Showing 21001 words to 24000 words out of 37653 words

Chapter 8 - MIJI GOMA. Hausa novel

23 Oct 2025

82

siya ba, babu rigar da za a tafi da ita asibiti, sai na zuba masa ido?"

Uwani ta ce"Kayyasa! Amma wannan yaron akwai mara kirki, kodayake laifinki ne ɓa wallahi, ni na rasa irin son da kike yi masa ba".

Maryam ta ce"Ta ya zai zama laifina?"

Ta ce"To akan me ba za ki yi masa kaca-kaca ba? Wannan wane wulaƙanci ne a ce ciki har ya shiga watan haihuwa ba a sayi komai ba? Haihuwar fari fa za ki yi Maryam, ko so kike mutane su samu abun faɗa a kanki? Wallahi da ki haihu ya zo ya ja mana abun kunya, gara ma mu san auren ya mutu wannan an san dama ba mijinki ba ne, ke ba ki ga Murja ba haihuwar fari yadda ta dinga tatso kuɗi a jikin mijinta hatta yajin da na yi mata da kuɗinta ne, to ba ki Murja komai ba? Shi kenan ki yi ta zama da wannan ƙaddararren auren".

Maryam ta ce"Ai shiyasa na ce ba zan taho ba sai ya zo".

Uwani ta ce"Ki miƙe tsaye ki tada masa da hankali kar ki yarda ki dawo gida haka hannu na dukan cinya".

Ta ce"To bari ya dawo".

Suka yi sallama, kalaman Uwani sun ƙara tunzurata don haka ta cika ta yi fam tana jiran dawowar shi, ƙarfe tara ya dawo unguwar, ya biya ta gidansu don ya karɓi mukullin gidansa, Umma ta ce"Wane irin mukulli kuma? Ina Maryam ɗin ta tafi?"

Ya ce"Au ba ta kawo mukulli ba? Gida ta tafi ai, kin ga ta yi nauyi idan ta haihu ta yi arba'in sai ta dawo".

Umma ta ce"Ikon Allah! Ku mazan zamani da ba kwa yarda mace ta tafi goyon ciki? Hamza anya kuwa? Kuma da sai ta tafi haka ko sanar da ni ba za ka yi ba?"

Ya ce"To ai ga shi yanzu kin ji, kuma goyon ciki ai ba komai ba ne".

Ta ce"Amma ni dai da ta haihu a ɗakinta, idan aka yi suna sai ta koma gidan".

Ya ce"A'a ta je ɗin kawai babu komai".

Ta ce"To Allah Ya sauketa lafiya".

Ya yi mata sallama ya fita. A ƙofar gida ya tsaya ya kira lambar Maryam,har ta fara bacci ma, ta ɗaga cikin muryar bacci, ya ce"Mayam kina ina?"

Ta ce"Ina gida mana".

Ya ce"Wane gidan?"

Ta ce"Gidanka mana".

Ya ce"To me ya hana ki tafiya?"

Kawai sai ta yi tsaki ta kashe wayar, ta tashi ta je ta cire sakatar ƙofar ta dawo ta kwanta.

Babu jimawa ya shigo gidan, ya same ta a ɗakin ya ce"Wai ni me ya sa ba ki tafi ba?"

Ta yi kamar ba ta ji shi ba, tana jin takaici wai ita miji yake nunawa yana son ta yi nesa da shi ƙiri-ƙiri babu sakayawa.

Ya ce"Magana fa nake yi miki".

Ta tashi a fusace ta ce"Hamza idan ka yi haƙuri zan bar maka gidanka har abada, amma sai na haihu, kuma dalilin ƙin tafiyata ai na faɗa maka sai ka yi mini siyayya, sannan ka sayi kayan jarirai".

Ya ce"Amma ai ce miki na yi zan aiko ko?"

Ta ce"Don ka yi magana dole ne na amince? Idan ji ya zama dole ai babu inda yarda take zama dole".

Ta juya ta kwanata.

Ya fice daga ɗakin yana tsaki.

Da ya ga dai har ta ƙara kwana uku ba ta da niyyar tafiyar, sai ya same ta suka zauna ya ce"Wai me da me kike buƙata?"

Ta ce"Za ka siyo kayan shayi na gwangwani fa ba irin wanda kake kawo mini ba, sannanza ka siyo kwalin indomi, da golden morn, sannan kayan jariran wanda mace da namiji za su iya sakawa kala uku, ka ga kenan shida za ka siya tun da su biyu ne".

Kalmar biyun nan ta saka gabansa faɗuwa, saboda har yanzu kuɗin abun yanka ma ɗaya ya tanada, shi ma lissafinsa tunkiya zai siya haka ƴar madaidaiciya.

Ta ci gaba"Ka ga za ka siyo tawul masu kyau kowa biyu, sai saitin kayan sanyi da saitin man shafawarsu, wannan su za ka siya kafin na haihu, idan na haihu aka ga me aka samu sai a san yadda za a haɗa kayan barka".

Ya ce"Wannan lissafin nawa ya kama?"

Ta ce"Oho! Ka ba da dubu ɗari sai a je a ji".

Ya yi mata wani mugun kallo mai ɗauke da manufar ba ki da hankali, ya ce"Dubu ɗari?"

Ta ce"To ka je ka siyo mana".

Ya tashi ya fice, a ranar ya siyo komai da ta lissafa, amma duk masu sauƙin kuɗi ya zaɓo, ya kawo mata ya lallaɓata ta tafi.

Uwani da ta ga kayan ta rafka tagumi har sai da Maryam ta tsargu, kafin ta ce"Maryam wane irin miji ne wannan da kike son rayuwa da shi? Wannan kayan tsohon ya yi masu mugun arha ya siyowa ƴaƴansa na fari? To sai dai mu ce Allah Ya kyauta".

Maryam dai ba ta ce komai ba.

Daga nan kuma sai Uwani ta tsiri saka ta ta cewa Hamza ya siyo mata nama, ko kayan marmari haka, idan ta kira shi ta faɗa masa sai ya fara masifa yana cewa shi fa ba shi da kuɗi, wataran zai kawo, wataran kuma ya ƙi kawowa, Uwani kuwa ta samu abun mita, ta yi ta masifa tana tsinewa auren, a haka dai har aka cika sati biyu, ranar tsakar dare Maryam ta fara naƙuda, Baba ya ce ga maƙotansu wani matashi yana da adaidaita sahu a kira shi su tafi asibitin, amma fir ta ƙi ta dinga kiran Hamza a waya, shi kuwa yana ganin kiran jikinsa ya ba shi ba lafiya ba, ya san dai ƙarshen zance cewa za a yi Maryam za ta haihu ko kuma ta haihu, don haka ya ƙi ɗagawa, sai ma ya saka wayar a silent ya ci gaba da baccinsa, dole dai aka bi maganar Baba, suka tafi asibitin a hanya tana ta zagin Hamza Baba yana kwaɓarta.

Sai da asuba Maryam ta haihu, ƴaƴanta mace da namiji, sai dai macen ta zo babu rai, sai namijin ga shi nan ma sha Allah, sai da gari ya waye ta kira lambar babar Hamza ta bawa Uwani, ta faɗa mata an sauka lafiya, ta ce"Ki sake kiran shi shi ma".

Uwani ta ce"Kin san kira nawa na yi masa jiya? Yanzu da ya tashi sallah ai zai ga miss call idan shi mutumin kirki ne ai sai ya kira!".

Bakwai da rabi Hamza ya zo asibitin tare da babar shi, suka kawo musu abun karyawa, a gaban babar shi Uwani ta caccake masa tass na rashin ɗaga wayar, ita kuma tana ta ba ta haƙuri, aka tafi da gawar yarinyar aka binne, sai da yamma aka sallami Maryam ta koma gida.

Sun ga tijara kafin ranar suna ta zo, don yanzu Uwani karɓar lambar shi ta yi, abu kaɗan ta kira shi ta ce ana buƙatar abu kaza, ranar da bai kawo ba ta yi ta tsine masa ƴaƴanta suna yi mata nasiha, amma kamar suna zugata.

Ranar sunan ma sai da ta raina abun yankan, kayan fitar suna ma kala ɗaya ya yi mata, wata atamfa ce aka sako ta a cikin kayan barka, don haka ita Maryam a ranta ta ƙudure wannan zuwa gidan da ta yi, ta zo kenan babu zancen komawa, don wannan idan ta ci gaba da zama da shi gorin Uwani ma kawai ya ishe ta.



08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_



*SADIYA ABDULRAZAƘ*


*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*

Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu

*FIRST CLASS WRITERS*

PAGE 10


https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee


Hamza sai ya bushi iskarsa yake leƙowa gidan har aka yi arba'in ɗin Al'ameen, ga wani raini da ya yiwa Uwani, saboda yawan roƙon shi da take yi, da yadda take raina ƙoƙarin shi, har wani kallon gani-gani yake yi mata idan ya je gidan. Uwani tana sane ta ce Maryam arba'in biyu za ta yi, saboda ta dinga ja masa rai har ya gaji auren ya sire masa, ba ta san kamar an zuga zugagge ba ne, don shi ma ba son ci gaba da zaman yake yi ba, Baba da ya yunƙuro a kan sai ta koma ɗakinta Uwani ta sanar masa ba ta da lafiya fa, ɗinkin da aka yi mata sanadin haihuwar nan bai warke ba, kuma likitocin sun yi gargaɗi da kakkaurar murya a kan kar ta koma sai bayan wata uku, su kuwa yaran zamani masu do a tsakar ka idan ta koma sai dai komai ya faru, don haka Baban ya ƙyale su ya zuba ido.

Watanta biyu a gida Hamza ya zo da daddare, sun gaisa yake cewa"Maryam yaushe za ki koma ne? Sannan ina ga fa sai dai ki koma gidanmu da zama..."

Ta katse shi da faɗin"Ban gane ba!".

Ya ce"Ai ganar da ke nake yi".

Ya ce"Kin ga dama kuɗin hayar ya ƙare, kuma ni ba ni da kuɗin da zan sake biya, sannan ma ina son tafiya wata ƙasar neman kuɗi, ana kan yi mini hanya, kuma ko ba wannan ba ni dama fa a zamanmu haƙuri kawai nake yi da ke, saboda tsakani da Allah ba ki da kunya, ba ki da tarbiyya ba ki san girmana ba a matsayina na mijinki".

Maryam ta yi mamaki sosai, don ko da wasa ba ta taɓa tunanin gidan nan ba na shi ba ne, sanda yana neman aurenta ya ce mata na shi ne ya gina tun da jimawa sai ya saka ƴan haya a ciki, yanzu ya tashe su tun da ya yi aure, ta ce"Hamza idan za ka kore ni ba sai ka yi mini ƙarya da gida ba naka ba ne, idan ka yi haƙuri dama ni ma wannan zaman da nake yi ba ni da niyyar komawa, saboda haka ka sallame ni kafin ka tafi inda za ka je".

Ya ce"Wallahi ba gidana ba ne, ki tambaya ki ji, kuma sannan ni fa ba ni da manufar rabuwa da ke, sai dai idan ke ce kika zaɓi hakan".

Ta ce"E ni ce na zaɓa ɗin, ka sake ni".

Ya ce"To gobe zan aiko miki saƙo".

Ya tashi ya fice, a tsakar gida ya samu Uwani zaune, ta ce"Ka fito?"

Ko kallonta bai yi ba ya yi dogon tsaki ya fice.

Ta shiga ɗakin dafe da ƙirji tana cewa"Na shiga uku ni Uwani, Maryam me zan gani? Mijinki ne yau ya yi mini tsaki, a gobe kuma sai duka, wallahi saura zagi da duka, Maryam wa kika kwaso mana ne haka?"

Jin shigowar saƙo wayarta ya sa ba ta kula Uwani ba, tana dubawa ta ga daga shi ne, ya rubuto mata ya sake ta saki ɗaya, ta nunawa Uwani wayar ba ta ce komai ba, ta ce"To rubutu nake gani, kuma kin san ni ba iya karatu na yi ba, na mene ne?"

Ta ce"Shi ne ya turo mini saƙo wai ya sake ni saki ɗaya".

Uwani ta sauke ajiyar zuciya ta ce"To Alhamdulillah! Tsaki da ya yi mini kuma ya je don kansa, tun da dai ya sallame ki ni ya biya ni!"

Ta zauna tana cewa"Maryam ki kwantar da hankalinki, wannan ba komai ba ne, in sha Allah nan gaba za ki samu miji na kere sa'a, wanda za mu yi alfahari da aurenki".

Maryam ta ce"Allah Ya sa".

Bayan kwana uku da sakin sai ga babar shi ta zo gidan, Uwani ta yi kicin-kicin ta tarbe ta a tsiyace, saboda kar ma ta yi zancen kome, irin yadda take amsa mata gaisuwa a daƙile kamar mai gyambo a maƙoshi har Maryam ɗin sai da ta ji babu daɗi, saboda ta zauna da matar lafiya ba ta da wata matsala, babar Hamza ta ce"Ashe haka abu ya faru, ɗan yau dai ka haife shi ba ka haifi halinsa ba, wallahi Hamza bai yi shawara da ni ba ya yanke hukunci, don Allah ku yi haƙuri".

Uwani ta ce"Ai ba komai ba ne a wajenmu, duk wanda ya rasa Maryam shi ke da asara, don haka shi za ki bawa haƙuri".

Ta ce"Ai kuwa ba a ce ba komai ba ne, aure irin wannan da albarkarsa har an fara samun rabo..."

Uwani ta katse ta da faɗin"Cewa za ki yi har an samu rabo, idan kika ce an fara da saura kenan za a ci gaba, kin ga mun gode amma don girman Allah ki ƙyale yaron nan sa hukunci shi, don ba a yi wa yaran zamani dole".

Ta ce"Haka ne, to Allah Ya rufa asiri".

Uwani ta gyara zama ta ce"Dama ai jira nake a cika sati na ga ƙarshen abun, da ba ki zo ba dama zan zo".

Babar Hamza ta ce"To lafiya dai ko?"

Uwani ta ce"Ƙalau, dama a kan wannan yaron ne, na ce ya za a yi da shi? Za ki karɓa ne ko kuwa biya za ku dinga yi tana shayar muku da shi?"

Ta ce"A haba dai ga uwarsa a raye ai bai kamata a raba shi da nonon uwa ba, sai a dinga ba ta wani abun".

Ta ce"To nawa za ku na badawa? Kin ga bayan shayarwa ma a kwai omo, sabulu, famfas kafin kuma ya fara cin abinci".

Maryam da duk matar ta ba ta tausayi ta ce"To babarmu ai ba sai an wani tsadance ba, ko me suka kawo Allah Ya saka masa albarka, ni ma fa ɗana ne".

Uwani ta galla mata harara, ita dai ta yi musu sallama ta tafi, ta ce gobe za ta dawo idan suka yi magana da Hamza.

Tun daga nan duk sati biyu sai babar Hamza ta zo ta gansu, wataran kuma ta tiso shi a gaba su zo tare, su ba su kuɗin shayarwa. Babu laifi Maryam ta samu kulawa sosai a wajen Uwani, yanzu hankalinta a kwance yake tana ra rainon ɗanta da yake ta ƙara girma da wayo. Al'amin yana da wata biyar ta ce za ta fara bussiness da kuɗin da ta siyar da kayan ɗakinta, Uwani ta so daƙile ta, ta nuna mata wannan fa duk cake ne ba samun ciniki ake ba, har gara ma siyar da abincin, ita kuma Maryam ta ga ya za a yi ta sana'ar abinci da ƙaramin ɗa, to da yake Uwanin ta san idan Maryam ɗin ta coge ba a iya ture ta sai ta rabu da ita, ita take zuwa kasuwa da kanta tana yo sarin abubuwa iri-iri, ta tallata a maƙota da kuma status kuma Alhamdulillah Allah sai Ya sakawa abun albarka, Uwani tana kallo take ƙirga ribarta tana adanawa.

Da ta yaye Al'amin sai ta daina zuwa kasuwar da shi, ta fara ɗaukar wanka don shirin fara zawarci, ai kuwa zawarawan suka fara layi, tana ta cafke musu ƴan canji,domin ta koyi roƙo sosai, idan ma kai faƙiri ne ko marowaci soyayyarku da Maryam ba ta taɓa yin ƙarko, bani-bani ne zai kore ka, idan gari ya waye dare ya yi ba su ci kaza ko balangu ba ita da Uwani to sai dai idan ita ce ba ta so ba, ma'ana idan ba ta bawa kowa damar zuwa ba, amma muddin ka ce ga ka nan tafe to za ta lissafo maka abin da za ka taho da shi, ai kuwa har wata ƙiba ta fara yi, ta yi kyau abunta.

Ba ta tsayar da mijin ba, tana ta tantancewa dai, yayin da ƴan'uwanta ƴaƴan Uwani suke yawan yi mata nasiha kan auren shi ne rufin asirinta, idan a gaban Uwani ne kuwa nan za ta hayayyaƙo tana cewa su ba su san ƙaddara ba? Ai ita Maryam ƙaddararta kenan, shi ma Baba ya fara matsa mata, don haka ta tsayar da wani Nasuru, a kasuwa suka haɗu, ya faɗa mata ya taɓa yin aure ƴaƴansa biyu suka rabu da matar, Nasuru ba shi da rowa, sosai yake sakar mata kuɗi, kuma ba shi da wata makusa a halitta, ta ji tana son shi za ta iya auren shi, don haka ta ba shi dama ya turo bayan ta gama shirinta.

A wannan karon wata biyu aka saka, aka ɗaura aure, aka mayar da Al'amin wajen babar Hamza ta ci gaba da kula da shi, a wannan karon Uwani ta san babu buƙatar yiwa ƴar tata wata huɗuba domin ta riga ta haddace karatunta, musamman ma a wannan zawarcin da ta yi ta ƙara samun gogewa ta rayuwa, don haka hankalinta kwance yake, ta san yadda ta tafi haka za ta dawo.

An kai amarya lafiya, zamansu da Nasuru lafiya ƙalau babu wata matsala daga farko, haka kuma shi yana son haihuwa ba kamar Hamza ba, don da ta samu ciki ya nuna mata kulawa sosai, bai taɓa nuna ƙosawa da yanayin laulayinta ba. Yaran shi suna zuwa gidan, wani lokacin ma har su kwana biyu idan sun zo ranar Juma'a sai ya mayar da su ranar Asabar, a yadda ta lura da alamunsa yana son yaran su zauna a wajenta, ita ma kuma ba ta ɗauki hakan a komai ba, tun da ba ƙananu ba ne sosai ballantana ta ce za ta ci kashinsu da fitsari, babban shekararaa tara, sai ƙanwarsa shekararta baƙwai, to da yake komai na gidan aurenta a tafin hannun Uwani yake ita ce ta nuna mata sam kar ta sake ta riƙe masa ƴaƴa, ɗan kishiya ruƙon mai haƙuri ne, ta zuga ta a kan idan ta haihu tana kallo zai yi ta fifita yaran a kan wanda za ta haifa, saboda an fi marmarin ɗan fari, haka dai ta harhaɗa mata raunana hujjoji marasa tushe bare makama, sai ta hau kai ta zauna ta fara baya-baya da yaran.

Nasuru ɗan kasuwa ne, dole ba zai rabu da mata a waya ba, musamman yanzu da kasuwancin ya koma na online, sannan da daddare ne yake samun damar zama ya nutsu ya duba saƙƙonnin da bai duba ba, sannan ya yi ta saka hotunan kaya a groups ɗin shi, ita kuma Maryam wannan karkata da yake yi a kan waya yana mugun ba ta haushi, ko kuma ta ga wata ta kira shi suna magana, duk da ga shi a zahiri tana ji zancen kaya ake yi, amma sai ta yi ta yi masa tijara tana cewa ƙarya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login