Showing 30001 words to 33000 words out of 37653 words
kawai take yi mana wanka".
Maryam ta ce"Tun da yanzu ba ta nan ai dole ku bari na yi muku".
Ta ce"Mu dai a'a".
Maryam ta juya ta fita, ta sanarwa da mahaifinsu, da mamaki ya ce"Ha'a, wai me yasa yaran nan suke haka ne?"
Ya fito ya zo ɗakin, ya ce"Ke Momy! A kan me ba za ta yi muku wanka ba?"
Ta ce"Ummanmu ta ce kar mu yarda da ita".
Maryam ranta ya ɓaci ta ce"Ai shikenan". Ta juya ta bar ɗakin.
Ya ce"Ummanku? Au haka ta tsara muku? Abin da ta turo ku ku yi kenan? To zan haɗu da ita! Ku saka kayan naku a haka ku tafi, idan ta damu sai ta dawo ta dinga yi muku wankan".
"Maza ku saka ku fito, mintu uku na baku". Ya ƙarasa a tsawace yana jin dole ya takawa Sauda burki don ba za ta lalata masa tarbiyyar yaransa ba.
Yana fita Momy ta shiga banɗaki ta kira Sauda ta sake faɗa mata, ai kuwa ta hasala tana ta zage-zage.
Suka fito kowaccensu babu sakewa, sai a lokacin suka gaishe shi, ya amsa kafin ya ce"Kun gaishe da Antinku?"
Duk suka yi shiru, sannan suka gaishe ta ɗaya bayan ɗaya, suka karya mai adaidaitansu ya zo suka tafi makaranta.
Sun gama karyawa ya ce da Maryam"Don Allah ki yi haƙuri, yara ne kin san duk yadda aka tsara musu ba za su yi nazari ba, amma zan same ta na yi mata magana, idan ba za ta barki ki yi yadda ya dace da su ba, to ta zo ta zauna da su".
Maryam ta ce"Allah Ya kyauta".
Kafin ya tafi kasuwa ya tsaya a gidan nasu, ya gaida Inna, ya samu Sauda tana karyawa, ko kallon shi ba ta yi ba, ya ce"Yawwa Sauda na ga kin aiko mini yarana, ina son ki sani Maryam za ta iya riƙe su fiye da yadda kike kula da su, sai dai ki sani indai kin bar mata su to fa sai dai ki koma gefe ki yi kallo, ba zai yiwu tana tufka kina warwarewa ba, saboda shirme kin zauna kina tsarawa yara shirmen banza, to matata uwa ce a gare su, ya zama dole su yi mata biyayya tun da ni na haife su!".
A hasale Sauda ta ce"Ita ta haifar mini su? Wallahi babu shegiyar da ta isa ta tsarawa ƴaƴana yadda za su yi, yarinyar da ba ta samu tarbiyya ba tun daga tushe, har kana kallona kana faɗa mini kalmar matarka?"
Sai kuma ta saki wata dariya mai kama da ta tsantsar baƙinciki ta ce"Heee masu mata manya! To a yi mu gani idan tusa za ta hura wuta, yarinyar da ba ta zaman aure har wata abar alfahari ce? To sai ka jira ka ga zaman ya yiwu kafin ka fara wulaƙanta ni ka watsar da ƴaƴanka!".
Ya ce"Ni dai na faɗa miki, idan kuma kin ƙi ji ba kya ƙi gani ba!". Ya fice ya barta tana ta bambami.
Inna duk a gabanta a ka yi komai, ba ta ce wani abu ba, dama idan da sabo ta saba da faɗan nasu, sai da ya fita ta ce"Sauda a nan fa ba ki da hujjar da za ki saka yara su raina matarsa, idan har ba kya son ta shiga sabgar yaranki to ya zama dole ki koma kansu ki ci gaba da kula da su, kin ga dai yadda ya gigice a kan yarinyar nan yake rawar kai, kina nan a zaune za ta gama mallake shi da kissarsu ta zawarawa, irin wannan gogaggun yaran da suke yin aure-aure wallahi ki kiyaye su,sai kin tashi a tsaye kin ɗaura ɗamara, saboda haka ni yanzu umarni nake ba ki ba shawara ba, ki kama hanya ki koma ɗakinki a yau, ki kula da ƴaƴanki, sannan ki yi iya yinki na ganin ba ta mayar da ke bora ba, kar ki yarda ta ƙwace miki mijinki da gidanki".
Sauda ta ce"Shi kenan Inna an jima zan koma".
Inna ta ce"Ko ke fa, wannan ai kina nuna mata ta fi ƙarfinki ne ba za ki iya da ita ba, saboda haka ki koma ki nuna mata gida naki ne, kuma miji da ƴan'uwan shi ma naki ne!".
Sauda ta jinjina kai cike da gamsuwa, ta tashi ta shige ɗaki.
Zama ta yi ta kira ƙawarta a waya ta sanar da ita za ta koma, ta ɗora da faɗin"Don Allah ya za a yi ki haɗa ni da wannan mai maganin? Na san shegiyar tana nan ta gigita shi, bazawara ana marari za a samu miji".
Aliya ta sheƙe da dariya ta ce"Alhamdulillah! Allah na gode maka da ka nuna mini ranar da Sauda za ta nemi maganin gyara zama".
Sauda ta ce"Au shaƙiyanci za ki yi mini kenan".
Ta ce"To ai ke ce kullum cikin kuri kike kina da ni'imarki ba sai kin sha komai ba, yanzu kika dawo hanya Hajiyata, zan turo miki lambarta".
Sauda ta ce"Malama yanzu fa nake so, zai yiwu ta aiko mini kayan a yau?"
Aliya ta ce"In sha Allah!".
Tana turo mata, ta kira ta a waya, suka yi ciniki gabaɗaya irin wanda ake cewa ban da me kishiya su ta siya na dubu ɗari, kuɗin gudunmawa ne dangi suka haɗa mata don ta yi gyaran dama, da yamma aka aiko mata da kayan, ta gama shirinta tsaf jira kawai take yi ya zo yi wa Inna sai da safe ta bi shi su tafi.
Yau ɗin Maryam shinkafa da miya ta yi, da alama yaran ba ma su taurin kai ba ne, don kuwa yau babu wanda ya yi magana a kan abinci, kowa ya ci, sannan sun tsaya ta yi musu wanka, ban da babbar da ta ce ita ce take yi da kanta dama, sai ta rabu da ita, amma dai sam sun ƙi yin fira da ita, don haka ita ma ta ke ta harkar gabanta.
Da yamma da ya dawo sai da ya tambaye ta yaran, ta ce babu wata matsala, ya yi wanka ya ci abinci, ya fita sallah ya dawo, dama idan zai fita sallar isha'i da mota yake fita saboda daga can yake wucewa gidan Inna ya yi mata sai da safe, don haka yau ma ya wuce, ya ɗan zauna bayan sun gaisa, hat yanzu ta ƙi dawo masa kamar baya, babu wata fira haka dai babu yabo babu fallasa, ya tashi zai tafi ta ce"Ka zauna".
Ya zauna yana sauraronta.
Ta ce"Sauda za ta bi ka ta koma kan ƴaƴanta, saboda haka kar na ji kar na gani, ka zama mai adalci a tsakaninsu, kar sabo ya sa a watsar da tsoho, ta farkon dai ita ce dahir ɗinka, ba zan ɗauki wulaƙanta mini ƴa ba wallahi, don haka ka ja kunnen yarinyar nan, ta kula ta kiyaye, tun da zuwa ta yi ta tarar da ita da ƴaƴanta, ba ta san faɗi-tashin da aka yi kafin ka kai matakin da kake a yanzu ba".
Ya ce"To Inna za a kiyaye in sha Allah!".
Ya tashi ya fita yana yi mata sai da safe, ya ɗan jima a motar kafin Saudar ta fito da akwatinta, ta buɗe motar ta shiga ya ja suka tafi, babu wanda ya ce wa wani ƙala har suka ƙarasa gidan, lokacin yaran suna ɗaki, Maryam kuwa tana hakimce a babban falo cikin wata fitinanniyar rigar bacci, suka shigo da sallama, niyyarta idan ya shigo ta je yin oyoyo amma sai ta yi turus ganin shi tare da wata wacce ba sai an faɗa ba ta san matarsa ce, sai da gabanta ya faɗi, ta daure ta ce"Sannunku da zuwa".
Alhaji kuwa ya bi ta da kallon burgewa, wankan ya burge shi, don Sauda babu ruwanta da wani wankan dare ballantana kuma kayan bacci, dogayen riguna ne marasa nauyi kayan baccinta tun da ta fara haihuwa, ya haɗiyi wani yawu muƙut wanda har Sauda ta ji sautin, zuciyarta ta ƙara kumbura, ta kasa shigewa kawai tana tsaye tana ƙarewa Maryam kallo, sai Alhaji ne ya katse shirun nasu da cewar"Na barki ke kaɗai a gida".
Sauda ta yi masa mugun kallo ta ce"E tabbas ita kaɗai, tun da a yanzu ita kaɗai kake kallo a mutum, su ƴaƴan naka ba mutane ba ne, komai ma ya same su ta matarka kake yi! Hmm!" Ta wuce fuuu ta yi cikin gidan.
Ya yi murmushin yaƙe ya ce wa Maryam"Kin ga Sauda ta dawo ko? Don Allah ku zauna lafiya, kin ga ma tun da ta dawo kan yaranta za ki fi kula da ni sosai ko?"
Ta yi farr da ido ta ce"Ƙwarai kuwa, zo ma mu je ka gani".
Ta yi ɗakinta, shi kuwa ya bi bayanta kamar raƙumi da akala, a gaban Sauda suka shige ɗakin nata, wacce ta fito daha ɗakin yaranta za ta shiga nata, ta manta rabon da ya shiga ɗakinta, sai dai ita ta bi shi nashi ɗakin idan ya kira ta, amma shi ne ya zo ya shige ɗakin amarya ko kunya ba ya ji, ta yi ƙwafa tana cewa"Lallai akwai aiki a gabana, tsohuwar kilaki ya kwaso".
Ta gagara zama a ɗaki, ko wanka ta kasa yi, sai leƙe take yi tana jiran fitowarsa amma shiru har ƙarfe sha ɗaya ta yi, ga shi ko sallar isha'i ba ta yi ba, kuma ta kasa yi, saboda tana son tabbatarwa da gaske a nan zai kwana? Shi kuwa Alhaji yana can Maryam ta saka shi a kwana ta kalallame shi, ta kanainaye shi har ya manta ma a ɗakinta yake.
Ƙashe dai sai sha biyu Sauda ta haƙura da leƙen ta yi sallah, ta kwanta, sai ta gagara yin bacci gabaɗaya ya ƙaurace mata, ta fara tunanin yanzu fa yana can tare da ita, lallai namiji ba shi da kunya, can dai ta fara tunanin ya za ta yi ta hana su sukuni, ta tashi ta fito a hankali ta shiga ɗakin yaranta, ta haska su, sai baccinsu suke yi hankali kwance, ta shiga tashinsu bisa shawarar zuciyarta, ta dinga jijjiga su duk suka tashi suna murza ido, ta sakawa fuskarta alamun firgici ta ce"Ku tashi don ubanku, aljanu ne suka shigo gidan! Suna ɗakin nan a ƙarƙashin katifarku!".
Ai kuwa a tare suka fara ihu, ta ce"Ku kwanta ba za su yi muku komai ba".
Suka fara kuka suna rirriƙe ta suna cewa a ɗakinta za su kwana.
Ta fizge tana cewa"Suna can a ɗakina sun cika ɗakin kowa ya yi ta kansa".
Ta fice a guje suka mara mata baya, amma kafin su shiga ta banke ƙofarta ta saka sakata, gabaɗaya suka ruɗe suka dinga ihu a mugun firgice kamar za su shiɗe.
A tare Maryam da Alhaji suka fito a ruɗe, suka tarar yaran suna ta buga ƙofar ɗakin babarsu, fitowarsu ya sa suka yi wajensu suna shigewa jikinsu cikin matsanancin kuka, Alhaji ya ruɗe ya fara tambayarsu me ya faru?
Suka ce"Aljanu, Abba aljanu a ɗakinmu".
Gabansa ya faɗi ya ce"Aljanu kuma? Me kuka gani?"
Inaa sun ruɗe, sai a lokacin Sauda ta fito tana cewa"Mene ne?"
Suka yi kanta suna kuka.
Alhaji ya ce"Kin ji wai aljanu".
Ta ce"Aljanu kuma?"
Ya wuce ɗakin a tsorace yana addu'a, ya haska bai ga komai ba, ya dawo a sanyaye ya ce"Abun ya bani mamaki wallahi".
Sauda ta ce"To kar dai fa ture aka fara yi musu".
Ya ce"Wane irin ture? Waye zai yiwa yaran nan ture?"
Ta ce"Wanda suka tsonewa ido mana, an ga yara sun cika gida tubarkalla ana son haukata su don kar ƴaƴana su moru".
Alhaji ya ce"Subhanallah! Kar na sake jin magana irin haka!".
Ya janyo yaran yana cewa"Tsorata kawai kuka yi babu komai a ɗakinku kun ji? Ku je ku kwanta zan yi muku addu'a".
Sauda ta ce"Au da gaske sai ka kora su, saboda kar kwanan ɗakin amarya ya wuce ka? Hmm dama uwa ce ba ta gudun ƴaƴanta duk runtsi, ku shigo nan!".
Ya ce"Ba za su shiga ba! A ɗakin nasu nake so su kwana ina son fahimtar wani abu ba ne kafin Allah Ya kaimu gobe na kira malamai a yi addu'a".
Maryam ta ce"Allah Ya rufa asiri". Ta koma ɗakinta, ita ma duk sai tsoron gidan ya kama ta.
Ya saka su a gaba suna turjewa suka shiga, ya zauna ya kunna karatun qur'ani a wayarsa, yana addu'a yana tofa musu, amma da bacci ya fara ɗaukarsu sai su zabura su farka suna maƙale shi, a haka suka kwana, ita kuwa Sauda ta yi baccinta ranta fess, tun da dai ta haramta musu wannan daren to ita fa buri ya cika, kuma ta saka a ranta yanzu aka fara wasan, ta ɗau alƙawarin sai ta fitini gidan gabaɗaya, sai kwana a ɗakin shi ya gagari Maryam, kafin ta tankaɗa ƙeyarta waje.
LAST FREE PAGES! A NAN ZAN TSAYA DA FREE PAGE, DAGA WANNAN SHAFIN DUK WANDA KUKA GANI A PAID PAGE NE, ƳAN'UWA KU BIYA KU KARANTA CIKIN AMINCI, YANZU ZA A FARA WASAN NAN, TAFIYA TA KISHI MAI CIKE DA ƘULLA-ƘULLA TURA ƊARI BIYAR ƊINKI TA NAN KI SHA KARATU CIKIN AMINCI.
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay
08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 13
Alhaji Haruna har zuciyarsa ya yi niyyar kamanta adalci, saboda haka duk da Sauda tana gidansu da ya tashi siyan kazar amarci haka ya siya da nata kashin, dama a baya kashi biyi yake siya da nata da na Innarsa, yau kuwa sai ya sayi kashi uku, ya tafi gidan don ya yiwa Inna sallama kamar yadda ya saba a kowane dare, lokacin tara saura kwata, ya same su a falo, ya ƙarasa a sanyaye ya zauna yana gaishe da Inna, ta amsa fuska babu walwala, ga yaran can rakuɓe a gefe, sun nuna kamar ba su san shi ba, saɓanin da, da idan ya shigo gida a guje suke rige-rigen zuwa gare shi, yaran su huɗu ne, Momy ita ce babba shekararta goma sha ɗaya, sai mai bi mata Kausar, shekararta takwas, sai Ummi shekararta shida, sannan Nana mai shekara huɗu, daga kan Nana ya ce mata ya kamata ta ɗan yi planing don mahaifarta ta huta, ta biye masa ta saka inplan na shekara uku da ya yi expire ta cire ta sake saka wani, don haka yanzu take ganin dama shi burinsa ta tsaya da haihuwar saboda amaryarsa ta zo ta zazzago masa ƴaƴa, kallo ɗaya ta yi masa ta kau da kai gefe, saboda mugun haushin shi da take ji, ya ce da babbar ƴar"Momy ko gaisuwa babu?"
Sai ta waiwaya ta kalli mahaifiyarsu, saboda tun da suka yi yajin nan kullum sai ta zaunar da su ta faɗa musu babansu yanzu ya daina son su dukansu, shiyasa zai ƙara aure, kuma shi ya kore su dukansu, sannan amaryar da zai aura muguwa ce, kashe ta za ta yi ta zama ita ce uwarsu, kuma dukansu za ta dinga yi, tana hana su abinci, shi kuma baban nasu ba zai yi komai ba, saboda ya daina son su, haka dai ta tsara musu abubuwa kala-kala daidai da tunaninsu, su kuwa hakan ya sanya musu damuwa da jin tsoron baban nasu.
Sai da ya yi magana sannan suka fara gaishe shi ɗaya bayan ɗaya, ya amsa yana ce musu"Ya makaranta?"
Sauda ta yi wani huci kamar zakanya ta tashi buguzun-buguzun ta bar falon, kasancewarta mace mai ƙiba kuma doguwa, ya bi ta da kallo, sai ya ajiyewa Inna ledarta ya bi bayan Sauda ɗin, zaune ya tarar da ita ta naɗe hannu a ƙirji, ya yi sallama tana kallon shi yana kallonta ta ƙi amsawa, ya zo ya zauna a gefen katifar da take, sai ta miƙe za ta fita, ya ce"Kin ga Sauda zauna mu yi magana".
Ba ta zauna ba, amma ta fasa fitar,shi ma sai ya tashi tsayen ya ce"Ni fa ban ƙara aure saboda kin gaza mini ba, sai don ina da ra'ayin yin hakan, kuma dama can mata biyu ne a ƙaddarar aurena, idan mai afkuwa ta afkuwa ya kamata ki ajiye komai a gefe, ki koma ɗakinki, ni sai nake ganin ba girmanki ba ne a ce yarinyar nan ta zo ta tarar kin yi yaji, kamar hakan zai janyo miki raini".
Ta yi shiru dai ba ta ce komai ba.
Ya ci gaba da faɗin"Maryam ƙanwarki ce, kuma tana da sauƙin kai, za ku zauna lafiya in sha Allah, ni dai yanzu ki wuce mu tafi gida kawai, wannan abin da kika yi sai ki jawo mini zagi a gari, nan kuwa ba ni na kore ki ba".
Ta ce"Babu inda zan je, ka je ka zauna da wacce ka zaɓa, kuma sannan zan aiko maka da yaranka, tun da ita ka zaɓa kake ganin za ta iya sai ta riƙe maka!".
Ya ce"To shikenan, ni dai ba zan yi miki dole ba, musamman ma da Inna ta goya miki baya, saboda haka ki yi duk yadda kika tsara, amma ki sani ni dai ba zan sake ki ba".
Ta ja dogon tsaki.
Ya ce"Akwai abin da kuke buƙata?"
Sai a nan ta ce"Ba na buƙatar komai daga gareka, kai kanka bana buƙatarka ballantana abun hannunka, ita da kake baƙo a wajenta ka je can ka yi mata komai!".
Ya yi ɗan murmushi ya ce"Sauda kina da kishi, amma ban taɓa zaton za ki bar gidanki saboda kishiya ba, wai har kina barazanar za ki ba ni ƴaƴana, to ki ba ni, zan riƙe su".
Ya ajiye mata ledar hannunsa, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya ajiye mata ya fice, bai tarar da kowa a falon ba, sai ledar da ya ajiyewa Inna, cike da dumuwa ya bar gidan. Amma ko da ya je gida ya tarar da amaryarsa sai ransa ya yi fess, yana son Maryam sosai, suka sha amarcinsu hankali kwance har ta mantar da shi yana cikin damuwa.
Washegari ya tafi kasuwarsa, ita kuma ta gyara gidan, tana ta baƙi jefi-jefi da maƙota da ƴan'uwa, maƙotan dai duka ƙawayen Sauda ne, don haka gulma ce kawai take kawo su, kowacce idan ta shiga ta ganowa idonta sai ta kira Sauda ta yi mata sharhi,