Showing 48001 words to 51000 words out of 116224 words
komai?shin zai amince da abinda zata faɗa masa ko yaya? Wane irin kallo zai musu idan yasan cewa amminsa ce ta kashe sarauniya Nazli da yaranta tare da baban tareeƙ,kuma abakinsu?anya kuwa basu barowa kansu aiki ba?
"Nanny kiyi magana mana kinyi shiru, ki sanar dani wake da hannu akan hadarin nan?"
Da sauri nanny ta dawo daga dogon tunanin data tafi,kallon tareeƙ tayi cike da karayar zuciya ,amma cikin ƙarfafa gwuiwa tareeƙ ya kalli nanny yana mai jinjina kai da nuna alamun ,kwantar da hankali.
Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe Tana mai kallon fuskar Adeeb,kafin ta fara magana.
"Magajin fada kamar yadda na faɗa maka,wasu abubuwan muna kallonsu ne ba a yadda suke ba,ka sani abinda zan faɗa maka ba ƙarya ,ba kuma cutarwa.shiru ta ɗanyi tana jinjina maganar kafin taci gaba"ba kowa ya shirya wannan hadarin ba, face Amminka"nanny ta faɗa tana mai kure Adeeb da ido.
Da wani irin slow Adeeb ya mike tsaye bakinsa bude,zuciyarsa na wani irin bugawa kamar guduma, ji yayi kunnensa ya ɗauki wani ƙara ƙuuuuuuuu!!!
Sai yake jin maganar ta nanny Tana rarrabewa,kamar baiji me take faɗi daidai ba,jikinsa rawa ya kama,ta yadda yana mikewa tsayen yaji kamar zai fadi dan haka da sauri ya koma ya zauna,idanunsa ƙuri,akan fuskar nanny,
Cikin in-ina ya ke cewa"na...nan.,...y mek....Ike ..son....f..a...ɗ..I n..ee." ya faɗa numfashinsa na rarrabewa,ji yake kamar zuciyarsa zata fito tsabar yadda take bugawa.
Da sauri nanny ta ƙaraso kusa da Adeeb ta zauna ,cikin nutsuwa take shafa bayansa tare da kallon fuskarsa cikin tausayawa,dole yaji maganar tazo masa kamar saukar aradu."ka nutsu Adeeb domin Abinda nake faɗa maka yana buƙatar nutsuwa,tabbas Amminka itace ta shirya wannan hadari,tare da taimakon wani ma aikaci dake cikin gidan nan,mai kula da harkokin motocin gidan"nanny ta faɗa cikin sanyin murya tana jin zafin rashin mijinta da uwar dakinta kamar yau abin ya faru.
Kallonta Adeeb yake cikin wani irin yanayi na mamaki ,al'ajabi,tsoro,ruɗu dakuma firgici,ji yake kamar zuciyarsa zata iya fashewa ako wane lokaci,wannan wane irin magana nanny keyi?anya kuwa tana cikin hayyacinta?yaushe nanny ta koma maƙiyarsa ta hanyar hade kai da amma?dan su shiga tsakaninsa da amminsa? Dan kuwa yana tabbatar da cewa wannan shirin amma ne,lallai duniya ba tabbas .cikin zuciyarsa yake wannan maganar,kafin a fili ya kalli nanny ,sannan ya kalli tareeƙ,sai kuma yayi murmushi wanda yafi kuka ciwo ,sannan ya miƙe tsaye yana mai sanya hannunsa cikin aljihu,sannan ya fara magana bayan ya juya bayansa yana kallon bango" ban taba tsammanin cewa matar data raineni tun ƙuruciya zata iya hade kai da makiyana,ɗan ganin sun shiga tsakanina da ammina ba ,yau na kara tabbatar da cewa lallai wanda kake kallonsa matsayin masoyi ,to shine makiyinka aboye, amma bantaba tsammanin haka daga gareki ba nanny;Adeeb ya faɗa cikin zazzafar murya yana mai juyowa ,idanunsa sun kada sunyi mugun jaa, kallo ɗaya zaka masa kasan cewa zuciyarsa akaraye take.ci gaba yayi da cewa"nanny why ?why nanny me yasa zaki canja daga yadda na sanki?me yasa zaki so ganina cikin damuwa?na dauke ki tamkar mahaifiyata,duk wani abinda ya dameni ina zuwa gareki dan samun mafita,ammina tana kula dake da duk wani bukatun ki,amma meyasa kika hada kai da maƙiyanta?me yasa kika saida kanki dan bata alaka tsakanin da da mahaifiya?nanny why?tareeƙ me yasa nanny zatayi min haka?Adeeb ya faɗa yana mai riƙe kafadun tareeƙ idanunsa na zubda kwalla ,gaba ɗaya jinsa yake kamar ba shiba, wani sashen na zuciyarsa yana son karbar maganar nanny,saidai sashe mafi rinjaye na zuciyarsa na tunatar dashi wacece ammi agareshi,dan me zai yarda da batun nanny?.
Cikin damuwa da alhini tareeƙ ya kama hannun Adeeb ,cikin murya mai nuna tabbatarwa ,tareeƙ ke fadin, "yallaɓai ka kwantar da hankalinka,kuma kayiwa maganar nanny kyakykyawar fahimta,da sannu zaka gano gaskiyar dake cikin batunta, yallaɓai munsan abubuwa da dama wanda kai baka sansuba,amma da sannu zaka gane da kanka"tareeƙ ya faɗa cikin marairaita yana kallon Adeeb.
Fizge hannunsa Adeeb yayi tare da dafe kansa da yake jinsa kamar zai tarwatse,kafin ya kalli tareeƙ yana mai jinjina kai"well na gane ,na gane tareeƙ kaima kana bin bayan mahaifiyarka ko?da kai aka hada baki,am disappointed tareeƙ" Adeeb ya faɗa yana girgiza kai cikin karayar zuciya,idanunsa na fitar da hawaye mai tsananin zafi da ƙuna.ahankali ya juya ya nufi ƙofa yana dafe kansa .
Cikin damuwa da zubda kwalla nanny ta miƙe da sauri tana kiran Adeeb" magajin fada karkayi saurin yanke hukunci akan maganata kana bukatar nutsuwa da bincike dan Allah ka yarda dani ɗana, bazan taɓa cutar da kaiba."nanny ta fada cikin zubda hawaye .
Ko waiwayowa Adeeb baiyi ba ya fice daga ɗakin ,cikin sauri, dan ko ganin fuskar nanny baya sonyi ahalin yanzu.zuciyarsa na tafarfasa ,ji yake kansa kamar zai kama da wuta.kai tsaye part ɗin ammi ya nufa ko zai sami salama cikin zuciyarsa.
"Tareeƙ ka gani ko?kaga Abinda nake faɗa maka,Adeeb ya riga ya makance,baya ganin laifin ammi ko kaɗan,yanzu bansan wane kallo zai rinƙa yi mana ba"nanny ta fada cikin kuka.
Kamata tareeƙ yayi ya zaunar da ita akan kujera ,hannunsa ya sanya yana share mata hawayen dake zuba daga idonta,kafin yace " ummee na,ki kwantar da hankalinki,dama shi aikin alheri haka yake,dole saika fuskanci ƙalubale,nasan yallaɓai zaiyi fushinsa na wani lokacin kafin ya sauko,kuma nasan daga yau zai fara bincike akan abinda kika sanar dashi,In Sha Allah muke da nasara ,tunda akan gaskiya muke"tareek ya faɗa cikin yanayin ƙarfafawa mahaifiyar sa gwuiwa.
"In sha Allah tareeƙ ,Allah ya datar damu"nanny ta fada tana share hawayenta.
Ameen yace ,kafin suka ci gaba da tattaunawa akan matsalar.
Kai tsaye ya shiga part din na ammi,ko kula gaisauwar da hadimanta keyi baiyi ba,dan zuciyarsa ba abinda take sai tafarfasa,bai taɓa tsammanin haka daga su nanny ba,lallai mutum bashi da tabbas.
Afalo ya ci karo da sarauniya suhaimat,tana zaune da yaranta,suna cin apple da ya'yan itaceya ,gefe guda kuma suna kallo.
Da gudu su zayyad suka taso suka rungume Adeeb suna murnar ganinsa,kansu kawai ya shafa tare da rungumarsu,shima.
Kallonsa sarauniya suhaimat keyi,dan kuwa taga tarin damuwa cikin idanunsa.
"Sannu yarima ,ya jikin naka?dana yarinyar ?"sarauniya suhaimat ta fada cikin yanayi na nuna damuwa .
Lumshe ido Adeeb yayi cikin damuwa da yanayinsa na rashin son magana yace "da sauƙi" atakaice .
"Allah ya bata lafiya " ta fada da yanayi na damuwa.
"Ameen" Adeeb ya faɗa ahankali.
"Ammin naka tana ciki"sarauniya suhaimat ta fada cikin kulawa.
Kai kawai Adeeb ya jinjina mata kafin ya wuce zuwa cikin dakin.
" Bangane ba ?kamar ya nayi sakacin da kwalbar ta fashe,bayan irin kulawa da ita da nake?kasan irin kuɗin dana kashe akan akwatin da aka ƙera na sanya kwalbar ciki?
Shiru tayi ,da alama tana sauraron abinda ake faɗane daga can bangaren.
"Shikenan ,yanzu muna cikin alhini ne na wannan abun daya faru,dan haka kajira nan da kwana biyu,zan nemeka,dan awannan karon aiki nakeso ayimin na ban mamaki,bana kuma son asami matsala " ammi ta faɗa cikin wani yanayi mai nuna ta shirya mugunta mai zafi cikin ranta.
Gaban Adeeb ne yayi wata irin faɗuwa da har saida ya dafe ƙirjinsa,wane akwati ammi ke magana akai?wace kwalbar ce ta fashe?da wa ammi ke waya?waɗan nan sune tambayoyin da Adeeb ke yiwa kansa,saidai bashi da amsar ko daya daga ciki.
Ganin ammin ta gama wayar kuma tana ƙoƙarin juyowa ne ,dan ta ba ƙofa baya,yasa Adeeb saurin saita kansa yayi sallama tare da shiga.
Da sauri aɗan razane ammi ta juyo tana kallon Adeeb ɗin,dan batayi tsammanin ganinsa yanzu ba, saidai da alama baiji me take faɗi ba,itafa wllh tsoronsa ma ta fara ji yanzu,amma saita maze ta saki murmushi,tare da miƙa masa hannu,alamun ya ƙaraso gareta.
Ahankali Adeeb ke takawa har yaje bakin gadon ya zauna,dan jikinsa sam ba kwari,murmushin ƙarfin hali yayiwa ammi yana kallon fuskarta,
"Habeebee ya jikinka? na tsorata sosai da yanayin dana ganka ɗazu"ammi ta faɗa tana mai janyo Adeeb zuwa jikinta.
Sam yau Adeeb ji yayi baya wani jin dadin kwanciya akan cinyarta,Dan saiyajisa kamar akan ƙaya, dan haka da sauri ya tashi daga kwanciyar da yayi,kafin ya dan saki murmushi,yana mai cewa"ƙalau nake ammi,kada ki damu,ya naki jikin?"ya faɗa sam fuskarsa ba walwala.
"Shafa kansa tayi kafin tace naji sauki dana karka damu"ta faɗa tana kallon fuskarsa ,dan kuwa sam ba haka yake mataba,yau kam ba wannan shaukin da yake nuna mata idan suna tare.
Mikewa yayi yana mai faɗin ammi zanje in duba yarinyar can zan dawo anjima" yana faɗin haka yayi waje abinsa.
"Yawwa yarima ,ina son in duba yarinyar nan "sarauniya suhaimat ta fada tana mikewa lokacin da Adeeb ya zo zai wuce.
Shiru yayi yana ɗan nazari,akwai bukatar ta duba ta ,tunda likita ce itama ,kuma fannin mata ta karanta.
Dan haka yace "ok muje ,tana part ɗina"
Ficewa sukayi tare suka nufi part din Adeeb.
Toh masu karatu ,mubi su Adeeb dan duba Hulwa.
Sai mun hade next page.
Mrs babi ce 💘💘
Share and comment fisabilillah.
More comment
More typing.m
[30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄
MACIJI NE 🪱🪱🪱
Na mammy kabeer
(Anty mammy)
Elegant online writers📚📚
Free book
Page 57/58
________________Gimbiya suhaimat ta gama tsara cewa data huta zataje part ɗin Adeeb dan ganin yarinyar nan,
Saidai shigarta part ɗin ammi da yanayin da taga ammin yasa ta saurin,ƙarasawa cikin dakin ,cikin damuwa take faɗin"ukktee meke damunki? Yana ganki akwance?gimbiya suhaimat ta faɗa tana kamo hannun ammi ,wanda ba'a daura mata ruwa ajikinsa ba.
Ahankali ammi wacce tayi nisa cikin tunani ta buɗe idonta tana kallon gimbiya suhaimat,kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ta buɗe" ke dai bari suhaimat,yau naga abinda ban taba gani ba arayuwata,nan ta bata labarin abinda ya faru,saidai ta boye mata asalin labarin fattu,sai cewa tayi wata baiwa ce Rashad ɗin yayiwa fyade,dan ita atunanninta Rashad yayiwa fattu fyaɗen.
Sosai gimbiya suhaimat ta tausayawa yarinyar,sannan tayi Allah wadai da halin Rashad,zuciyarta na tsananin bugawa ,har cikin ranta take jin tausayin yarinya.kuma tayi alwashin ,saitaje taga yarinyar nan kafin ta bar ƙasar.
Rashad kuwa kai tsaye aka wuce dashi,lafiyayyen asibitin dake masarautar,emergency akayi dashi,cikin gaggawa likitoci suka duƙufa akansa dan ceto rayuwarsa.
Dan da dama cikin likitocin , sunyi tunanin hatsari ya samu mai muni.
Karon farko ruwa suka fara ɗauka masa,kafin suka fara bincikarsa,karayama kusan biyar ce ajikinsa, bayan munanan raunuka dake jikin sa,sannan since kansa ya bugu ,dole sai sunyi bincike akwakwalwarsa, dan tabbatar da lafiyarta.
Amma kuka take sosai cike da tarin damuwa da baƙin ciki ,meyasa Rashad zaiyi mata haka?me yasa gaba ɗaya halayyar Rashad ta sauya ne?da ɗan ta mai hankaline da nutsuwa ,sannan yana bin maganarta,amma daga baya ya fandare ya zama gagararre,yanzu ga irin abinda ya jama kansa.karaya har biyar ajikin mutum.Nan dai taci kukanta ta ƙoshi,tana zaune gefen ɗan ta.
Nanny ma ta farfaɗo ,hankalinta amatukar tashe ,tana zaune hawaye na zuba cikin idanunta,yayin da tareeƙ ke rarrashinta cikin kwantar da murya.
"Kayya tareeƙ abinnan na magajin faɗa,ya isheni yaron nan tun yana ƙuruciya yake haɗuwa da tuggun maƙiya,har zuwa girmansa,yaushe ne zai sami salama shima,kadufa wai Adeeb ne ya zama wannan ƙaton macijin,wanda idan awani gurin ka ganshi,sai inda ƙarfi ka ya ƙare wajen ceto rayuwarka.
Yanzu idan haka ta faru dashi awani gurin yunkurin kasheshi fa zasu yi"nanny ta ƙarasa cikin kuka tana fyace majina.
Hannunta tareeƙ ya kara damƙewa cikin nashi,kafin yace " wai ummeee yaushe zasu sanar da gaskiyar da muka jima da sanine?yaushe zamu taimakawa yallaɓai mu haska masa hanya danya gane irin haɗari dake bibiyarsa arayuwa?na gaji da boye gaskiya ummeee kiyi wani abu"tareeƙ ya faɗa cikin damuwa.
"Tareeƙ baka san masarautar ya take ba,idan baka iya kama ɓarawoba ,to shi zai kama ka,dole mubi komai asannu,akwai lokacin bayyana gaskiya kaji?kayi hakuri"nanny ta faɗa tana mai shafa kan ɗan nata.
Yanzu ya jikin ɗiyata yake ?shikenan yanzu yaron nan ya lalata nata rayuwa?ya karbi budurcinta awulaƙance sannan tana cikin al'ada ?kai ban taba ganin fajiri irin Rashad ba,Allah ya saka miki ɗiyata"nanny ta faɗa cikin kuka sosai,tana tausayawa fattu.
Tareeƙ ma runtse ido yayi zuciyarsa na masa zafi,dan kuwa yasan ahalin yanzu Adeeb yana can cikin bakin ciki da damuwa,saidai shikam yana ganin kamar Rashad ɗin bai sami damar yiwa fattu fyaɗen ba suka karaso, yana kuma fatan Allah yasa hasashensa yazama gaskiya.
Akan gado Adeeb ya shimfida fattu,wacce ke kwance kamar gawa,bata ko motsi,gaba ɗaya jini ya wanke mata fuska,jikinta ko ina raunine ,dan kuwa ba ƙaramin azaba Rashad ya gana mata ba,lips ɗin ta sun bushe idanunta ya kumbura sosai.
Runtse ido Adeeb yayi lokacin da idanunsa suka sauka kan wuyanta zuwa ƙirjinta ,fasassun kwalabe duk sun soketa, zama yayi abakin gadon,cikin wata irin karaya da zafin zuciya.ji yake kamar yaje ya kama Rashad yayi gutsin-gutsin dashi,
Hannunta ya kama na dama ,ya riƙe cikin nashi,gam-gam .jikinsa sai rawa yake ,yama kasa aikata komai akanta.wai hulwarsace kwance agabansa kamar gawa.
"Why Rashad ?why ?duk matan dake cikin fadar nan sai matata?me yasa zaka aikata haka agareni?Adeeb ya faɗa afili yana mai kaiwa bango naushi, ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta.
Da sauri ya mike tare da ɗauko first aid box ɗinsa, dan Adeeb cikakken likitane akan fannin lafiya yayi karatunsa .
Farar vest ɗin fattu data yage kaɗan daga sama ya kama,wacce ta rine da jini, ya cire mata ahankali,nan da nan albarkatun ƙirjinta suka bayyana,cikin faduwar gaba Adeeb ya kawar da kansa ga barin kallonsu,zuciyarsa na ci gaba da bugawa. haka ma ya zare wannan dogon wando dake jikinta ya ajiye gefe,ya rage daga ita sai pant Wanda shima gaba ɗaya yayi stairs saboda yadda jini ya ɓalle mata ,tsabar yadda ta shiga ruɗu da razani.
Hannun Adeeb karkarwa yake ya kasa aikata komai,dan haka cikin sauri ya janyo ƙaton bargonsa ya lulluɓe fattu dashi,iya saman ƙirjinta zuwa kanta ya bari abuɗe.
Sosai ya tausayawa fattu lokacin da yake cire mata kwalaben nan,dan kuwa taji ciwo da yawa,ko yaya ya taba gurin da kwalbar take saita zabura kamar zata farfaɗo.
Haka dai ya gama cire mata kwalaben nan,tas yayi mata dressing ɗin duk inda ya kamata, ya sami ruwan zafi da towel ya goge mata jikinta .sai dai kuma ba wani kayan da pant da kuma pad ɗin dazai canja mata.
Dan haka rigarsa ya ɗauko fara ƙal ,doguwar ya zura mata, kafin ya dauko mata kayanta,dan kuwa yana tunanin ta dawo nan part ɗinsa da zama kenan. Ƙarin Ruwa ya sanya mata ,kafin ya nufi ƙofa, kai tsaye ya kulle ƙofar ya fita zuciyarsa kamar wuta haka yake jinsa,ya nufi part ɗin nanny.
"Tareeƙ na roƙeka kada kace zaka sanar da magajin faɗa komai ahalin yanzu,dan kuwa bamu da kwararan hujjoji akan hakan ,ka bari nan da lokaci kankanin shida kansa zai gano komai,zamu nuna masa hanya ta yadda zai fahimci abubuwa da dama" nanny ta faɗa tana rike da hannun tareeeƙ.
Umme wllh zuciyata zafi take,Aduk lokacin dana ga yallaɓai cikin wani halin,yana zagaye da maƙiya ,amma bai sani ba,shi yana zaune dasu zuciya ɗaya ....
"Su waye maƙiyan nawa?sannan wace gaskiyar ce ake boyemin?"
Suka tsinkayo Muryar Adeeb yana faɗin haka cikin sautin da ba wasa acikinsa.
Da sauri suka juyo gaba ɗayansu, dan basu tsammanci ganin Adeeb ɗin awannan lokacin ba.
"Magajin faɗa yaushe ka shigo?ya jikin naka?ina ɗiyata take ?"nanny ta faɗa cikin inda-inda da son n kawar da zancen.
Ƙura mata ido Adeeb yayi cike da tuhuma ,gaba ɗaya ta daburce.da alama akwai abunda take boyewa ita da tareeƙ .kallonsa ya dawo dashi kan tareeƙ wanda kansa ke ƙasa ,shi yaji dadin jinsu da Adeeb yayi,fatansa ɗaya ayi komai yau akare.
"Tareeƙ, what wrong me kuke ɓoyemin? Dama akwai Abinda zaka iya boyemin tareeƙ ?na dauke tamkar kanina da muka fito ciki daya,why tareeƙ?" Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ.
Kallon nanny tareeƙ yayi,yana jin ba dadi cikin ransa,dama yasan watarana hakan zata iya faruwa,shi baiga amfanin biye boyen ba , amma suna haɗa ido da nanny tayi saurin girgiza masa kai,alamun karya ce komai.
"Tareeeƙ,am tolking to you me kuke hidden mini?kada kusa na fara zarginku fa,Please nanny,bayan ammina da abie, ku kadaine mutanen dana yarda dasu arayuwata,ku kaɗai ne waɗanda nake ganin bazasu taba cutar dani ba,karki karyamin zuciya nanny, Please me kuke ɓoyemin?" Adeeb ya faɗa cikin wata kalar murya mai cike da tsoron kar ace nanny da tareeƙ suma suna daga cikin maƙiyansa .
"Ka kwantar da hankalinka magajin faɗa,wllh har abada bazamu taba cutar da rayuwarka ba,saidai mu bata kariya, amma kasani akwai mutanen da kake kallo matsayin maƙiyanka,saidai sam,ba haka abin yake ba. azahiri kake ganinsu matsayin maƙiya,amma abaɗini sune masoyanka na haƙika.
Su kuma wadanda kake kallo matsayin masoya,suke son ganin bayanka, sune waɗanda suke cin dunduniyarka,Adeeb ka kula kazamo mai lura da mutanen da kake tare dasu " nanny ta faɗa tana mai riƙe da hannun Adeeb,fuskarta ɗauke da damuwa.
Kallonta kawai Adeeb keyi,tunda ta fara maganarta ,me take nufi kenan?su waye ya yarda dasu ,kuma suke cin dunduniyarsa?
Sannan suwaye yake wa kallon maƙiya ,alhalin sune masoyansa na asali?kallon nanny yayi cike da tarin tambayoyi zuciyarsa na harbawa da gudu.
"Nanny ban fahimceki ba,me kike nufi da kalamanki? Please kiyimin bayanin da zan gane"Adeeb ya faɗa yana kallon nanny,idanunsa sun kada sunyi jajur dasu.
Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe mai ƙarfin gaske,sannan tace magajin faɗa ,idan baka manta ba,shekaru kusan sha takwas mijina da kuma gimbiya nazli sunyi haɗari suka mutu,sanadiyyar wuta data kama motar da suke ciki,harda yaranta mata su biyu,nanny ta faɗa tana kallon Adeeb,
Runtse ido Adeeb yayi da mugun ƙarfi,har abada bazai taba mantawa da wannan baƙar rana ba ,ranar data zamo mafi muni arayuwarsa.
Bude idonsa yayi wanda suka cika da kwalla yana kallon nanny kafin cikin rawar murya yace " tabbas nanny bazan taɓa mantawa da wannan rana ba,domin itace rana mafi muni arayuwata" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa hawaye suka ziraro sharrrt.
"To kasani wannan haɗarin ba afkuwa yayi ba ,shiryashi akayi" nanny ta faɗa tana mai kallon Adeeb ,
Azabure Adeeb ya bude idanunsa,da suka gama zama jajur dasu,kallon nanny yake cikin kiɗima da ruɗewa" nanny kamar ya ban gane ba,me kike nufi da shiryashi akayi?waye ya shirya?kuma meye dalilin shiryawa?"Adeeb ya faɗa aruɗe.
Kamo hannunsa nanny tayi ta zaunar dashi akan kujera dan kuwa gaba ɗaya jikin sa rawa yake.
"Tareeƙ maza jeka kulle mana ƙofar nan"nanny ta faɗa cikin damuwa.
Ahankali tareeƙ ya nufi ƙofar tare da kullewa, yana jin sanyi aransa,koba komai yau zasu sauke nauyin da yayi musu bake bake acikin zuciya.
" Nanny kiyi saurin sanar dani, domin zuciyata gab,take da tarwatsewa,dan kaɗuwa" Adeeb ya faɗa cikin tsantsar zaƙuwa .
Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace " ina son ka saurari maganata da kunnen basira