Showing 9001 words to 12000 words out of 81157 words
irin masifa ce,
Cikin tsananin zafin Rai da baqin ciki yace"
Allah ya tsinewa ubanda yayiwa ruqayya cikin balai.
Amin dattiya da iya talatu Suka fada atare sbd tsananin matsen dasuke da zakin.
Dattiya dake jin tsananin zugin qafarsa data fara kumburi yace"
Allah yaji qanki ruqayya ya saka Miki da duk Wanda yayi Miki wannan ta'asar Dan kuwa yaci amanar marainiya baiwar Allah ta tafi ta huta da ganin wannan balai.......
Shigowar JJ ce tasa dukkaninsu yin tsit suna matse fuska da bacin rai sbd sunsan Zaki na kusa tunda sukaga JJ.
Nadiya dake zaune gefen talatu tana mata aiki tana dago Kai Yana shigowa
Kyakkyawar fuskarnan tasa a tamke Saidai wani sirrin kwarjininsa dake Hana ayi masa kallon qwaf yasa tayi qasa da kanta kafin yaqarasa sauke takaicinsu baba akanta.
Dakinsa yashiga daidai shigowar zainab da hijabin data aro gurin anty samira amaryar baba idi sbd sanin Yaya Zaki nanan tunda taga bataliyarsa a qofar gidan.
Tashi baba idin yayi Yana sake daure fuska Yana Harare Harare ya fice Yana cewa"
Allah dai baya bacci tunda gumi akace dai mutum ya hada gurin neman halas Kuma mun hada Amma gashinan.
Kawu Dattiya najinsa yaqiyin magana sbd kar ajisu Dan shidai yagaji da wannan masifar daga yanxu zai ringa iya yinsa gurin raba hanyarsa da Zaki Dan yagama sani yanxu Kam tsaf Zaki zai iya ganin bayansa,
Shi wlh dama yasani yabari neyo ya auri ruqayya dabataje ta samo musu wannan iftila'in ba Dan kuwa gwara ta'addancin neyo so ba adadi akan na Zaki tunda gashinan sbd harta haihu ta rasu Bata daina qaunar neyoba tunda Zaki ma aliyu haidar neyo tasaka masa gashinan sunan neyon yabisa.
Tashi Nadiya tayi sum sum ta dauki bokiti ta Debi ruwa da tsintsiya ta nufi bayi tafara wankewa sanin duk yafita yashawo Rana idan yadawo Yana wanka.
Tana gama wankewa tafito kenan shikuma zai shiga baisan da itaba
Itama batasan dashiba sukai karo tayi saurin yin baya zata fadi
Da hanu daya yariqo hannunta a tsorace ta dago Saidai takasa kallon fuskarsa kafin tasake dagowa ya jehota waje tareda rufo bayin.
Dattiya da tun dazu ya miqe zuciyarsa na tsalle ganin Zaki zai shiga bayi 'yarsa na ciki Yana ganin anjehota waje yasake ajiyar zuciya sbd Rashin madafa sai kawai yahau Nadia da fadan Rashin dalili,
A zuciyarsa kuwa sauqi yakeji da duk iskancin Zaki baya ko kallon mata bare nemansu da lalata sbd 'yar Nadiarsa yake gudun a lalata tunda ita zainab uwarta ta daure mata gindi tana yawonta bai saniba ko tagama lalacewar,
Ita kuwa Nadia ko maqure masa ita akayi za'ayi lalata da ita batada muryar idon neman ceto,
Kai shidaima gwara yayi mata aure ya huta ta huta itama Dan haka zai bama 'dan gidan mal zailani dayake sana'ar gyaran su fanka dama tunda yace Yana sonta.
NADIA kyakkyawar black beauty ce Saidai ba baqa bace sosai Sam batada wani jiki sosai hakama tsawonta daidai misali Saidai kusan dukkaninta daka ganta kasan mahaifiyarta ta 'dauko Saidai 'dan duhun fatar na mahaifintane ta dauko.
Sanyin haline da ita shiyasa ayukanta Suka zama suma a sanyaye takeyinsu.
Juyi tayi kan shimfidarta tareda bude ido ahankali sbd kamar jin alamar wani acikin dakin....
Faduwa gabanta yayi da qarfi sbd tunanin hakan datayi gashi tsakiyar dare ne komai Bata gani sbd duhu gashi ita ko fitila batada.
Miqewa tayi zaune tafara laleben kofin silver datake kwana dashi kullum sbd amfani dashi dan irin haka.
Tana cikin lalaben taji ta lalabo qafar mutum wata muguwar zabura tayi jikinta na tsananin rawa tayi bayi tanason ihu takasa sai hawaye tafara qoqarin tashi zata gudu taji kowanene ya damqota tareda matseta a bango Yana dariya qasa qasa.
Rawa jikinta keyi sosai tana qoqarin kwace kanta hawaye tuni Suka fara jiqa rigarta musamman ma wani irin tsamin giya dake tashi ajikinsa.
#MAMUH.
*_Buri daya_*
*_Mamuhgee8_*
'Dagata yayi cak tana buge buge yakwantarda ita qasa tareda danneta Yana neman wuyar rigarta inda zai zura hannunsa.,
Sake lalubar kofin silverta tayi hankalinta a matuqar tashe ganin rabata da mutuncinta zaiyi Dan kuwa tuni ya farka rigarta dataqi Bari hannunsa yahau kan qirjinta da kyau.
Wani irin kuka takeyi mai qarfi Saidai ba sauti,
Hannunta ne ya sauka akan kofinta ta wuwuri kofin ta jefa saitin qofa da qarfi gashi qofar itama langa langa ce.
Sautin qarar sai akan kunnen Zaki sbd hakanan yau yakasa bacci Wanda JJ ma ganin hakan yakasa bacci.
Dattiya ma yaji ya miqe yataso da fitilarsa Yana fitowa tsakiyar gidan gabansa yayi mummunan faduwa jin motsi mai qarfi Yana fitowa dakin nadiyar.
Sbd tashin hankali sakin fitilarsa yayi ya banka dakin da qarfi Yana kiran sunanta hankali tashe.
ba zato yaji mugun bugu a bakinsa a gigice ya dago cikin duhun ya riqo hannun Nadiya Yana qoqarin qwaceta ban qaton ya haushi da bugu.
Tun lokacinda kawun yakira sunan Nadia ya rufe idanuwansa ahankali sbd jin jikinsa nafara rawa.
JJ ne yayi saurin miqewa daga kwance yadauki fitila da wata sharbebiyar kakkaifar Adda yafito ya nufi tsakar gidan.
Bayan fitars JJ sake rintse ido yayi wannan karon numfashinsa yaji Yana shaqewa kamar mai asthma.
JJ na isa yaga abinda ke faruwa nadiyarma kamar ta suma ga kawun yariqeta yaqi sakarwa shegen shikuwa dukan hannun kawun yakeyi Yana janta.
Cikin tsananin tashin hankali da baqin ciki jj yakaiwa kb din wani mugun naushi a fuska Saida yasaki wani razanannen ihun daya tayarda sauran mutanen gidan duk Suka fito.
Sunan Nadia da kawun yasake Kira da qarfi yasa iya talatu kallon kayanta dasuke yage tafara salati tana tsinewa kb.
Shaqosa JJ yayi a fusace ya daga hannu zai Kai masa mugun duka kb din ya daga hannu zai tare sai ganin hannun sukayi a qasa jini na wani irin tsirtawa wani guntun fitsari iya talatu tasaki zainab kuwa gabaki daya tasaki nata fitsarin sbd Basu taba ganin wannan tashin hankalin ba.
Dukkaninsu juyowa sukayi sukaga Zaki riqeda addar da JJ ya ajiye.
Atake kb yafadi Yana ihu da qarfi sbd ganin hannunsa a qasa ga Zaki ya sare,
JJ ne kawai baiji tsoron ganin jini da abinda Zaki yayiba tunda sun Saba gani aikinsu ne,
Shaqo kb din yayi Zaki ya hanasa tareda jawo kb ko gani bayayi sbd tsananin halinda yake ciki yau idan bai raba kb da duniyaba bayajin abinda yakeji zai fada masa,
Rintse ido yayi ya hangota kwance some jikin kawu kayanta dake babbarke ne suke neman haukata qwaqwalwarsa.
Wata sharbebiyar wuqa ya fizgo a jikin jj ya yaga wandon kb din da ita ya daga da qarfi zai sare masa gabansa JJ dasu nano dasuka firfito daga dakin qofar gidan Suka riqesa suna Allah ya huci zuciyarka sarki Amma karka masa wannan hukuncin,
Cikin hasala jj yace"
Neyo kabarmu dashi,
Yataba hurumin da ba'a tabawa zamuji dashi.
Wurgi yayi da wuqar Yana yamutsa kansa jin yake kamar ya cinnawa kansa wuta sbd zafin da zuciyarsa keyi,
Jiyake abinda ya tokare masa a qirji kamar zai kashesha,
Da qarfi yace"
Ku sauyamin kamanninsa yanda ko uwar data haifesa koya warke bazata ganesa ba,
Ku karya sauran dayan hannunsa daya taba suturar dake jikinta,
Ku karyamin qafafunsa,
Ku kasheminshi,
Ruwa JJ yayi saurin kawo masa yayi wurgi dasu Yana cewa"
Zuciyata zata saukane idan nagansa kwance cikin mummunan yanayi.
Aikuwa wani irin duka su JJ dasu Nanu sukai masa duk da dare ne atake gurin yacika Dole aka Kira police ganin zasu kashesa.
Koda police sukazo kb kawai Suka dauka sukai asibiti dashi tareda gundulen hannunsa a leda.
Cikin gidan kuwa ruwa zainab ta debo qafafunta da hannuwata na rawa taba baban ya kelayawa Nadia
Atake ta farfado a firgice cikin tsananin tsoro jikinta na rawa
Zainab tayi saurin rungumeta tana hawaye itama sbd kaf dinsu gidan suna tsananin son junansu Saidai halayensu ne kesa ka dauka basason junansu.
Baban kuwa miqewa yayi yace suje dakin zainab su kwanta tare.
A Daren Kam kowa bai koma bacciba musamman Zaki da dattiya daya qara gama yanke shawarar aurar da ita cikin qanqanin lokaci.
Washe gari duk wasu yaran Zaki Saida sukai baqin cikin wannan Rana sbd sarki dai ranar ko qofar gida bai fitoba ataqaice dai Saida ale dikko ya Aiko masa da babban likitansa ya dubasa sbd ko miqewa tsaye daidai ciwon kirji mai qarfi yaqi Bari yayi.
Kb Kuwa ba'a mutuba Amma anci wuya Dan kuwa gabaki daya a kumbure yake ga jini daya zubar sosai sai qara masa akeyi gashidai yanxu baida hannu daya Kuma hukuma nagani tayi biris yanajin sauki aka sallamesa yayi alwashin saiya Rama abinda sarki yayi masa shida yaransa Dan kuwa shima baya tafiya.
Bayan kwana biyu duk tasake zama wata iri da ita sbd sanyi data qarayi sosai gabaki daya rayuwarta mutum biyune rayuwarta,BABANTA da YAYA ZAKI tunda abin nan yafaru Zaki ya daukewa 'yan gidan wuta gabaki daya sai shakkarsa taqara shigarsu sai kaffa kaffa sukeyi musamman ma ita.
Baba kuwa tuni yasamu mal zailani da maganar auren da 'dansa bello yace yanaso na Nadia.
Babu wani dogon qunbiya qunbiya Suka gama maganarsu tunda kowa yasan kowa tare sukai samartakarsu.
Bayan mal zailani yayi magana da bello kan maganar shima yace a shirye yake asa Rana kawai.
Har gida mal zailani yasamu dattiya shida wani yayansa da abokinsa
Shima dattiya yakirawo mal idi
Suka sake magana akai neman aure Suka bada kudin nema dubu goma.
Washe baki dattiya yayi ganin 'yan dubu dubu Yana cewa aransa""Ankwana biyu baa haduba"
Karba sukayi aka yanke ranar aure wata biyu masu zuwa insha Allah.
Suna tafiya dattiya yasake qirga kudin Yana murmushi yaciro dubu biyu ya miqawa mal idi ya zuba saura aljihu Suka fita.
Lokacinda ya sanarda iya talatu maganar kallonsa tayi cikeda haushi tace"
Kai yanxu Dan Allah shine ka karbi kudin gaisuwar zuqeqiyar yarinya kamar Nadia a dubu goma??
Kunna radio dinsa yayi Yana kamo gidan fm yace"
Eh ko dubu biyar ne dai na bayar
Lokacinda wani shegen zai sake shigowa ya asarani kinacan kina baccin wahala ko dubu 'daya bazatayiba.
Tsuke fuska tayi tana hararar qafafunsa dasukai 'yar banzar qura tace"
To nidai karka doramin wainnan qafafun masu dau'da a tabarmar sallah ta tunda Nima koda nahada kudin gumina nasiyeta kanacan kana yawon ta zubar a gari.
A kufule ya kalleta yace"
To ko natashi ma akai gaba daya?
Talatu kin renani waike bakisan darajar miji bane koyaushe bakimin 'daa sai gasa baqaqen maganganu.
Tabe baki tayi tana cigaba da hada garin matarta data gama zubawa 'yar fulawa.
Miqewa yayi Yana masifa ya zari babbar rigarsa ya fice koba komai yau basuje sana'ar ba gwara ko ita yaje yasamo ko dubu biyu ko 'daya yamaga ana taro acan gaba.
Da harara tabi bayansa tana cewa"
Kadaiji dashi
Lokacinda jarababben mai mulkin gidannan zaiji ka karbi kudin gaisuwar nan ai lokacin ne zanbaka tabarmar jinyar kanka.
Zainab dake fitowa cikin daki tasaki dariya sbd tana jinsu sbd itama tasan daga baban har bellon na ruwa tsundum.
NADIA kuwa yitayi kamar batasan abinda ke faruwa tacigaba da sha'ainin rayuwarta.
#MAMUH.
*_Buri daya_*
*_Mamuhgee9_*
Bayan sati biyu da magana ranar jumaa da yamma Bello yazo qofar gidan tareda abokinsa nuhu dukkaninsu sunyi adonsu cikin yadin wagambari na leda sai qyalli yakeyi na gugar dayaji,
Dattiya dake tareda idi a bakin masallacin layin suna magana Yana hangosu ya washe baki cikin jin dadi sbd yanzu yagama adduar Allah yakawo masa hanyar samun ko dubu 'dayace.
Atareda mal idin Suka fito sarari dansu hangosu aikuwa suna hangosu gurinsu Suka nufo har qasa Suka durqusa Suka gaidasu
Dattiya sai saka musu albarka yakeyi Yana washe baki kafin yayi gaba Yana cewa"
Bismillah ku qaraso ciki aikaima Bello yanzu kazama 'dan gida tunda zaka auri NADIYA.
Wasu ruwa da JJ yasaka abaki Suka mugun dawo masa da qarfi sbd jin maganar qarshe da kawun yafada,
Tari yafara mai qarfi sbd sosai ruwan Suka sarqesa,
Kallon qofar dakin sarki yayi sbd yabarsa Yana bacci yakumasan qila yatashi.
Saurin juyawa yayi yashiga dakin yagansa Yana motsin tashi Kuma ya tabbatarda baijiba.
Juyowa yayi yafito zuciyarsa na jujjuya zancen to kodai shine baiji daidai ba Amma Kuma su bellon yanda suke wani sassauke Kai yatabbarda akwai wani abin.
Kasa zama yayi yakoma dakin yaga yatashi Yana zaune bakin katifa Yana waya cikin basarwa yagane da ale dikko ne yake wayar,
Sake juyawa yayi ya fice duk hankalinsa ba'a kwance ba sbd bayason sarkin ya fito.
Bai gama tunaniba yagansa ya fito fresh skin dinsa mai haske Yana zufa alamar zafine yafito dashi koba komai lokacin wankan maraicensa ne.
Bai kalli qofar gidanba idan su JJ da sauran yaransa suke yayi cikin gida Dan yin wanka da threequater dinsa da armless riga dama sai tawul rataye a wuyansa fuskarnan tamke kamar ko yaushe.
Zainab ce tafara hangosa ta miqe tareda daukar wayarta dake gefenta tareda takalmanta data gama wankewa ta nufi dakinsu tana cewa"
To Bello sai anjima nizan shiga na Dan yi waya.
Cikeda jin dadi bellon yace"
Yauwa zainab to nagode.
Cikin 'daga murya iya talatu tace"
Ke Nadiya bazakiyi sauri kifito bane kinbarsu sun gaji da tsugunawar qafafuwansu harsun fara rawa.
Batareda dattiya yasan da zuwansa ba yace"
Shashanci me kika tsayayi haka za'ayi auren kije kina masa sanyin jiki?
Baice musu qala sai ita daya kalla lokacinda tafito sanyeda sabon hijabi zainab ta sanyo mata Hoda harda janbaki maroon dayayi mata kyau sosai kasancewar Bata taba saka janbaki mai kalaba iyakacinta Vaseline abaki.
Wani mugun kallo ya watsa mata atake ta rikice tana neman juyawa cikin muryarsa mai saka shiga taitayinta yace"
Bani ruwan wanka.
Da sauri nuhu abokin Bello ya miqe Yana cewa"
Sarki Bari na debo maka da kaina ma...
Wani kallo sarkin yayi masa dayashi saurin sakin bokitin...
Gyaran murya dattiya yayi tareda hararar gefen zakin yasaki yaqen Dole yace"
Nuhu Aida kabarshi ta Diba tabashi saiku koma daga soron gidan zaima fi muku nutsuwa can din.
Aikuwa kamar jira suke Suka miqe Suka koma soron gidan Dan dama dukkaninsu a tsarge suke da ganin Zaki na gida sun dauka bayanan.
Aikuwa tana Kai masa ruwan tadawo ta nufi soron gidan tanajin ba dadi cikin ranta sbd ganin wani kallo dayayi mata lokacinda ta aje masa ruwan.
Suna ganinta Bello yahau washe baki sai alokacin Suka saki jiki Suka fara gaisawa itadai tana rakube a gefe.
Nuhu ne ya zaqe yanata jawo musu fira sbd yafi bellon rawar Kai da iyayi shikuwa bellon sai kallonta yake Yana murmushi Dan kuwa shi harya farajin sati biyar dinda Suka rage sun masa nisa.
Qamshin sabulun wankansa na imperial L da ita kadai tasani yasata sake rabewa tareda sunkuyar dakanta
Bello kuwa harda qara Ware idanuwansa da kyau Yana sake mata kallon qurulla
Ga nuhu sai kawo musu zancen soyayya da yanda Bello kesonta yakeyi Yana qarawa.
Tsaf fararen idonsa Suka shiga cikin nata atake jikinta yadau rawa taji hawaye na ciko idanuwanta.
Yana shigowa soron JJ yataso daga qofar gida yashigo
Kallo daya yayiwa Zaki yaga ba fuskar masa magana harya shige dakinsa shikuma yajuyo gurinsu Bello fuska a hade yace"
Kai ku Ware daga nan bamason hayaniya,
Wuqa ya fitar mai shegen kaifi da qyalli ya Dora saitin wandon Bello da jikinsa yafara mazari yace"
Duk Randa nasake ganinka gidan nan saina maka zanen gobirawa anan""yaqarasa fada Yana zungurin wandon da wuqar.
Nuhu tuni yayi muryar sanyi yace"
Zamu kikyaye oga JJ.
Qofa ya nuna musu tuni Suka wuce da sauri wani na tunkudar wani musamman sauran yaran neyon dake cikeda qofar gida duk sun mimmiqe.
Kamar Bello zai fashe da kuka haka ya isa gida ya tube yasaka riga da wandonsa na aiki ya nufi shago Yana fushi Dan kuwa wlh JJ yacucesa daya korosu Dan kuwa so yayi yau ya dasa soyayyarsa a zuciyar nadiyarsa.
JJ kuwa bayan fitarsu mayarda wuqarsa yayi ya juyo gurinta fuskarsa a sake sosai Dan dama dashi kadaine take dadewa Yana Mana fira.
Fira yadinga mata wani lokacin har murmushi takeyi tana rufe fuska sbd rabi duk tsokanarta ne yakeyi da maganar soyayya.
Ahaka har kusan magriba kafin yabarta tashiga gida tana murmushi shikuma yayi waje Dan kuwa yasan sarki baison kusancin kowa ayanxu.
Dattiya dake jiran shigowarta ya qurawa hannunta dake cikin hijabi ido
Cikin sanyi take qarasowa tana murmushinda itama Bata saniba
Ahasale dattiya yace"
Wai meyene haka kike tafiya kamar Mara ruwan jiki???bazaki cire hannunki daga hijabin bane saikace matar alaramma.
Fitarda hannuwanta tayi yaga Babu komai a hannun ya tsuke fuska yace"
Ruwan alwala kikazo dibar musu???
Girgiza Kai tayi tareda masa alamar sun wuce.
Cikin yayi da qananun idanuwansa tareda miqewa ya dauki buta baisake cewa kowa qala ba yashige bayi tun acan ma yayo alwalarsa Yana fitowa butar kawai ya aje ya fice.
A masallaci ma koda yaje kusada Zaki da JJ yasamu sahu nan yasake tsuke fuska musamman dayaga JJ namasa wani ladabi yasan cutarsa zasuyi Saidai ganin fuskar JJ a tamke tam Babu Wasa yasa yasake tsuke tasa shima Dan ko gaisuwa baiso.
Ana gama sallah yafito JJ yabiyo bayansa suna fitowa yaja ya tsaya yace"
Lafiya zaka bini?
Murmushi JJ yayi Yana Sosa Kai cikin 'dan ladabi zaiyi magana kawun ya katsesa da cewa"
Wannan ladabun mai amsheka ba sam,
Kafitomin a zallar yanda kake kamun magana idan ma itace kakeda ita.
To kawu dama inson Nadiya ne shine nakeson sanarda Kai Kuma Nima aurenta nakeson yi......
Wani kallon takaici kawun yamasa kafin cikin bacin Rai yace"
'yar tawa zanbawa magajin dake jiran gado a dabanci,ta'addanci,da Sara Suka?
Wato gani dattiyan mahaukata tunda kaga Ina sake muku fus....
Ido hudu yayida Zaki dake bayansu saiya qarasa maganarsa da cewa"
Kaga jabiru kabarni da wannan maganar nariga nabawasu Bello saura sati biyar bikin ma.
Juyawa JJ yayi sbd jin yanda kawun yayi magana cikin lalama sabanin farko daya fara masa Rashin arziki
saiyaga Zaki yasaki murmushi kenan ganinsa yasa kawun sassauta harshensa.
Ahankali yaqaraso yau kyawunsa duk yasake bayyana sbd jallabiyace yasako ash data fito da farin fatarsa ta asalin Igbo.
Kallon kawu yayi yace"
Muje gida kawu.
niba gida zani ba inada abinyi.
Juyawa sukayi Suka barsa
Sanin akwai abinda ke Shirin faruwa yasa yabiyo bayansu Yana zuba masifarsa suna jinsa sukai banxa dashi.
Har tsakar gida Suka shiga Zaki ya kalli kawun yace"
JJ nason auren waccan yarinyar
Meyasa baza'a bashiba?????
Kallon JJ kawu yayi yace'
Sbd Ni ubanta namata miji.
Kallonsa Zaki yayi yace"
Shikenan????
Eh"kawun yada Kai tsaye sbd shima yau Rashin arzikin yakeji.
Juyawa yayi ya wuce JJ yabi bayansa suka fita.
#MAMUH.
*_Buri daya_*
*_Mamuhgee10_*
Tundaga lokacin ba'a sake tayarda maganar ba sai shirin biki sukeyi abinsu musamman iya talatu data fara hidimar bikin gashi dangin mahaifiyarta daga qauyensu sun Aiko kudin nasu gudunmawar har naira dubu arbain da buhun gero da masarasa da dawa kowanne buhu biyu,
Murna gurin dattiya ba'a magana ganin buhuhuwan hatsi jingine yau agidansa abinda bai taba yiba kullum yafison awo idan za'ayi abinci agidansa.
Nadiya kuwa yanxu tasake sakewa da JJ Babu sbd kullum saiya kirata sunyi fira
Tuni taji ita shitake so akan bellon da har yanxu bai sake zuwaba,
Zainab kuwa kullum ita ke sanmata kayanta na kwalliya ta shafa mata.
Tsumi da kayan mata kuwa iya talatu tabatasu marasa sirki Saidai