Showing 12001 words to 15000 words out of 37977 words
ya yi.
Mama takaici kamar ya kashe ta, ta mike tsaye tana cewa, Na kuwa daina tada hakarkarina a kan a sake ki, don ki auri mai sonki da gaskiya, tunda naga kina son abinki duk rashin kirkinsa, hada kayanki kafarki kafarsa, kafin a kara yi min abin da yafi karfin idona.
Haba! Hauwa ta rushe da kuka tana, Na tuba Mama, na tuba na bi Allah na bi ki, wallahi ba inda zan iya zuwa in barki.
Mama ta yi kwafa ta ce, ji min munafurcin Hauwa-Kulu, yau da kika sa kafa kika bishi kika barni ma na sani? Ni a wa? Bi mijinki a sha soyayya lafiya, da ma tare na ganku.
Na so ki bari mu wujijjiga shi yadda zai kara sanin darajarki, to kin kwashi jiki kin bi shi kun sha soyayya ko? Bayan ya kwashe shekara bai neme ki ba, da yake ke sakarya ce wadda ta rako mata, kiss din abun banza ne da ki ka barshi ya samu a arha?.
Hauwa kuka kawai ta ke na nadama da kaka-nikayi ta kasa magana, duk sai ta bai wa Mama tausayi.
Ta sassauta ta kama hannun Hauwa, ta ce, Ba ki yi min laifi ba Hauwa kin ji, kuma ba ki yi wa Ubangijinki ba.
Karewa ma lada ki ka samu kinji.
Ni na san Sarham yana sonki duk abin da nake yi kuma ina sane. So nake in sa shi ya gane da kansa yana sonki ba auren jihadi da taimako ya yi da ke ba. So nake ya furta min da bakinsa ya janye kalaman kanwar nan da yake jifanki da ita, It does hurts me a lot!
Karshen kaskancin da namiji zai miki kenan, ya tari gaban idon ki yace, ba ya miki so na soyayya. Sarham ba shi da saiti, ki bar ni in saita shi yadda ko wani ya ji ya ce ke kanwarsa ce zai musa da bakinsa yace aah matata ce abar so na.
Hauwa na kuka da sharbe ta ce,
Insha Allah Mama ba zan sake yarda ba.
Tausayi ya kama Mama don kuru-kuru ga soyayyar lelen Abba nan ta fito yau a idonta, da ko gani ba sa yi, ina ga suna ganin cool kamanninsa da kyakkywan sajen sa da murmushinsa mai daukar hankalin mata?
Mama ta tashi ta fita kwallar tausayi fal idonta.
Mardiyya ta dawo dakin tana cewa,
Anti ba ki ci abinci ba, Anti don Allah ki daina kuka yana daga min hankali.
Ta hau share hawayen da gefen mayafi ta ce, Na daina Mardi!.
Ta ce, To abincin fa?
Sai an jima, ki kulle mu ta ciki, ko Yaya Doctor ne ya buga kada ki bude kin ji? Murajiar karatuna zan yi.
Taje ta dauro alwalla, sai ta ga cewa ba za ta iya alwala a haka ba, dole sai ta yi wanka don abin da ba ta taba gani ba ne ta gani a tare da ita yau.
An gaya mata kuma da jimawa wankan iri daya ne da na sallah.
Ta yi sallah ta dora da nafila ta zauna tana murajiar karatun da Mama ta kara mata jiya.
Cikowar yan uwansu da abokan arziki a gidan ma bai barshi ya iya sake shigowa da daddaren ba balle ya tadda kofar tasu a kulle da mukulli bisa umarnin ko ya buga kada Mardiya ta bude.
Dangin mijin Surayyah suka ce su a wannan ssatin zasu dauki amarya zuwa Ikko don haka dole aka zarce da bikin maimakon sai sati mai zuwa da mama ta saka. Don haka a washegari aka yi wunin Surayya a Gadon Kaya, da daddare dinner sai shirin kai amarya gidan su Engnr. Aliyu a Dorayi washegarin ranar.
Hauwa ba ta je dinner ba ta kulle kanta a daki, amma Mardiyya ta je. Mama ta sameshi har dakinsa ta kora masa ‘warning’ din kada ya kara shiga dakin Hauwa sai ya zo mata da hukuncin da ya yanke wa zamansu.
Shi ma kuma yana ta nasa shirin duk don ya wanke ran Mama, ya kuma yi ‘repenting’ kuskurensa, tuni ya karbo passport din Hauwa ya kai gun visa.
Yan biki duk sun watse bayan an kai Surayya family house din su mijinta. Yau kwana uku kenan Mama na gadin Hauwa, ta hana shi kebewa da ita. Ta hanashi rawar gaban hantsi. Iyakar tsaka mai wuya Sarham ya shige ta don sosai yake cikin bukatuwa da Hauwa, don haka ya maida hankali wajen sakin kudi a yi a gama visarta. Ga Abba ya ki shiga maganar, ya ce shi a bayan mai sharia yake.
*** *** ***
MUTANEN JEDDAH
Sumayyah ce kadai zaune a falon gidan Yayanta tana karatu da gilashi a idanunta, aka danna kararrawar son shigowa, Sumayyah ta mike ta aje littafin da ke hannunta tana fadin, Naam, ina zuwa. A zatonta Madinah ce ta dawo daga unguwar data tafi.
Tana budewa suka yi tozali da wani sardidin saurayi son kowa. Amma kuma fuskarsa looks so familiar to her.
Ya yi mata murmushi, ya ce, Salam, how are you? Tana ciki ne matar gidan? Na kasa kama ta a waya”.
Sumayyah ta kasa magana, don gayen ya kai makura wajen kyau, ga tsafta ga sanyin murya.
Da kyar ta iya cewa, Ba ta nan!.
Sai ya mika mata wata leda ya ce, ok. Please ga shi ki bata, kice in ji Hajja Ramlah.
Hannun Sumy na rawa ta karba sai ya ce, Ke bakuwa ce suka yi halan daga Nigeria?
Eh. Kawai ta ce.
Ya ce, Ok, toh. Ki gaya mata zan dawo bayan magriba. Sunana Usman Attahiru, yaya sunan malamar?
Oh! Are you? Usman?
Ya ce, Yeah.
Anti na yawan zancenka, ina ji kullum. Nice meeting you.
Ya ce, Na gode, kin san sakuwata ce. Kullum fada muke a baya, ina cin zalinta in more, shiyasa yanzu nake kyautata mata, na maida kaina ma direbanta at times, don in wanke kuruciya mara dadi da muka yi nida ita.
Duk suka yi dariya mai sanyi.
Ya ce, Ya sunanki?
Sumayyah Abbas.
Oh-oh! Ko ke ce Sumayyah kanwar Baban Waheedah?
Eh ni ce.
By the way, nice to meet you too Sumayya, I love the name.
Cikin murmushi Sumayya ta ce, Na gode Uncle Usman. A gaida gida.
Bayan tafiyarsa Sumayyah ta adana sakon, amma sai ta kasa zaune ta kasa tsaye, Usman Sorondinki da muryarsa ya tsaya mata a rai farat daya, irin yadda wani namiji bai taba shiga ranta ba.
Madinah na dawowa Sumayyah ta bata lokaci ta kintsa, kafin ta kai mata sakon har dakinta, karonta na afarako da sanya kafarta a dakin Madinah tun zuwanta gidan. Ita kanta Madinah ta sha mamaki.
Ya zo nan kadan kafin dawowarki, yace shi Yayanki ne, wai Osman sunansa.
Oh! Zai dawo an jima, mun yi waya na manta da zuwansa ne na fita.
Sumayyah ta ci gaba da shiru a tsaye, ta kasa tafiya, Madinah ta ci gaba da sabgoginta ta manta da ita. Ganin haka ta ja matattun kafafunta ta fito daga dakin.
Ko da ya dawo kamar yadda ya ce zai dawo, Sumayyah ya cimma a falo Madiah tana daka tana sallah don haka suka balle da hira shi da Sumayyah, kan kace meye wanan sabo ya fara shiga tsakanin Usman da Sumayyah, bini bini ya zo gidan bayan ada sai in Madinah ce ta kira shi ko Hajjah Ramlah ta aiko shi, ya zama suna dasawa sosai har ta kai su ga karbar lambar wayar juna.
Kafin ka ce me? Madinah ba ta ankara ba aka soma yi mata midnight call’ a gida. Sumayyah har mantawa ta ke Usman Attahiru Yayan Anti Madinah ne, gabadaya ta rufta nan take, kafin dawowar Sarham.
Ranar da Madinah ta fahimci wai soyayya ake tsakanin Sumayya da Usman ta sha mamaki, at the same time a take anan ta nuna wa Usman rashin goyon bayanta, da hujjarta na cewa Sumayyah tun fil azal ba ta kaunarta, kuma an gaya mata ita ce ta hannun daman matar wulakancin da sarham ya auro mata.
Usman kuma ya ce mata, a gaskiya shi bai son gutsiri tsoma irin na mata ba, ya ga Sumayyah ta yi masa, komai nata ya yi masa ba ruwanshi da shirmensu, Sarham kawai yake jira ya dawo ya gabatar da kansa.
Madinah ta lashi takobin ita kuma sai bayan ranta Usman zai auri makiyarta. Ko mata sun kare a duniya bazata bada goyon baya ba, dama dai Surayyah ce kuma tayi aure ita.
**** **** ****
KANON-DABO
A
ka kawo masa visa din Hauwa a wayewar garin litinin, bayan an gama bugawa. Mama na shirin fita office sallamar Sarham ta dakatar da ita. Ya shigo dakin da karfin gwiwarsa yau dai, da kallon marairaita da karbar laifi, suka gaisa shi da Mama ba yabo ba fallasa.
Cikin brown envelope ya mika mata abu,
Ga shi Mama na karbo!.
Mama ta amsa ba tare da ta san meye a ciki ba, tana kokarin budewa ta gane passport ne.
Za ta fara fadan har yaushe aka je aka yi passport din ita bata sani ba, ta tuna subutar bakin Hauwa na cewa, sun fita da Sarham kwanaki. Ta yi kwafa kawai ta aje a gefe ko bude visar ba ta yi ba balle ta ga wace iri ce ko ta wata nawa ce. Murya fal ladabi Sarham ya dukar da kai yace,
Mama kin yi izni za mu iya tafiya tare? Already na yi mana booking jibi ne tashin namu insha Allah.
Mama ta yi shiru, ya ci gaba da roko, da ban hakuri da ban baki da alkawarin bazai kara maimaita kuskurensa ba kuma zai kula da Hauwa tsakaninsa da Allah. Da kyar Mama ta ce,
To karatunta fa?
Ma yi wannan shawarar daga baya in mun je naga yadda abubuwa zasu kasance.
Mama sai ta kasa musantawa, tunda abin da ta ke rokon Allah dare da rana ne yau Ya amsa musu. Sarham ya dawo kan hanya kuma ya fahimci kansa. Ko bai fada ba ta ga ‘seriousness’ a kan Hauwa wannan karon a tare da shi sosai.
Duk da haka ta kawo nata kalubalen na cewa, ya zai tafi da Hauwa babu Mardiyyah?
Wa zai dinga taimaka mata?
Sarham ba tare da tunanin komai ba, ya ce, I will take care of her, my self Mama, for the mean time, kafin in yi deciding akan ko zan iya daukar Mardiyyar a gaba. I will do everthing to undo the hurt I caused you Sweet Mum.
Mama tayi ajiyar zuciya a karshe, ko bata ce ba hakan na nufin amincewarta.
Hankalin Mardiyyah ba karamin tashi ya yi ba jin Mama ta ce ta hada wa Antinta kaya za su tafi Jeddah.
Mardiyyah tana kayan Hauwa a jakar matafiya tana kuka wiwi, amma ta danne bakin da dankwalin ta kada Hauwa taji kukanta, amma saida taji sheshsheka. A kwance take amma saida ta tashi zaune tace Mardhiyya lafiya? Ta gaya mata abinda aka ce da ita. Hauwa kanta jikinta yayi wani irin sanyi. Mama ta alkawarta ma Mardhiyyah tafiya Saudiyyah tare da ita duk lokacin da za ta je umrah, kuma ba za ta mayar da ita Shanono ba ko ba Hauwa a gidan, za ta ci gaba da zama tare da ita ne har aurenta.
Hauwa kanta na kasa, ko dagowa ta kasa yi sabida nauyin Mama da damuwar data cika ranta. Mama lakca guda ta hau yi mata a kan ta zauna lafiya da kowa da zama ya hada ta da shi, kuma ta girmama Madinah tunda ko a girme ta girme ta, ba a aure kawai ba.
Ta ce, Na san ba ki da matsala ko kadan a kan girmama na gaba da ke Hauwau, amma zaman mata biyu karkashin inuwar miji daya sai an daure an kai zuciya nesa ba kusa ba. in ba haka ba duk zaku taru ne ku kai junanku wuta. Ki sa a ranki ibadah ki ka je yi domin zaman aure ibada ne Hauwa, balle wanda ya zamo ku biyu ne a wurin mijin.
Jikin Hauwa bakidaya ya yi laasar ta soma hango babban kalubalen dake gabanta, nan take ta ji kamar ta ce da Mama babu inda za ta je, amma ganin yadda Mama ke ta kai da komowa wajen yi mata shirin tafiyar, da bata magungunan da bata san ma kona menene ba da yadda Sarham din kansa ya dauki komen nata Jeddah da matukar muhimmanci sai ta kasa magana, duk da Mama ba ta kara bari sun kebe ba, ta maida Hauwa dakintama kwata-kwata ana saura kwana biyun su tafi, tana ta yi mata kyakkyawan shiri da tsumi kala-kala da tukudi.
Ita kanta Hajiyar Abba, wato Hajiyar Gadon Kaya cewa tayi ba ta ga dalilin zaman Hauwa tare da su ba, in makaranta ce ai babu inda babu ita. Kada su sake su bata mata rai su tattara mishi Hauwa ya dau kayarsa. In don rashin ido ne ya sa Mama ajiye ta shekara guda a daki ai ya fi kowa sanin ba ta da idon ya je ya auro ta.
Ranar sun sha fadan Hajiya Kulu wadda ta yi tattaki har gida ta sille Mama da Abba don Sarham ya gaya mata takunkumin da Mama ta saka masa na saki, da yaki kuma ta kuma hana shi ko magana da Hauwa.
Shi ya sa ma ranar da ya kawo visa mama ba ta yi dogon jainja ba, don Abba ya ce a daina yin duk abin da zai saka Hajiya Kulu yin fada, saboda BP dinta.
**** **** ****
Duk wani shiri na tafiyar hauwa Mama ta gama sbhi cikin lokaci, komai da tasan zata bukata ta tanadar mata. Kuma ita da kanta ta kai su filin jirgin Malam Aminu a ranar tashin nasu. Bata dawo gida ba sai da aka kira fasinjoji domin shiga jirgi.
A daren ranar duk kokarin Sarham na samun Madinah a waya bai yiwu ba, ko network ne ko wayar tata a kashe take? Ya so tun a daren ya gaya mata cewa tareda Hauwa zai dawo. Ta shirya mata daki daya cikin dakuna biyun da bata amfani dasu. A zuciyarsa baabu fargabar komai, don yarda zuwa yanzu dole ya kara zama namijin duniya a tsakanin matan nasa kuma ya zauna da Hauwa cikin iyalinsa cikin adalci, bai yarda da raba gida ba shi raayin sa shine samar da kyakkyawar muamala ta fahimta da taimakekeniya tsakanin Jiddah da Madinah kasancewar Hauwa nada lalura. Ba zai kaita wani gida ta rayu ita kadai ba.
Yana fatan wannan din ya hada kan iyalin sa da samar da zaman lafiya da kaunar juna a tsakanin su. Don shi wai bai yarda da hargagin Madinah na cewa ita Madinah tafi Hauwa komai ba, wai don tana takama da tanada zurfin ilmi da iyaye masu kudi yen-yen-yen to shi ina ruwansa da wadannan din, tunda dai shi ko wani nasa bai taba aikawa gun Daddy neman taimako daga ISDB ba, itama ba su ne dalilan da suka yi mujazar auren shi da ita ba.
Dr. Sarham Abbas ne rike da hannun matarsa Hauwa Bilyaminu, suna taka matattakalar jirgin ‘emirate’ wanda zai tashi da su zuwa kasa mai tsarki a daren yau.
Hauwa kankame ta ke da hannun Sarham cikin tsoro na rashin sabo take taka matattakalar, shi kuma ba tare da damuwa da kallon da ake musu ba ya rike hannun nata sosai yana gaya mata cewa,
Mind the stairs (ki kula da matattakalar).
Lokacin da jirgin ya karci kasa zai tashi, Hauwa