Showing 33001 words to 36000 words out of 37653 words

Chapter 12 - MIJI GOMA. Hausa novel

23 Oct 2025

89

wanda hakan bai ƙara mata komai ba, sai baƙinciki da tsanar Maryam ɗin, ita kuwa Maryam dama ta yi tunanin za a yi hakan, don haka babu wata mace da ta sakarwa fuska, kadaran-kadahan take karɓarsu.

Wajen ƙarfe biyu ta gama girki tana sallah ta ji ana buga gidan, an daɗe ana bugun saboda tana tayar da sallar aka fara, da ta idar ta taho da sauri ta buɗe, sai ta ga yara ne su huɗu da unifom a jikinsu, jikinta ya ba ta ƴaƴan mijinta ne, sai mai adaidaita sahun da ya ajiye su ya ƙaraso da waya a kunnensa yana cewa"Ai ga shi ma ta buɗe".

Don kuwa da ya ga yaran suna ta bugawa ba a buɗe ba, sai ya kira Sauda ya faɗa mata, ta kuwa harzuƙa ta miƙe tsaye tana zage-zage da cewar gidan ubanta ne da za ta hana su shiga?

Ya miƙawa Maryam babbar jakar dake hannun shi yana cewa"Ga shi mamansu ce ta ce na kawo su".

Maryam ta karɓa ta ce"To ka gaishe ta".

Ta kalli yaran ta ce"Ku shiga, sannunku da zuwa".

Babu wanda ya amsa, ballantana su gaishe ta, wannan huɗubar mahaifiyarsu ce, suka shige ɗakin kwanansu, Maryam ta biyo su da jakar kayansu ta ajiye tana cewa"Ku cire unifom, sai na yi muku wanka ku canza kaya ko?"

Momy da take babbar ta ce"A'a, mun yi wanka da safe".

Ta ce"To ku canza kaya ku fito ku ci abinci".

Suka fara kiciniyar cire kayan, ban da Momy da ta ja ta tsaya tana ta ɓata rai, sai da Maryam ta fita sanan ta fito da duka kayan cikin jakar, sai ga waya keypad ta bayyana, ta ɗauka ta shige banɗaki, ta danna ta kira babarsu a waya, Sauda tana ganin kiran ta miƙe ta shige ɗaki, don ko Inna ba ta san da wannan shirin nata ba, tana ɗagawa ta ce"Momy yaya aka yi?"

Momy ta ce"Ta ce mu yi wanka na ce mata mun yi, shi ne ta ce mu fito mu ci abinci".

Sauda ta ce"To ko me ta dafa ku ce ba kwa ci, kowa ya zaɓi abin da yake so ya ci, kin ji ko?"

Ta ce"To, amma wallahi Nana ce uwar kwaɗayi, na san ci za ta yi".

Ta ce"Ki gargaɗe ta, ki ce idan ta ci za ta mutu, ta ce doya take so ta ci, ku kuma ku zaɓi wani abun kowa na shi da ban".

Ta ce"To"

Ta ce"Ki ɓoye wayar nan fa sosai, ki saka a ƙarƙashin katifarku, kuma kar ki fita ko falo da ita".

Ta kashe wayar ta fito ta faki idon ƙannen nata ta ɓoye, sannan ta ba su kayan da za su saka, ta zaunar da su ta ce"To Umma ta ce ko me ta dafa kowa ya ce ba ya ci, ke Nana ki ce doya da ƙwai za ki ci, ke Kausar ki ce shinkafa da wake, ke ke kuma Ummi ki ce shinkafa jollop, idan kuma shinkafar ta dafa sai ki ce macaroni, wallahi Umma ta ce duk wacce ba ta ce haka ba sai ta ci ubanta".

Duk suka gyaɗa kai, sannan suka fito a tare, Maryam tana falo tana chart, ta ce"Kun fito?".

Ba su ce komai ba, ta tashi ta shiga kitchen ta juye musu taliyar da ta dafa da miya, leda ɗaya ce dama ta dafa ko ci ba ta yi ba, plate biyu ta yo ta kawo ta ajiye a gabansu tana cewa"Ku yi maza ku ci".

Daidai lokacin kiran Uwani ya shigo wayarta, ta ɗaga tana gaishe ta, Uwani ta ce"Oh! Maryam har na fara kewa, ya kike ya gidan?"

Ta yi ƴar dariya ta ce"Lafiya ƙalau".

Ta ce"Babu wata matsala dai ko? Kin san zama da kishiya".

Da a da ne sai ta faɗa mata ga shi har yaran shi sun zo, amma yanzu kuwa ta ce mata babu komai, kuma ba ta ma faɗa mata uwar gidan ta yi yaji ba, ko da ƴan kai amarya suka zo ma duk a zatonsu ɗaki ta shiga ta kulle saboda kishi.

Suna gama wayar ta juyo ta ga yaran ba su da niyyar sakkowa su ci abincin, ta ce"A'a! Ya ba ku fara ci ba? Ko sunayenku ba ku faɗa mini ba ma, ku gama ci ku zo mu yi fira ko?"

Momy ta ce"Mu ba ma cin abinci a ƙasa sai a dining, kuma ba ma son taliya".

Ta ce"Ba kwa son taliya? Kwata-kwata ba kwa ci a gidan?"

Ta ce"E".

Maryam ta ce"To me za ku ci?"

Momy ta ce"Ni tuwo nake so".

Ummi ta ce"Ni kuma jollop ɗin shinkafa".

Nana ta ce"Ni doya da ƙwai".

Kausar ta ce"Ni shinkafa da wake, da mai da yaji da salak da tumatur da albasa, da cocomba". Ta ƙarasa da karsashi, don dama Momy kowa abin da ta san ya fi so ta ce ya faɗa.

Maryam ta tsaya kallon su da mamaki, ba sai ta wahalar da kanta da tunani ba, saboda ba zai taɓa yiwuwa ta biyewa yara ta yi girki kashi-kashi ba kamar wata ƴar aiki, girki kala huɗu? Sannan wannan ai ba tarbiyya ba ce yara su dinga zaɓar abincin da za su ci, don haka ta ce"Duk na ji, amma fa sai dai ku zaɓi abu guda ɗaya dukanku, saboda kun ga idan na yi girki har kala huɗu na yi almubazzaranci, don haka ku tsayar da abu ɗaya".

Duk sai suka kalli Momy tun da ita ce shugabar tawaga, ta ce"To ai mu ba ma cin taliya".

Ta ce"Na ni ba za ku ci taliya ba, ku zaɓi kala ɗaya sai na dafa muku".

Ta ce"Sai dai a yi mana tuwon shinkafa miyar agushi".

Maryam ta ce"Ni ba ni da agushi, sannan ba zan takurawa babanku ba yana kasuwa, amma akwai wake, zan yi muku miyar wake".

Da gaske Nana ba ta cin miyar wake, don haka ta taɓe fuska za ta fara kuka ta ce"Ni dai ba zan ci ba".

Kausar ta ce"Nana ba ta cin miyar wake".

Maryam ta ce"Zan dafa mata indomi".

Ta wuce kitchen ɗin, a ranta tana mamakin yadda aka sangarta yaran, ita idan ƴaƴanta ne gaskiya ba za ta saki fuskar da za su yi mata haka ba, amma su ma ɗin muddin a wajenta za su zauna to kuwa tabbas sai ta saita su. Ta ɗora tuwon da yake ta tarar da komai har farar shinkafar da akwai, da yake gas ɗin mai huɗu ne tana wanke waken sai ta ɗora miyar, sannan ta zauna ta ci taliyar.

Tana tafiya kitchen Momy ta tashi ta shige ɗakinsu, ta ɗauki waya ta shiga banɗaki ta kira Ummansu, tana ɗagawa ta zayyane mata komai, Sauda ta ce"Amma dai Allah Ya yi miki albarka Momy, yanzu kin san yadda za a yi?"

Ta ce"A'a".

Ta ce"Idan ta gama tuwon ku yi loma ɗaya ku ce babu daɗi ku ba kwa ci kun ji ko? Ko kun ji daɗi fa kar ku ci".

Momy ta ce"To Umma yunwa muke ji fa".

Ta ce"Idan kun ƙi ci sai ku shiga kitchen ku ɗauki golden morn ku haɗa ku sha, idan ya dawo ku ce masa ba ku ci komai ba yunwa kuke ji, ku ce ba ta ba ku tuwon ba".

Momy ta ce"To". Amma a sanyaye, saboda yunwa take ji.

Sauda ta ce"Ki yi haƙuri kin ji ƙawata, ni na san me zan siya muku".

Ta ce"To".

Ta ajiye wayar, sai da Maryam ta koma kitchen sannan ta sake tsarawa yaran, ta ce inji Umma, ta ce sai sun ƙi ci za ta dawo, ai kuwa suka yarda.

Sai da ta sauke tuwon ta dada indomin saboda ta manta, ta zubo ta kawo musu,lokacin har ƙarfe uku ta gota, ta ajiye ta ɗakkowa Nana indomi, ita kam ana ajiyewa ta fara ci ta manta da gargaɗin yayarsu saboda yunwa take ji, kuma dama duka-duka shekararta huɗu, su kuwa manyan ba su saɓa ba, loma ɗaya kowa ya yi a layi, idan wannan ya ci, sai wannan ya ci, sai suka tsaya suna kallon tv, Maryam ta ce"Ya dai? Ku ci mana".

Momy ta ce"Ni dai ba na ci, na ji babu daɗi, ko Kausar?"

Su ma suka haɗa baki wajen faɗin"E babu daɗi".

Ran Maryam ya ɓaci, lallai sun yi sa'a a wannan karon zama ta zo na mutu-ka-raba, da babu abin da zai hana ta fesawa babbarsu mari, ba ta ce komai ba, ta kwashe ta kai kitchen, babbar ta shige ɗaki, duk suka bi ta, babu jimawa kuma ta fito ta shiga kitchen ɗin Maryam ta bi bayanta, ta tarar tana haɗa golden morn, ta haɗa shi kofi uku ta ƙwala musu kira, suka fito suka ɗauka suka koma ɗaki, ita kuwa Nana sai ta zauna a nan falon tana kallo.

Maryam ta cika da mamakin yaran sosai, ta kuma saka a ranta ta san zaman da za ta yi da su.

Da yamma da ta yi baƙi sai ta ba su taliyar, tuwon kuma ta rufe musu shi, tana jira babansu ya dawo ta sanar masa ta ga matakin da zai ɗauka.


LITTAFIN NAN NA KUƊI NE AKAN NAIRA 500
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay

08028966015

*MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_



*SADIYA ABDULRAZAƘ*


*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*

Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu

*FIRST CLASS WRITERS*

https://chat.whatsapp.com/BuEB69AOiqBKg0PMiBzdG3

PAGE 14


Suna ƙule a ɗakinsu baban nasu ya dawo, Maryam ta tare shi ranta fess, ta haɗa masa ruwan wanka ta kai banɗaki, abin da ba ta taɓa yi wa sauran mazan da ta aura ba, ko ruwa a buta ba ta taɓa zuba musu ba, amma shi wannan da yake zaman gaskiya ta zo ta ɗaura ɗamarar yi masa hidima iyakar iyawarta, tsaf ta taya shi shiryawa bayan ya fito, sannan ta ja hannunsa kamar wani ɗanta zuwa falo, ta kawo masa tuwon, tana ba shi a baki suna ta firarsu cike da nishaɗi, har ya yi mamakinta saboda shi kansa ya san kafin auren ba wani son shi take sosai ba, kiran sallar magriba ne ya tashe shi, ya yi alwala ya tafi masallaci yana jin shi fess da shi, ya manta rabon da ya samu kulawa da soyayya irin wannan, sautari sai bayan magriba yake yin wanka saboda sai ya ce Sauda ta dafa ruwan take dafawa, wataran ma a haka yake kwanciya ko ya yi da na sanyi, sannan Momy ce mai kai masa abinci dining, idan ma ya shiga ɗakinsa yana wani aikin ko kuma ya shigo da wata damuwar, babu ruwan Sauda da zuwa ta ji dalilin ƙin fitowarsa, sai dai ta aiko masa da abincin ɗakin nasa, sannan babu ruwanta da tambayar shi fita unguwa, indai ka ga ta tambaye shi sai dai idan nesa sosai za ta je, gidan Inna kuwa idan za ta je tun rana idan ta tafi sai dare idan ya je yi mata sai da safe su taho tare, babu ruwanta da me zai ci ranar, babu dai wata kulawa akwai matsaloli birjik, wanda shi ne dalilinsa na son ƙara auren, kuma tun yau ya fara tunanin za a samu canji in sha Allah!

Ya dawo daga masallaci Maryam ta ga bai yi maganar yaran ba, ta dai leƙa bayan fitarsa ta ce duk su yi alwala su yi sallah.

Ta ce"Alhaji dama ina so mu yi magan a kan yaran nan".

Ya ce"To, wasu yara?"

Ta ce"Yaranka".

Ya ce"Me ya faru? Ba za ki samu matsala da su ba in sha Allah! Kin ga ma yara ne, uwar ma don Allah ki kau da kai ga matsalolinta".

Ta ce"Ba wata matsala ba ce, ka ga yau taliya na dafa da safe, na ba su suka ce wai ba sa cin taliya, sai kowaccensu ta shiga zaɓar abin da take so, ni kuma na ga ba zao yiwu na yi girki har kala huɗu ba, ko hakan bai zama almubazzaranci ba ai ka ga ni ma ina buƙatar hutu, tun da ba bautarsu na zo yi ba, sannan ba ma tarbiyya ba ce yara su dinga zaɓin abin da za su ci, na ce su tsayar da guda ɗaya, suka ce tuwo, shi ne na yi, loma ɗaiɗai suka yi suka ce mini ba daɗi, ƙarshe sai suka sha golden morn suka ƙule a ɗaki".

Alhaji ya ce"Ikon Allah! Wai kina nufin su yaran suna gidan nan? Waye ya kawo su?"

Maryam ta ce"Wai dama ba ka sani ba? Daga makaranta mai adaidaita sahu ya kawo su".

Ya ce"Yanzu suna ina?"

Ta ce"Suna ɗaki".

Ya shiga ƙwala musu kira ransa a ɓace, suka fito, Kausar da Momy suka haɗa baki wajen faɗin"Abba yunwa muke ji, ba mu ci komai ba".

Ya daka musu tsawa da faɗin"Ku nemi wajen zama!".

Suka zauna duk suka sha jinin jikinsu, saboda Abban nasu ba mai yawan faɗa ba ne.

Ya ce"A cikinku waye ba ya cin taliya? Yaushe kuka daina cin taliya?"

Duk suka yi shiru suna raba ido.

Ya ce"Wato ku har kun yi girman da za ku yiwa babba rashin kunya? Ku sa ta yi tuwo ku ce babu daɗi?"

Ya kalli Maryam ya ce"Idan akwai ki sako musu".

Ta tashi ta je ta ɗakko shi a yadda suka bar shi, ta ajiye, ya saka su a gaba sai ga shi sun cinye tass, har da ƙari, ya yi mamakin dalilin da ya sa suka yi mata haka, ya zaunar da su ya yi musu nasiha sosai, ya nuna musu ita ma Maryam babarsu ce, duk abin da suka san ba za su yiwa babarsu ba to kar su yi mata, suka ce to, sannan ya saki jiki da su suka yi fira, Maryam ta ce su je ta yi musu wanka, ba su yi musu ba suka wuce, sai a lokacin ma ta sa suka yi home work, ƙarfe takwas Abba ya ce su je su kwanta, ita kuma Maryam ta kwashi unifom ɗinsu ta tafi wankewa, sai ga shi sun yi wankin a tare da Alhaji suna yi suna fira.

Ita kuwa Momy suna shiga ɗaki ta ɗauki wayar ta sanarwa Sauda duk yadda aka yi, Sauda ranta ya ɓaci matuƙa ta ji kamar ta taso ta taho gidan yanzu, ta fara tunanin wato daga zuwanta za ta sa ya tsani ƴaƴansa har yana yi musu faɗa? Nan gaba ai sai duka, kenan ya goyi bayanta nan gaba ko ita ce da laifi tana kallo za a tauyewa ƴaƴanta haƙƙi, ai kuwa ba zai yiwu ba, ta fara tunanin hanyar da za ta bi don ta hana su cin amarci, sai dai yaran sun yi ƙanƙantar da za ta saka su yi wata kissar, don haka kawai ta yanke gara ta dawo su fara gabza yaƙin, ta ce wa yarinyar ta yi haƙuri su kwanta, amma kar su sake bari ta yi musu wanka, ita ta yi da kanta sannan ta yiwa ƙannenta.

Washegari haka Maryam ta yi sammakon tashi saboda yaran, don tun a daren ya faɗa mata girki biyu ake yi da wanda za su ci, da wanda za su tafi da shi, ta dafa shayi ta soya doya da ƙwai ta saka musu a lunch box ɗin, sannan ta tafi ɗakinsu, ta tarar Momy ta yi wanka za ta fara yiwa sauran, Kausar tana cewa ita ba za ta yi mata, ta ce"Ya za a yi ki yi musu? Ke ma ai ba wuce wankan kika yi ba, ku wuce na yi muku".

Momy ta ce"Mu fa Ummanmu ce kawai take yi mana wanka".

Maryam ta ce"Tun da yanzu ba ta nan ai dole ku bari na yi muku".

Ta ce"Mu dai a'a".

Maryam ta juya ta fita, ta sanarwa da mahaifinsu, da mamaki ya ce"Ha'a, wai me yasa yaran nan suke haka ne?"

Ya fito ya zo ɗakin, ya ce"Ke Momy! A kan me ba za ta yi muku wanka ba?"

Ta ce"Ummanmu ta ce kar mu yarda da ita".

Maryam ranta ya ɓaci ta ce"Ai shikenan". Ta juya ta bar ɗakin.

Ya ce"Ummanku? Au haka ta tsara muku? Abin da ta turo ku ku yi kenan? To zan haɗu da ita! Ku saka kayan naku a haka ku tafi, idan ta damu sai ta dawo ta dinga yi muku wankan".

"Maza ku saka ku fito, mintu uku na baku". Ya ƙarasa a tsawace yana jin dole ya takawa Sauda burki don ba za ta lalata masa tarbiyyar yaransa ba.

Yana fita Momy ta shiga banɗaki ta kira Sauda ta sake faɗa mata, ai kuwa ta hasala tana ta zage-zage.

Suka fito kowaccensu babu sakewa, sai a lokacin suka gaishe shi, ya amsa kafin ya ce"Kun gaishe da Antinku?"

Duk suka yi shiru, sannan suka gaishe ta ɗaya bayan ɗaya, suka karya mai adaidaitansu ya zo suka tafi makaranta.

Sun gama karyawa ya ce da Maryam"Don Allah ki yi haƙuri, yara ne kin san duk yadda aka tsara musu ba za su yi nazari ba, amma zan same ta na yi mata magana, idan ba za ta barki ki yi yadda ya dace da su ba, to ta zo ta zauna da su".

Maryam ta ce"Allah Ya kyauta".

Kafin ya tafi kasuwa ya tsaya a gidan nasu, ya gaida Inna, ya samu Sauda tana karyawa, ko kallon shi ba ta yi ba, ya ce"Yawwa Sauda na ga kin aiko mini yarana, ina son ki sani Maryam za ta iya riƙe su fiye da yadda kike kula da su, sai dai ki sani indai kin bar mata su to fa sai dai ki koma gefe ki yi kallo, ba zai yiwu tana tufka kina warwarewa ba, saboda shirme kin zauna kina tsarawa yara shirmen banza, to matata uwa ce a gare su, ya zama dole su yi mata biyayya tun da ni na haife su!".

A hasale Sauda ta ce"Ita ta haifar mini su? Wallahi babu shegiyar da ta isa ta tsarawa ƴaƴana yadda za su yi, yarinyar da ba ta samu tarbiyya ba tun daga tushe, har kana kallona kana faɗa mini kalmar matarka?"

Sai kuma ta saki wata dariya mai kama da ta tsantsar baƙinciki ta ce"Heee masu mata manya! To a yi mu gani idan tusa za ta hura wuta, yarinyar da ba ta zaman aure har wata abar alfahari ce? To sai ka jira ka ga zaman ya yiwu kafin ka fara wulaƙanta ni ka watsar da ƴaƴanka!".

Ya ce"Ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login