Showing 63001 words to 66000 words out of 81157 words
kaimu.
Kallonsa dad yayi zaiyi mgn nadey ta rigasa da cewa"
Please dad muje can din first Dan Allah.
Daga Kai yayi suka Kama hanyar gidan kawu lokacin duk masallatai sunfito sallar asuba har gari yafara haske.
A qofar gidan Suka tsaya Allah yasa babu wasu mutane suka shige gidan dukkaninsu suna Jin kewar gidan nadawo musu sabuwa.
Da babbar malum malum dinsa yafito daga dakin iya talatu Yana hamma sbd yau baisamu sallar asuba ba sbd kwana yayi da lalataccen ciki na wani romon Kai dasukaje Suka Sha shida mal idi a gurin wani bikin daurin aurenda ko gayyatarsu baayiba.
Buta ya dauka zai shiga bandaki yaji sallama ahankali ya juyo yayi ido biyu da wadda ko mutuwa yayi yadawo fuskarta Bata bace masa,,,
Zaro qananun idanuwansa yayi zai saki ihu saiyaga Zaki yashigo shima cikin sallamar
Take ya saki butar hannunsa jikinsa na daukar mazari saikga JJ yashigo tareda neyo.....
Hannu ya Dora akai tareda zubewa cikin tsananin tsoro da tashin hankali yafara qwala Kiran sunan talatu Yana cewa"
Talatu zoki bani shahada lokacin tafiyar yazo matacci nake gani wlh,
Gashi nidai wlh ban dandadi dadin arkin danake roqoba Koda na awa dayane na roqi Allah yamin arziki Kona wucin gadin ne Amma Banda rabo.....
A rikice iya talatu tafito dakin tana daura dankwali zatayi magana ganin Wainda ke tsaye saita murza ido tasake murzawa...
A hasale cikin muryar kuka dattiyan yace"
Ke banason diban albarka zakiban shahadane kokuwa saina mutu Banda rabonta...
#MAMUH.
_*Mamuhgee38*_
Hannu iya talatu ta Dora akai Saidai kafin tasamu ikon yin magana jikinta yasaki tafadi a some.
Dattiya na ganin hakan baisan sanda ya fashe da kuka ba jikinsa na makyar kyarar tashin hankali baki yakeson budewa yakira ceto Amma ya kasa gashi dukkaninsu sun jera masa tsaf a gabansa murmushin Zaki daya Saba masa idan zai masa gayya shiyakeyi ko yanxun sbd shiyace karkowa yayi mgn.
Ahankali ya sanya hannu aljihu yayi kamar zai Ciro Abu dattiyan na ganin hakan yasan addar cire ransa ce zaa fitar sai kawai yasaki jiki yayi baya jikinsa na rawa cikin ransa yace gwara nayi sumar qarya koma menene ayi idona rufe.
Da gudu nadey dake hawayen tsananin farin cikin ganin babanta na nan da hallayarsa ta tarosa jikinta tareda fashewa da kuka tana cewa"
Baba karka Suma wlh Babu wasu matacci dakake gani mune gabanka bamu mutuba,
Kabude idanuwanka kagani mudin daine muka dawo gareka.
Dattiya najin hakan jikinsa yasake daukar mazari yasake sake jikinsa yaqi motsawa danyaqara nuna a some yake,
cikin zuciyarsa kuwa kuka yakeyi sosai Yana tsinewa qarfin aljanunsa dasuka hanashi Suma adaidai yanxun sbd hankalinsa ya mummunan sake tashi ganin matacci gabansa su hudu Ras har Wanda rabonda yagansa shekaru fiyeda talatin.
Murmushi Zaki yasaki tareda matsowa gabansa ya tsaya cikin murmushi yacewa JJ ya shafawa iya talatu ruwa.
Gyaran murya yayi Yana kallon kawun ya dago ya kalli nadey dake kuka cikin sakin fuska yace"
Lemme handle this.
Wayarsa ya fitar daga aljihunsa wandonsa ya kunna fitilar wayar ya kashewa kawun ido da ita saiga idanuwan kawun sun fara marmadi alamar idanuwansa biyu.
Cikin sanyin murya Mai taushi Yana kallon nadey yace"
Ayyya sai hakuri fa yariga ya tafi JJ daukesa muje mu rufesa kawai dama yace idan yatafi kar 'dan dabar dayayi zaman gaisuwarsa.....
Jin kawai Sukayi ya fashe da kuka Yana cewa"
Talatu kinci amanar zaman tare dakika Suma kika barni...
Wata irin dariya Suka sake kusan atare Banda nadey da batasan lokacinda takai masa duka a hannuba tana harararsa da hawayenta
Dad ma matsowa yayi yana cewa"
Ku matsa karku bugarwa da Yaya zuciya.
Kamasa yayi ya miqe daidai iya talatu itama ta farfado Suka zaunar dasu a tabarma dad Yana sake kwantar musu da hankalin Babu wata fatalwa dayake gani ko matattu sudin daine.
dattiya da hankalinsa Bai Gama kwanciyaba murya na Yar makyarkyata yace"
Eh nidai kubari nakira Dan uwana mal idi zanfi Jin hankalina ya kwanta.
Zai tashi iya talatu tarigasa tashi sbd tasan bazai dawoba dagacan zasu iya guduwa shida mal idi din tace"
Bari nakira makashi ta katanga.
Wata irin muguwar harara yabita dashi Yana ayyana irin Rashin qaunar dake tsakaninsa da talatu datake masa irin wainnan abubuwan.
Zaki dayafi kowa sanin waye kawun yasaki murmushin dayasa nadey harararsa ahankali
Ya dauke gira daya cikeda mamakinta wato ta manta waye Zaki Dan bazaice Mata haydar ba sbd shi kansa yafi qaunar Zaki akan haydar.
Mal idi da qarfinsa yashigo Yana asuwakinsa babbar rigarsa tun ta jiyace a jikinsa da ita ya kwana da ita yatashi..
Yana ganin baqi masu Kama da turawa yasaki asuwakinsa tareda washe dukkanin haqoransa Yana cewa"
Shikenan mafarkin dattiya yazama gskia da kuzarinsa ya iso shimfidar tareda zagayowa gurin amininsa zaiyi mgn idanuwansa suka sauka akan fuskokinsu yafara binsu daya bayan daya da kallo Yana Dora ido akan Zaki sukaga yayi baya Yana neman kakkafewa.
Dattiya ne ya tarosa Yana basa salati Yana cewa"
Daure danne mal idi wannan duk sharrin talatu ne Kuma zataga matakin dazan dauka.
Cikin yanayi na son fashewa da kuka mal idi ya kalli talatu Yana cewa"
Meya shiga tsakanina dake talatu da kikemin wannan bita da qullin.??
Cikin gyaran murya dad yace"
Wlh anan gurin babu fatalwa dukkaninmu Muna Raye Kuma bamu taba mutuwaba,
Haba Yaya Ina katabajin anmutu andawo ko acikin kafirai bare musulmai,
Tabbas akwai tsoro da bugawar Kai da zuciya kasan mutum ya rasu tsawon Koda wata biyu ne kagansa bare shekaru tabbas wlh akwai furgitarwa..
Daqyar dattiya yabude baki yace"
Wlh Ni ko yanxu mutum ya mutu muka rufosa muka dawo nagansa to akwaifa qura bare shekaru...
Mal idi shidai baisamu na tofawa ba zufan dake masa tsiyaya cikin riga ya sharce sbd wannan shi ake Kira baqar safiya,
Gasu dai an rutsasu cikin gida Babu hanyar gudu to wlh Bari agama dattiya yashiga tsakaninsa da talatu Banda manta alheri dabai tsaya Mata agurin dattiyan ba Aida ba ita zai auraba wata hanne ce.
Sallah Suka farayi dukkaninsu a tabarmar tsakar gidan
Sudai su dattiya na rabe gefe mal idi jira yake yaji abinda bai masa ba yayi ihun kawo ceto.
Dattiya kuwa Banda tagumi daya rafka Yana Kiran Jin idan su dinne yafara zubo nasa zancen.
Aikuwa suna gamawa aka sake gaggaisawa nadey na kusada iya talatu da itakam tuni tafara murna musamman la'akari datayi da cewa nadey dama basuda tabbacin ta rasu tunda Bata tayi.
Ahankali dad yafaro bawa dattiya bayani tun daga ranarda yahadu da ruqayya a Lagos har mutuwarsa da dawowarsa inda yake bibiyan nan gidan haryasan Zaki dansa ne,
Shima yayi gwagwarmaya ta sana'ar Mai kusan shekaru shida kafin yadawo yafada ta masu aikin ginar zinari nanma kusan shekaru goma kafin Allah yayi anan arzikinsa yake gurin aiki yasamu dunqulen zinarenda shine silar arzikinsa.
Ahankali ya koro musu duk labarin nadey Dana haduwarsu da Zaki tareda qarshen dillas...
Cikin tsananin farin ciki iya talatu ta janyo baby z dake jikin JJ ta rungumeta tana hawayen farin cikin tasamu wata zainab din.
Mal idi kuwa gyara zama yayi yana sakin dukkanin fara'ar fuskarsa da bakinsa yafara hamdala Yana kallon dattiya dake kallon nadey baya ko qyaftawa sbd tsananin farin ciki Yana sakin hawayensa dasuka kasa boyuwa.
Zaki yakoma kallo Yana washe baki kafin yasake kallon baby z wadda allah yayi ba agansa zatazo duniyaba duk irin qone qone da azabar dayaci akanta.
Jawota yayi jikinsa akaro na farko da tsananin son qananun yara yakamashi baisan lokacinda ya washe baki ba Yana cewa"
Nadiya wannan 'yarki ce???
Oh ni dattiya Allah nagode maka Ashe dai arzikin ta jikoki zaizo.
Dariya yabasu mal idi yace"
Ai wlh alhaji dattiya kuka da baqin cikin Rashin Zaki da Nadiya ya qare Bari ma naje aikin shelar a dare daya Allah yayi bature.
Washe baki dattiya yayi yace"
Eh daganan ka taramin layin almajirai zanyi sadaka yau dai daya.
Kallon iya talatu yayi haqoransa basa rafuwa yace"
Maza doramin wainar dubu 'daya zanbaki gobe.
Miqewa dukkaninsu Sukayi dad yace zaitafi gida tukuna.
Nadey kuwa nokewa tayi tace anan zata zauna tukuna.
Zakima dakinsu yashiga yaga ya lalace Sam ko shiga baa iya yi Dole ya hakuri yabi dad shida JJ sbd su huta suyi wanka su sake gyarawa.
Bayan fitarsu gyara zama dattiya yayi Yana sake magana Sosai da 'yarsa idan ya kalli ko qafafuwanta wani farin ciki yakeji Wai wannan baqar baturiyar yarsace
Wai har qasashen jirgi tayita Hawa.
Zabura dattiya yayi da kansa baby z na riqe a hannunsa Suka fito Yana cewa abi layi yau shine zai bayar ba basa zaayi ba.
Ganin wainar zataja lokaci yasa ya fiddo duk tsiminsa na kudi yafara raba nera hamsin hamsin
Dasuka qare kuwa yace idi yabasa aro da sauri idi yakwaso duka kudinsa yabasa Yana cewa"
Dama alhaji dattiya wlh munada zuciyar bayarwa Allah ne baiyarda mubayar dinba shiyasa muke a haka.
Wani iska yaji Yana kada babbar rigarsa duk idi yakirasa da alhajin nan
Jiyake kamarma yafi dikko kudi yanxu.
Nadey wanka tayi tashige dakin iya tayi kwanciyarta sbd Yaya dahiru da matarsa suntashi gidan sun canxa gida sbd masifar iyayen nasu dabasu Saba da itaba.
Wani manya manyan dankalin hausa da ake soyawa da doya da fresh yo mal idi yasiyowa baby z dake kallon mutane a tsorace sbd Bata Saba ganin mutane hakaba.
Fresh yo din kawai ta karba shima batashaba riqewa kawai tayi saita yo cikin gida tana qwala Kiran mummynta.
Nadey najinta tayi shiru harsaida iya talatu ta nuna Mata dakin da hannu tashiga ta fada jikinta tana cewa gurin daddynta zataje.
#MAMUH.
*_ZAFAFA BIYAR na kudine idan idan kanason kowanne daga ciki ka nemi wainnan numbers din_*
*_Daurin boye_*
_safiyya huguma_
*_Buri daya_*
_mamuhgee_
*_Wutsiyar rakumi_*
_billyn Abdul_
*_kaimin halacci_*
_Miss xoxo_
*_Sauyin qaddara_*
_hafsat rano_
*08030811300*
*07067124863*
*_Mamuhgee39_*
Manya manyan dankalin dake hannun mal idi ya kalla cikin nishadi yace"
Mal idi waccan me Kama da wankakken karas din kasan bazata iyacin wannan shaquri danne dinba maza hadashi gurin sadaka alhaji idi nawa.
Wata irin dariya da baitaba yiba a rayuwarsa ya sake Yana washe dukkanin haqoransa rigarsa na cika da iskan nishadi Jin dattiya yakirasa da alhaji..
Dattiya yakallesa Yana wani gyara babbar rigarsa hango su mal zailani zuwa yace"
Alhaji idi ga baqi nan inaga gurina zasuzo kasan fa ba damar aji kayi kudi shikenan bakada shaqat sai adameka sauqin abin dai Allah beyini me rawa ba Dan har gyara zansa adanyiwa layin.
Mal idi ma su liman din dake dososun ya kalla Yana cewa"
Alhajin Allah kabari kawai ai Allah yasan tanadin dayayi Mana shiyasa muka debo shekaru a yawon maula sbd muyo ilimin ya abin yake,
Tunda gashi yanzu da bamuyo ilimin abinba ba qaramin wayon jama'a zamu fuskantaba.
Su mal zailani da liman na isowa Suka hau gaishe gaishen barka da arziki tareda sake jinjina alamarin na ubangiji mal idi shine yake zayyano musu labari Dalla Dalla wani abin kamar gabansa akayi
Shikuwa alhaji dattiya gyada Kai kawai yake yana murmushi kamar wani basaraken da fadawansa ke gabansa
Yau Jin kansa yake ko shugaban headquarter Yan sanda da shugaban 'yan drugs zai iya Mari idan yakawo masa shashanci.
Kusan dai shimfidar karbar gaisuwar Taya murna Suka shimfida a gurin har guraren qarfe daya saiga wasu tawagar motocin Yan daba kusan bus bus uku da golf biyu sai mashin mashin tun acikin garin sukayo rally suna ihu take gari ya hautsine da mamaki dakuma murnar dawowar sarkin Yan ta'addan yankin Wanda duk wani Dan daba dake nan da Wainda suka tuba da Wainda Basu tuba ba tuni suka firfito aka hada rally aka garzayo sbd girman sarki da soyayyarsa da Allah ya Dora a zukatansu sbd yawancinsu sarki shine gatansu.
Dattiya na hango tawagar da ihun makamansu da ake gurzawa da titi tuni Suka miqe Yana cewa"
Tofa ai shikenan dattiya kaidai da Yan daba Allah yayi zakayi rayuwa ka Gama wannan mutu ka raba har Ina???""yafada Yana kasa boye murnarsa na ganinsu Dan harga Allah yanzu yasan kowane mutum ko Yaya kagansa Yana rayuwa to da ranarsa Kuma badan sun watseba yasan duk yanda Zaki ke Kare qimarsa da mutuncinsa Suma zasu tsare masa Amma ko yanzu Kam Yana maraba dasu koba komai yanzu shi alhaji ne yanzu Yana buqatarsu sbd tsaro tunda mutane ba dama kayi kudi magauta zasu taso masa tunda gashi nan mal hamisu yaqi zuwa masa barka da arziki Kuma yagansa Yana nan bai fita anguwaba.
Kusan yawansu yasa wasu Basu iya zuwa har gabansu kawun Saidai manya manyan ne suke agaba.
Nanu da Lilo dasu sunny sune agaba Suka qaraso gaban kawu cikeda tsananin farin cikin ganinsa da kewarsa dasuka yi Suka duqa har qasa Suka gaishesu.
Cikin tsananin farin ciki dattiya ya washe baki yahau amsawa Yana saka musu albarka tareda musu adduar kariya akan makamansu ya Dora da cewa"
Zaki baya nan Yana can gidan babansa sunje janzowa Amma nasan yanzu Yana hanya ku jirasa ai Zaki yanzu ne zai buga mulkin.
Ihu Suka dauka ana gwara makamai dattiya na ganin haka sukai saurin shigewa gida kar asamu kuskuren Karo a saresa tun baici arzikin da yayan nasa sukayoba talatu ta cinye ita kadai Yana daga kwance.
Yana shigowa gida nadey nafitowa daga dakin tagamo sallah zatakai baby z fitsari Wai Bata iya shiga toilet dinsu.
Murmushin farin ciki yasake tareda kamo hannun baby z din dayake tana Jin hausar ba laifi sbd mamanta da dady j harma da dad duk hausa suke Mata sbd ta iya kartazo kamar irin haka sundawo Babu hausa abakinta.
Yana nuna Mata fadin tsakar gidan yace"
A gidan nan kinfi kowa gata agurin me gidan wato ni,
Ki duba duk inda ya Miki y tsakar gidan nan kiyi fitsarinki sai a wanke kinji 'yar baturiyar matata.
Zaro ido nadey tayi cikin sanyi tace"
Baba ko Ina fa kace??
Eh Nina fada sbd gidana ne
Ke jeki kiyi fitsarinki a can qofar tsohon dakin uwarki.
Tanajin haka ta Kama bakinta sbd duk dokinta dayake tasan tsaf bazai boye ko danne halinsa ba.
Yana tsaye kuwa baby z tayi fitsarinta iya talatu ta Mata tsarki suna gurin sukaji sallamar JJ yasamu shigowa shi Zaki kuwa Sam mutane sun dabai bayesa sun rufesa gabaki daya sai ihu da hayaniya akeyi titin layin yacika da mutane ko wuceba baa iyayi da abin Hawa sun kashe layin.
Wani irin farin cikine yacika zuciyarsa sbd shi duk wani Dan daba a Dan uwansa na jini yake kallonsa,
Jinsu yake cikin ransa kamar yanda suke jinsa,
Babu wani Dan daba dazai iya Bari aci zarafinsa sbd Suma qaddarar Allah ce atare dasu,
Da wani zai dubesu ya tallafi rayuwarsu wasunsu da dama dasun shiryu sbd wasu Rashin mafitane take kaisu ga hakan tareda qaddara Dan haka shi shine gatansu Insha Allah.
Cikin Jin dadin ganinsa nadey tace"
Yawwa dady j pls Ina buqatan waya zankira Jasmin akwai email dinda nasan zaishigo yau akan new project din hannun mss ambryam Marshall.
Kallonta yayi Yana daukar baby z yace"
Kiyiwa sarki maganar zai baki...sai kawai ya share maganar dayiwa kawu zancen abinda ke faruwa waje Yana qara basa bayanin irin qaunar da akewa sarki.
Wani dadi kawun yasake ji ya washe baki Yana cewa"
Aikai jabiru kabarni nan Ni nasan komai bayan tafiyarku wlh duk wagarewa Sukayi Dole su qaunaceku uwa uba Ni tunda nine ake zaune gidana.
Dariya JJ yayi Yana cewa kawu will Neva change.
Nadey datajisa tasaki murmushi sbd tafi kowa sanin baban nata qarshene.
Zaki har dare baisamu kansaba sbd mutanensa da tuni Suka kasa Suka tsare wasu duk sun tafi Amma duk sauran Wainda suke da anan din sunanan sunyi zamansu Dan kuwa tuni aka bude shagon qofar gidan dayake amatsayin dakinsu tun ada.
Sai bayan ishai yasamu shigowa cikin gidan lokacin baba bayanan iya talatu na dakinta itakuma fitowarta kenan daga wanka ta Dora sabon hijabin iya talatu a kan daurin qirjinta Sam Bata lura dashiba Saida ta fito tsakar gidan gabaki daya taga mutum tsaye Yana kallonta gashi akwai nepa.
Daure fuska tayi tafasa zuwa dibar ruwan wanke qafafuwanta dazata sake Yi ta juya zata shige dakin iya talatu.
Taku daya yayi ya riqota tareda dawo da ita jikinsa ya matseta ta baya tareda shinshina qamshin shower gel din jaggins dake tashi a ruwan wankan jikinta ya lumshe ido ahankali gajiyar jikinsa na qaruwa ahankali ya iya bude baki yace"
Please.....
Haka kawai yace take taji jikinta ya mutu da muryarsa Mai sanyin taushi batasan lokacinda ta lumshe idanuwanta ba tana sakin ajiyar zuciya sonsa na sake tsiro cikin ranta.
Jin jikinta ya saki yasashi juyo da ita ahankali ya zura hannuwansa cikin hijabinta zai......
Wani mugun Bari sukaji anyi tareda guntun salati sukai saurin sakin juna suna juyowa,
Iya talatu ma da sauri cikin tashin hankali ta fito tana cewa"
Waye yafada rijiya naji fadawar Abu a ruwa inji dai ba......
Kasa karasawa tayi sbd tsananin mamakin ganin qatoton durum dinta na ruwa me cin jarka goma dattiya yafada ciki Zaki na kokuwar fiddosa babbar rigarsa ta dabaibayesa ya matsu ya fito ya Fadi abinda ke ransa.
Cikin haushi iya talatu tace"
To Kuma me kakeyi kaje ka fada durum baka saniba???kaifa ba dama kaga arziki shikenan zakabi ka addabi kanka saikaje ka halaka kanka abanza acinye kana daga kwance.
Nadey dake rabe jitayi duk hankalinta na neman tashi sbd tsoro da fargabar Allah yasa Basu yaganiba yafada ruwan.
Ganin yakasa tsayawa aciresa yasa Zaki buga durum din da qafarsa ya fashe ruwan ciki suka tsiyaye sai alokacin ya samu damar zare babbar rigarsa data dabaibayesa ya fito Yana zare qananun idanuwansa dasuka Sha ruwa yayiwa talatu kallo daya yace"
To 'yar baqar fata wacca kullum bataimib fatan kwarai wuce mutafi to ba rijiya na fadaba tunda haka kikeso.
Bayansa nadey tabi da kallon tausayinsa harya shige daki Yana tsiyayar ruwa ta juyo gurin Zaki dake kallonta cikin dauke gira daya wani juya ido tayi ta sakar masa wata hararar datasashi matsota tayi saurin juyawa zata gudu ya riqota tareda Kai bakinsa kan kunnenta Saida ya sakar Mata numfashinsa Mai dumi kafin ahankali yace"
Ina Zaki shigar musu daki kawu na ciki fa.
Rintse ido tayi tareda turesa cikin daure fuska tace"
Babana nefa ka daina yimasa haka.
Dan dauke gira daya yayi yace"
Nikuma kawuna ne abokin adawata akan iyalina.....
A masife ta daga hannu zata turesa yayi saurin yin baya tareda ficewa Yana murmushin da Bai cika yiba.
Kamar munafuka haka ta tsaya a tsakar gidan harya canzo Kaya ya fice tashiga ta shirya Allah ma yasa baby z tabi dady j suntafi gurin dad can zata kwana gurinsu Dan tun safiyar yau aka Kai masu aiki gidan su biyu suka Mata.
Washe gari da safe bayan sun Gama karyawa da wata farar wainar shinkafa dataji Naman kaji wanda mal idi ya siyo musu danshifa tuni yasaki dukkanin bakin tattalin arzikinsa Yana kashe musu sbd yasan year uban ribarsu zaici.
Dattiya cikin shirinsa na fita zuwa kasuwa ya bada rumfarsa ga wani nasiru daya damesa tun jiya yanaso zasuje shida idi suyo musu bankawana.
Kallo iya talatu tabisu dashi cikeda mamakin yanda suka are Suka yafe tun ba'a ce musu gashi din ba.
Yana