Showing 24001 words to 27000 words out of 37977 words
Don cikin abubuwan da ya lissafa bakidaya wato abubuwanda ya bata zabi ciki har dana zama da shi ko aah? Ko yin muamala mai kyau da matarsa Hauwau, ko ta dinga dafa abinci tana bata ita tana kwana da miji, ko ta zauna da matarsa cikin aminci, babu wanda za ta iya aikatawa a cikinsu gabadaya.
Don haka ta yanke shawarar yin abinda take ganin ya fiye mata aala, wato komawa aikin asibiti, in yaso ta dauke ido daga kansu ta bar musu filin gidan ya cinye matarsa Hauwa-Kulu makauniya Kulu don soyayya.
Amma ita kam ta gama hada jiki da Sarham! Don zuciyarta ba za ta jure sharing miji da makauniya ba. Sannan ba za ta zabi zuwa gida ta yi rayuwar zawarci da yi masa rainon Waheedah a gidan iyayenta saboda kishiya ba.
A take ta dauki waya ta buga zuwa Dr. Siddiqah Hospital Jeddah. Zuciyarta a matukar kuntace. Hakika kishin mijin da kake matukar so abu ne mai matukar ciwo da sai wanda aka yiwa ne kawai zai iya bada labari. Amma abu daya zamu tuna mu kwantar da hankulanmu cewa auren mazajenmu sunnar Annabi ne, umarnin Ubangiji ne, na su aura daga abinda yayi musu dadi daga daya-daya ko biyu-biyu ko uku-uku har hur-hudu, don kare kansu daga dattin zina.
Abinda ya kamata Madinah da sauran mata irinta mu duba kenan, mu sassautawa zukatanmu.
Ta tabbatar musu da amsar aikinta da ta ce a dakatar sai ta yi yayen Waheedah, Dr. Madinah dai ta yi kyakkyawan kudiri na fita harkar mijinta a dalilin kishiyar da ta ke ganin ba ta isa zama kishiyarta ba, saboda makasar ido da Allah ya dora mata da kuma da asalinta.
Har gobe tana son Sarham dinta, kuma matsayinsa bai canza a zuciyarta ba, amma ta yanke shawarar jingine shi a kan dai ta yi sharing dinsa da Hauwa.
Maganar da ya yi na bata zabi na zama da shi ko aah ya girgiza ta, tabbas namiji ya baka option na zama da shi ko barinsa to hakika ya kasa jure drama dinka ne. Yanaso ya kawo karshen ta ya huta.
A rayuwarsu bata taba yi wa mijinta horon yunwa ba amma yau kishi ya koya mata, bata taba kwararsa a shimfidar auren su ba, amma yau duk kishi ya koya mata har ta kware da hakan, ta jingine komai na hidimar mijin, wato shi kansa Sarham din ta yafe, da ita kanta soyayyarsa da ke ranta duk ta basu baya, da bukatuwarta da shi a matsayinsa na mijin da ta ke matukar so wanda suka gama gina rayuwarsu tare duk ta yafe, tunda har ya iya rufe ido ya yi mata kishiyar da bata kai ta komai ba, a lokacin da bata taba tsammani ba, don haka duk ta hakura da su ta barwa yar cikin Badala, watakila ta hakan ne zai gano muhimmancinta da bambancin da ke tsakaninta da Hauwa.
Asibitin sun tabbatar mata ko a gobe ne ta zo ta yi reporting don suna matukar bukatarta dama. Don haka tun a daren ta ce ma Hajjah Ramlah gobe za ta kawo mata Waheedah zata fara zuwa aiki a Dr. Siddiqah.
Hajjah Ramlah da tausayi Madinah ke bata yanzu, don ta fahimci son da take ma Sarham ya zama jarabta ga rayuwarta, tunda har ya iya yi mata wannan tozarcin, amma ta kasa barinsa.
Ta ce, Ki kawo ta, bayan aiki ma ki kara da ayyukan sa-kai a asibitin gwamnati da philanthropic ayyuka duka, kuma ki ci gaba da tafiya programs da ki ke zuwa na marriage coaches rana daya kika daina yanzu, ki bar musu gidan tun safe har dare, in yaso ki barshi da makauniyar ya ci uwar da zai ci da ita, fitinannen yaro kawai marar godiyar Allah, ina ganinsa mai kirki ashe macijin sari ka noke ne, in ki ka daina wuni a gidan na ga wanda zai kula masa da makauniya.
Tunda aurensa ya zame miki jaraba kema dai kamar aka ce shi ne autan maza.
Murmushi Madinah ta yi, Hajjah ba za ta gane ba. Tabbas Sarham shi ne autan maza, amma a wurinta da duniyarta kadai, don ita kadai ta san ko waye shi, da darajojin da Allah ya yi masa, wadanda ba duka maza ya yi wa alfarmarsu ba.
Za ta ci gaba da zama karkashin aurensa har karshen rayuwarta, ko da ya sake ta ne a kan karan kansa to kuwa za ta ci gaba da zaman rainon Waheedah don ba za ta iya auren kowa in ba shi ba, Sarham is her life, her happiness, amma dole ta jingine shi yanzu, tunda ya ki zame mata namiji dan goyo.
Sannan maganganunsa na yau sun kara kashe jikinta daga tunanin rabuwa da shi haihata-haihata, amma dole ta janye masa.
Tayi zurfi a wannan tunanin lokaci mai tsaho, tana jin sanda ya gama girkinsa ya rufo kitchen din, gidan duk ya bade da kamshin farfesun kayan ciki da jallop din cous-cous da Sarham yayi, don su suka fi masa saukin hadawa. Ya dauka da kansa akan ‘tray’ ya jera duk abinda zasu bukata ya dauka zuwa dakin Hauwa.
Sai Madinah ta yi mishi ‘text messege wanda bata da tabbacin ya gani ko ya karanta, cewa gobe in Allah ya kaimu za ta yi reporting fara aiki da Dr. Siddiqah hospital.
A karshe ta ce masa “tana neman yardarsa”.
Yana dakin Hauwa sakon nata ya shigo wayarsa don haka bai duba da wuri ba.
Maijidda barcin bayan isha ba shi da kyau, tashi ga abinci na hada mana.
Jin muryarsa ya sa Hauwa tashi zaune daga kwanciyarta, yace ba kya ko cigiyar mijinki cikin gidannan. Hauwa ta ji kunya na mijinta da ya ce din don dai ita har yau ta kasa sabawa. Wai Likitan Innane miji agareta.
Ya ajiye abincin akan ‘center table’. Ya zauna daidai kafafunta, idanunsa na bin yatsunta da suka sha adon baki da jan lalle a hade da Mardiyyah ta yi mata da wani nisantaccen kallo na yabawa. Sai ya ji motsin shigowar sakon Madinah a wayarsa.
Fiddo wayar ya yi, ya karanta sakon nata. Girgiza kai ya yi, ya kuma mayar mata da gajeruwar amsar cewa,
Allah ya yi jagora.
Daga haka ya kishingide abinsa a gadon Hauwa, ya dora kansa bisa cinyoyinta, ita kuma tana zaune tsakiyar gadon ta mike sambala-sambalan kafafunta, ta bar masa cinyar yana shan raba, ya ce kasa-kasa kamar cikin rada.
Ba ni labarin rayuwar makarantarku BUK, da yadda ki ke coping a aji kullum, I know it will not be easy for you at all.
Sannan kuma dai an gayamin wai har da samari da Farfesoshin jamia ke bin layi gun Abba, duk da aure na? Ya fada (with a little bitterness) a muryarsa. Hauwa dai bata tanka ba sabida a lokacin hannunsa ya kai bisa lallausar tafin kafar ta, ya ja babban yatsanta da wani irin salo, mai bayyana manufa ingantacciya.
Kafin ya mirgina ya kai bakinsa tsakiyar tafin kafar tata ya sumbata. Tsigar jikin Hauwa ta tashi yarrr! Gabadaya, ta kasa ce masa komai, tana jin sanda Dr. Sarham ya janyo ta bakidaya jikinsa ya ce,
Maijiddah, zo ki samu lada kinji, wannan yunwar da ke ji tafi wadda nake ji ta abincin dana dafa mana.
Nan ma shiru ta yi, jikinta ya soma bari, don ba duka ta gama healing ba, kamshin jikinsa da niimar numfashinsa su suka agaza mata tsoron yake raguwa, lokacin da ya fara sarrafata son ransa, bakidaya ya hautsina Hauwa-Kulu. Yayi sama da bakinshi a hankali ya bata kyakkyawar sumba a kuncinta da lips dinta hannunsa sarke cikin yatsunta.
Daga nan yace. “wannan barin jiki haka? Ki yi hakuri zan yi a sannu, I promised I will not hurt you kamar jiya.
Hauwa ta rasa inda za ta saka kanta don kunya, gabadaya Sarham ya shige cikin jikinta, ga numfashinsu ya sarke wuri guda, wato ya zamanto numfashi guda suke shaka nasa kadai sabida kusancin da ya assassawa fuskokinsu, da lips dinsu daya sarke wuri guda yana caressing dinsu softly. Hannunsa ya kai ga zip din rigarta kuma ba tare da ta samu sukunin rikewa ko gardamawa ba, ya kai zip din kasa. Cewa yake cikin gigicewa.
Na kara janye kalamaina, na kara janye su daga gareki Maijidda, YOU ARE MY LOVE! My true love and eternal happiness. Not a sister!.
Hauwa ji ta yi hawayen farin ciki na sauko mata ta koina saboda yadda Dr. Sarham ya himmatu wajen fassara son nan a aikace, by caressing her tears da tsinin halshensa. Ya hanata kowanne irin katabus, nauikan sumbar yau daban suke, sumbace yake mata kala-kala naui-nauI data kassara dukkan gabbanta, ta kuma fahimtar da ita irin yadda Dr. Sarham yake da matukar son sumbatar matarsa har fiyeda ya tara da ita.
Wayyo Inna! Hauwa ta furta cikin son kasar ta tsage ta hadiye ta kawai ta huta da kunyar da Sarham yake jefa ta a yau.
Wato wannan din ita ce rayuwar da Mama ke mata fighting mata don ta samu, shima kuma akan karan-kansa ita ce irin soyayyar da yake ikirarin ita baya yi mata a can baya?
Tana iya jin amon sautin muryarsa har zuwa lokacin cikin kwanyarta, a sanda yake cewa, ya janye kalamansa na baya.
Yau kam ta gasgata cewa Mama Uwa ce ta gari kuma mai sonta da alkhairin da kowacce mace ke samu a gidan aure, ta yarda Mama Uwar kowa ce ba ta Sarham kadai ba, domin yau ne ita ma ta san tana da wani boyayyen feeling mara fassaruwa a kan Sarham da ba ta san da shi ba sai yau. Kuma yau ne ta san mecece soyayyar kanta.
Da kyar ta roke shi kan yayi hakuri tana jin yunwa kuma bata yi sallah ba. Abincin da sai da ya sandare Sarham da Hauwa suka samu cin sa. Kasancewar dama a bowl na tangaran ya zuba musu baa warmers ba.
Da ya dawo sallah ya samu itama tana sallah, sai ya dauki abincin ya ajiye a kan ‘center-table’ ya jira har ta idar, shi ya zuba musu abincin suka ci a bowl guda.
Tun kafin ma ta gama cin abincin ya karkade gadon ya sake shimfida da sabon zanin gado hade da duvet dinsa, ya dauke wancan ya saka a kayan wanki, ya gyara dakin ya kimtsa komai da ta bata a dakin ya fesa room fresh, ya kuma hada mata ruwan wanka.
Hauwa na kammala cin abinci ta ji ta dauke a hannun Sarham. Bai direta ko a ina ba sai cikin ruwan wankan da ya hada ya saka ta da kayan jikinta da komai gaba daya, yace I wish you could see.. cewa yau tare Sarham da Hauwa zasuyi wanka abinsu. Gadaya ya sukurkuta Hauwa, ya kidimata da abinda yake fada. Daga bisani ta dauka marfi take yi saboda alamuran da yake gudanawar a gare ta masu ruda kwakwalwa ne da kidima masoyi, Hauwa-Kulu za ta iya cewa a cikin kwamin wankannan ta kara amsa sunan matar Sarham ba tare da ta ankara da yadda hakan ta faru ba. Amma hakika ta yi dauriyar da shikansa ya yaba mata. Don ba ta yi wani hobbasa don hana shi samun nutsuwar da ya nemi samu daga gare ta ba don ganin cewa a toilet ne, ta jure duk ta faranta masa rai a yadda ya bukata.
Shi ma kuma ya biyar da ita ne ta hanyar da ya kara mamaye zuciyarta da so da matsanancin so da kaunarsa.
Tun daga ranar Sarham da Hauwa suka dinke suka zama abu guda, musamman da Madinah ta ba su fili ta hanyar fita sabgar mijin kwatakwata, sai hakan ya bashi damar samun wani irin kusanci da Hauwa-Kulu, Madinah ta fara zuwa aikin dole datasa kanta, su kuma sun zama tantabaru don soyayya a gida. Wani lokacin yana office da ya samu sararin aiki kawai zai tuko motarshi ya dawo gida, ya kuma samu Hauwa matan da ake shuara bata nuna gazawa bata korafi akan dukkan bukatunsa, Hauwa sai yadda yake so ta ke yi, wato sai abin da ya koyar da ita.
Madinah na tunanin bar musu filin gidan da ta yi shi zai sa Sarham ya yi marmarinta, ya gane banbancinta da Hauwa, wato ya gane bambancin da ke tsakanin musaka da mai aji, bata san cewa a fannin matantaka duk mace sunanta mace ba, in dai tanada koshin lafiya kuma tana kula da jikinta, bata san hakan ya bai wa Sarham da Hauwa damar dinkewa ba suka manne wa juna suka like kamar tip da taya cikin morar niimar da Allah ya halatta a tsakaninsu, da wata irin soyayyar auratayya mai wuyar fassaruwa.
Kusan kullum ne Sarham sai ya sato jiki daga office ya dawo gida, don dai ya tabbatar da lafiyar Hauwa dama kuma Mama ta gama shirya yar ta tsaf, fiye da tsammanin dan Adam, don haka Hauwa ta gama tashin kan Sarham gaba daya, tunda Madinah ta shata layi a tsakaninshi da ita tun zuwan Hauwa gidan, a cewarta ta barwa Hauwa, tana kyamar hada miji da mijin musaka.
Madinah kam sai dai ya gode mata da wannan filin da ta bashi yake wani irin amarci kamar bai taba samun lafiyayyar mace a hannunsa ba sai a kan Hauwa. Shi da kansa ya hana Sumayya dawowa gidan, ya gaya mata ba yanzu ba, sai sun gama honeymoon, kada tazo ta bata masa mata da kilbibi.
Ko daga nan Sumayya ta gane Hauwa komai zamzam, don ko waya bata samun amsawa yanzu, kullum likita na makale da ita, ta nan Sumayyah ta gane komai ya fara saisaita. Farin cikin Sumayyah ya kasa boyuwa. Ga Usman ya like yana bin Sarham da gaske yana so ya turo ayi tambayar aurensa da Sumayya. Sarham kuma yana basarwa yana cewa ya nemi amincewar Madinah.
Madinah wadda a lokacin fama take da kanta, cikinta ya fara girma da ga matsaloli irin na mace mai juna biyun da ya fara tasawa, ga rashin kwanciyar hankalin data sawa ranta na barranta kanta da rayuwa da mijinta, wanda ta debi shekara da shekaru cikin fafutukar samunsa. Wannan yasa ba tareda sanin ta ba, a tsaitsaye BP dinta ya hau, yau tana asibitinsu tana duba patient mai hakiyar ido, Hauwan Sarham ta fado mata a rai. Tsaki tayi kanta yayi mugun sarawa, kawai sai ta saki komai ta dafe kanta, ta sulale a kujerarta cikin wani hali na unconsciousness. With high blood pressure.
Nurse din da suke tare suna duba patient din ce ta ankara da gushewar hayyacin Dr. madinah, tayi maza ta yi kanta ta, kuma dinga danna ‘alarm’ na kiran likitoci da gaggawa.
A karshe gado aka baiwa Dr. Madinah a asibitinsu. Nan da nan aka shiga bata taimakon gaggawa don tana bleeding, kokarin su shine su tsayar da cikin jikin ta amma a karshe suka ga tsayar da shawarar gara su cire shi don ceton nata rayuwar.
Sarham na asibiti yana aiki Usman ya kira shi wai yazo yasa hannu zaa yiwa Madina tiyata a Dr. Siddiqah.
Tsananin kidima data same shi a lokacin manta hanyar asibitin nasu yayi sai Usman ne suka hadu a hanya yayi masa jagora.
Ya samu duk yan gidansu Madina sun riga shi hallara a asibitin shikadai ake jira amma kafin ya zo ma Daddy ya kulu ya saka hannu yace a shiga ayi mata, ciki kuma a cire shi in shi ke bata matsala. Babban Yayansu Madinah wato Abubakar Attahiru yace Daddy baka da wannan hurumin fa, ka bari mijinta ya karaso. Sai gashi ya shigo kamar an jefo shi shida Usman.
Daga kallon da Hajjah Ramlah take masa duk ya sha jinin jikinsa. Amma ya maida hankali ga yin needful, wato ya saka hannu aka shiga da Madina dakin tiyata.
Dukkansu jigum-jigum sukayi a reception shida iyayen Madina da yayyenta, Hajjah Ramlah ta kasa shiru tana tsane ido tace wallahi in Madinah ta rasa ranta saboda kai Sarhamu, bazan taba yafe maka ba, tun farko ai nace ta hakura da aurennan babu dole tunda har zaka iya rufe ido kayi mata kishiya da makauniya nace ta hakura, amma da yake kunnenta na kashi ne ta zauna a gidan kuna guma mata takaicin da yau yake neman ranta.
Alhaji Attahiru Habibu Sorondinki, ya kankance ido akan matarsa yana neman karin bayani yace me ke faruwa wai? Ki yi min bayani. Hajjah Ramlah na kuka ta zayyane masa komai cewa Sarham kara aure yayi da makauniya yar talakawa shine fa tun lokacin Madina take boye musu itama daliline yasa taji data yi tsami tsakanin ta da kanwar mijin nata.
Alhaji Attahiru jikinsa har tsuma yake ya nuna Sarham da dan alinsa yace wallahi in ya ta ta mutu sai nayi karar ka, azzalumi wanda bai san mutunci ba. ai shiyasa