙwarya ke bugawa. Nanfa ƙananun magana suka fara tashi, zukatan su Ameerah fal baƙin ciki da takaici. ji suke wata muguwar tsanar Hibbah na sake shigarsu matuƙa, amma dai duk sun danne a zukata bisa huɗubar iyayensu akan shirinsu.
     Oho su Yaya Abubakar ma basusan sunai ba. Su dai kawai burinsu autarsu tayi farin ciki, tafi kuma kowa. Burin nasu kuwa ya cika. Dan ta haska haskawa mai tsayawa a rai duk da ango baizo ba danginsa sunzo ansha shagali da su.

     Washe gari kuma alhamis akai walima da hajiya mama ta ɗauki nauyi😝. Aka gayyato matan Sheikh Aliy sukai wa'azi, yayinda aka ci aka sha kowa yay ɗiff. Gab da magrib aka tashi. Su Ameerah kuma suka dasa nasu fatin su da kawayenau maza da mata a hotel. Babu ango ko ɗaya a wajen, dan su su Yaya Muhammad ma zuwa lokacin suna manne da Umminsu dake ta musu nasiha suna sharar hawaye tamkar ba gida ɗaya zasu cigaba da kasancewa ba. Hibbah kuwa kuka take iya iyawarta harda amai. Da ga ƙarshe kuma sai zazzaɓi ma ya rufe ta. Har sai da Isma'il da yazo kawo drinks da za'ai amfani da shi na ɗaurin aure ya kira family doctor ɗinsu yazo ya dubata. Ana mata allura yay tafiyarsa shi da doctor ɗin.

*_RANA BATA ƘARYA........_*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😂.

*LALLAI YAU AKE TAKUN SAƘAA😖🐒*


TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082





*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*





*_Chapter Nineteen_*

...........Kamar yanda suka saka ɗaurin aure bayan sakkowa sallar juma'a su Ummi basu canja ba. Gida ya gama cika da dangin Momy da na Hajiya mama anata hidimar girki. Sai wasu tsiraru da ga abokan arziƙin Ummi na nan anguwa dana nesa.
        Anguna kam suna can a gidan da suka samu aro anan anguwar da abokansu. Sai dai tunda safe sun shigo sun gaida Umminsu. Tare da sake lallashin ƴar ƙanwarsu Hibbah da duk tabi ta takura kanta. Zazzaɓin nata yama sauka tunda safe amma duk ta zama wata kalar tausayi. Magana kaɗan sai ta kama hawaye. Ga ƙawayenta na secondary cike da ɗaki amma duk ta ƙi sakewa. Sai faman shaƙiyanci suke mata ta kasa maida murtani dan bakin ya mutu murus.
          Kusan sha ɗaya wata ƙawar Ummi ta shigo ta sata tashi dole tai wanka. Mai kwalliya ta shigo tai mata dai-dai misali dan da farko ma catai bataso sai da Ummi tai magana. Itama taci gayunta ɗas tamkar wata ƴar talatin. Dan sam Ummi bata da ƙiba, ALLAH yayi mata jiki mai ƙyau, shiyyasa da yawan mutane idan akace itace ta haifa su Yaya Muhammad sukan musa, inba ka nutsu wajen kallon fuskarta ba sai ka ɗauka yayarsu ce kawai.
      Amarya Hibbah ta fito ras abinta, tamkar ka saceta ka gudu. Ƙawayenta nata tsokanarta akan gaskiya ya kamata a ɗauka hoto a turama ango. Banza tai musu dan ita sai ma yanzu ta tuna da wani ango. Tun jiya damuwarta kawai rabuwa da ahalinta batashi take ba. Ga shi tanajin kewar su Zahidah da babu dama suzo nan suma suna gidajen iyayensu.

      A ɓangaren amare su Ameera ma kowacce ta ɗau kwalliya ta gani kasheni, da ka gansu kaga amare kam dan anata zuba iyayi da gwalli. Su barin gidan ma ko'a jikinsu suke jinsa. Ga ƙawayensu sun zagayesu sai taɓara da zancen banza suke zubawa suna sheƙa dariya.

         Ƙarfe sha biyu da kusan kwata anguna suka shigo gidan cikin kwalliyar fararen shaddoji tas iri ɗaya. Hatta da Ammar irin kayan ya saka shima. Idan ba'a faɗa ba sai ka ɗauka shima angon ne. Guɗa mata da ke kai kawon girki a tsakar gida suka shiga musu. Kowa na yaba ƙyawun nasu da yima mahaifinsu addu'a da babu rabon ya ga wannan rana.
         Ummi da ƙawayenta na zaune a falo suka shigo. Tai sagade tana kallonsu idanunta na cika da ƙwalla. Tanaji a ranta inama ace Aliyu na raye wannan rana...... Durƙusawar da sukazo gabanta sukai duka ne ya katse tunaninta. Tasa hannu ta share ƙwallar da suka taru mata a ido tare da kai hannu ta dafa kan Yaya Usman da ke kusa da ita. Sai kawai ta fashe da kuka. Har rige-rigen matsawa suke gabanta kowa ya riƙe hannunta idanunsu na cikowa da ƙwallan suma.
        Sosai abin ya birge mutane ya kuma basu tausayi. Ummi ta shiga kwarara musu addu'oi da sanya albarka ana amsawa da amin. Kafin a kira Hibbah itama mai hoto yay musu. Itama kanta sai da tai hawayen jin daɗin ganin ƴan uwanta kamar ka sacesu ka gudu dan ƙyawun da sukayi. Sai dai tanajin ɗacin kasancewar su Amlah matsayin matansu bayan su Zahidah.
      Suna tsaka da hotunan kira ya shigo wayar Hibba. Tayi ƙoƙarin sharewa aka sake kira. Yaya Muhammad dake kusa da ita ya ɗauka wayar ya duba. Ganin Shuraim ke kiran nata ne ya sashi hararta yana miƙa mata. “Auta bana son rashin ji fa. Maza kije da ga waje sai ki ɗaga”.
      Kanta kawai ta ɗaga masa. Tare da tashi tabi ta kitchen ɗinsu ta zagaya baya domin kiran Shuraim ɗin......
      “Yauwa A.G zamu iya magana yanzu na fito”.
    Muryar Abba ta saka Hibbah saurin dakatawa a ƴar barandar kitchen ɗin nasu. Abu biyu ne yaja hankalinta ga Abban. Na farko yanda yake tsaye a laɓe wajen tamkar wani tsohon munafuki, na biyu sunan A.G da taji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login