Showing 51001 words to 54000 words out of 124209 words

Chapter 18 - FURAR DANKO PART 1

Unknown   

12 Nov 2024

8782

ajiye littafin addu'oin da ke a hanunta da faɗin, “Baka da lafiya ne Hydar?”. Hannun ya janye da ga goshinsa ya ɗan furzar da iska. “Kaina ne ke ɗan ciwo kaɗan kawai Ammah, na kuma sha magani ma. Ina yini”. Maimakon amsawa sai ta cigaba da kallonsa cike da nazari. Ganin yanda ta kafesa da ido ya sashi duban Hawwah cikin son kauda hankalin Ammah ɗin ya ce, “K babu wata damuwa dai ko?”.
         Kanta ta jinjina masa itama da ɗan damuwar ganin yanayin nasa. “Ba komai Yaya Hydar. Sai dai kamar ba ciwon kan bane kawai ke damunka. Ka wani zabge a lokaci ɗaya kamar wanda ya kwanta ciwo.”
   Baiyi mamakin jin furuci nata ba. Dan a duk lokacin da ciwon ya bugesa ba ƙaramar fyaɗa yake masa ba. Ya ɗan sake furzar da iska yana tashi zaune da ƙyau da kamo hannayen su Nasreen. “Ciwon kai ne kawai kin san bai min da wasa”. Badan sun gamsu ba dai suka yarda da hakan. Maryam ce ta kawo masa abinci da faɗin, “Ko sai kayi sallar isha'i”.
        Nan ma iskar ya ɗan furzar da duban kular abincin. Yasan dai shinkafa ce dan ya ga Salim na ci a wajen Umma. Shi kuma sam shinkafa bata da farin jini a wajensa sai dai kawai ya cita dan yunwa. “Ai banama jin zanci abincin nan ɗauke kawai. Ko kuna da ƙullin kamu ki ɗan dama min kaɗan”.
     “Eh akwai. Dama na kunun gyaɗa da Ammah tasa aka markaɗo ɗazun ko shi za'a dama makan”.
     “Yauwa dama min shi ɗin kawai bara naje massalaci na dawo”...

        Ana idar da sallar isha'i ya sake dawowa. Anan yasha kunun gyaɗar da Maryam ɗin ta dama masa Ammah harda badawa a sayo masa ɗanyar awara dan tasan yana so sosai, kasancewar bata da yawa duk kafin ya dawo har an soya. Kusan ma tare suka cinye awarar da Nasreen da ke ta faman zuba masa surutu. Murmushi kawai yake mata cikin ƙarfin hali. Ammah dai da ke ɗan kallon tv duk tana lure da shi. Cikar agogo ƙarfe tara yasa Amma maida channel zuwa NTA, su Maryam ba wani son kallon labaran suke ba sai dai dole. Musamman ma Asma'u. Tashi yay ƙoƙarin yi shima sai dai kanun labaran suka ja hankalinsa. Inda rahoton farko ya kasance akan yanda shari'ar matashin nan Emanuel da aka kama a anguwar Yakasai akan lalata yara ƙanana maza da ya ɗauki tsawon shekaru uku yanayi. Kusan wata huɗu kenan ana tafka shari'ar sai a yau ne aka yanke masa hukuncin bisa jajircewar lawyer ɗin da ke tsaye akan bibiyar hakkin yaran da al'amarin ya shafa. Har tsakkiyar kansa yaji saukar muryarta tamkar a gabansa take kamar ko yaushe. Yanda take magana cikin nuna takaici da kuma jin daɗin samun nasara a shari'ar ya sashi kasa ɗauke idonsa ga tvn. Tambayar da ɗan jaridar yay mata akan miyasa a duk irin waɗan nan cases ɗin in dai tana a cikinsa da wahala bata samu nasara ba, anya ba tana saye bakin alƙalan bane ba ta bayan fage.
       Ƙaramin murmushi da ke sake fidda loɓawar kumatunta duka biyu ta saki tare da yamutse fuska kamar yanda ya santa musamman idan tanajin masifa. Cikin izzar nan tata ta bama ɗan jaridar amsa da faɗin, “Mi zaisa sai na sayi alƙali akan abinda yake gaskiya. Ashe ma karatun da nai akan harkar shari'a da wahalhaluna sun zama a banza kenan in har sai na sayi alƙali akan gaskiya ta. Nasarata itace gaskiyata. Dan bana tsayawa mutum sai na tabbatar da gaskiyarsa. Na kumayi alkawarin cigaba da yaga mutunci da rayuwar duk wanda ya kasance bunsuru mai halayen dabbobi akan mutuncin yaran mutane. Dan ni duk wanda zai iya ƙwatar mutuncin yarinya ta ƙarfi ballema wadda take ƙanƙanuwa bashi da wani suna a gareni face Dabba alade. Yanzu shi wannan da na kai ƙasa ma ai yafi matsayin alade a gareni bamma san mizan kirashi ba. Shege ya baro yankinsa yazo yana ɓarna a namu yankin saboda suna ganin muna haihuwar yara mu saki a titi kamar bamu san ciwonsu ba. Indai akan harkar fyaɗe ne nai alƙawarin ni Mawaddat Isma'il Ibrahim Jiƙamshi sai na hana waɗannan aladun shan ruwa da numfashi cikin salama. Dan nan gaba kaɗan abinda suke lalata yaron mutanen da shi zan koma datsewa da almakashi ƴan ƙaniya. Idan aure kuke so uwarmi kuke jira da bazakuje kuyi ba ko ku tafi gidajen karuwai Mtsowww!!”.
      Ɗan jaridar ya ce, “Turƙashi. Da alama dai Barrister Mawaddat Jiƙamshi ta fusata a wannan karon, masu halin binsiraye sai ku kama kawunanku, inba haka ba za'a sake maimaita gilli da girma bayan wanda akasha da ƙanƙanta. Sai dai a yayin da wannan zantuka na Barrister wasu ke nuna goyon bayanta wasu ƙalubalantarta suke musamman akan zance gilli da zata fara da kanta. Dan haka a yinin yau zantukan barrister suka ɗauki ɗumi da zagaye kafafen yaɗa labarai harma dana yanar gizo aketa tafka mahawara. Ballema da wasu ƙungiyoyin mata masu yaƙi da wannan ɗabi'a ta fyaɗe suka fito muraran da cewar sumafa suna bayanta. Dan zasu sayi nasu almakasan su fara sakawa a jakuna dumin tayata aikin gillin. To ALLAH dai ya ƙyauta, kowa rai yayma daɗi ai baran mai shi ne. Shi dai wannan gashi zai ƙare shekaru talatin cif a gidan kaso bisa tasa mummunar aƙidar mai muni, tare da biyan maƙudan kuɗin da za'a fuskanci lafiyar yaran da ya ɓatama rayuwa”.
        “ALLAH yay ma wannan yarinya albarka da iyayen ma da suka kawo ta duniya”.
    Furucin Ammah a bazata ya maidosa hankalinsa. A tare Hawwah da su Asma'u suka amsa da amin. Har Asma'u na faɗin, “Ammah nima in sha ALLAHU lauya zan zama. Wlhy tun randa na fara ganin matar nan kan case ɗin nan nake jin ƙaunarta da sha'awar nima na zama kamarta.....”
        (Ba Amin ba a ɓoyayyar halayyarta) ya faɗa a zuciyarsa yana miƙewa batare da ya ƙarasa jin zancen Asma'un ba. Sallama yay musu ya fito acewarsa zai sha maganin ciwon kai ne ya kwanta. Sun masa addu'ar samun lafiya, yayinda Ammah ta dakatar da shi da faɗin yazo ta kama masa kan. Gabanta ya dawo ya zauna. Ta kai hannun nata saman goshinsa da ke da ɗumi har yanzu. A hankali ya sauke ajiyar zuciya da har ta iya jiyosa, sai dai batace komai ba dan tun ɗazun zuciyarta ke bata kodai lamarin nasa ne ya motsa bai son faɗa, ko kuma yana son ya motsa ɗin. Sosai tai masa addu'a yanata faman sauke ajiyar zuciya kafin ya miƙe yana jin wata nutsuwa ta musamman na ratsa masa jini da ɓargo. Koda ya koma ɗakin ma magungunan da malam ya bashi ya shashsha sannan ya kwanta. Maimakon barcin sai abinda ya gani a tv ya shiga dawo masa tiryan-tiryan. Shi yama rasa a mizai fassara wannan yarinya. Ita dai gata nan rabi mutum rabi muna mutum. Sai dai kalaman nata na yau sun matuƙar tasiri garesa har yana haɗasu da na jiya data dinga faɗa cikin shirmen buguwar ita ba ƴar iska bace. Bawai ya gamsu da hakan bane. Dan babu ta yanda za'ai irinta mai ƙwalewa da kayen maye ta iya furta ita ƙillatacciya ce ya yarda. A yanzu hakan ma wani sashe na zuciyarsa na kallon kalamanta na ɗazunne kawai a gurbin fuska biyu irin na halayyar ɗan adam na yanzu. Ya ɓoye zahirinsa na mutumin banza, ya shiga gaba-gaba wajen bayyanama duniya shi na kirki ne na ALLAH. Guntun tsoki yaja da lumshe idanunsa yana fatan barci ya ɗauke sa.....

      
     ★★★

★.★.★★

   Tabbas a daren jiya yanda yaga rana haka yaga dare dan ko sau ɗaya bai rintsa ba. Sai faman bulbulama cikinsa hayaƙin cigarette da yay tayi dana shisha. Baya taɓa neman abu ya rasashi, haka ma bai taɓa harar mace sau biyu ba ta zille masa sai a kanta. Duk da ɓacin ran da ya tsinta kansa dalilin rasata a jiya bai ji ko ɗigon sha'awarta ya ragu masa a rai ba. Sai ma ƙaruwa yay yana sake azalzakarsa da sake tunzura buƙatarsa. Neman hanya ta uku ya tsunduma a tunani, sai dai zuciyarsa ta rabu gida biyu. Ɗaya na tabbatar masa ya nema aurenta kawai itace hanya mafi sauƙi. Ɗaya na tabbatar masa bazata amince ba, dan haka kota halin ƙaƙa kawai ya kore ƙishirwarsa, kai koda sakawa a sace masa itane. Ganin ya rasa makamar riƙewa sai kawai ya yanke shawarar neman shawarar abokinsa. Gabanin asuba yay kiransa, bugu biyu kuwa aka ɗaya dan shima a lokacin yana cikin club ne a Abuja..........✍️



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
[9/9, 11:48 AM] +234 906 603 9102: 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣2️⃣



........Motar taima key ta cigaba da tafiya duk da ta fara jin kanta ya ɗauka. Da ƙyar ta iya kai kanta office saboda abinda tasha ɗin ya fara aikinsa. A yanda ta shiga duk da bawai tana layi bane yasa mutane da yawa ɗan binta da kallo. Office kawai ta faɗa tare da maidashi ta rufe harda saka key. Tai jifa da handbag ɗinta da key da takalma har ma da mayafi da ɗan kwali. Zama tai jikin kujera ta dunƙule jikinta waje guda tana mai tura kanta data dafe da duka hannu biyu tsakanin ƙafafunta. Surutai takeyi ƙasa-ƙasa irin wanda idan ba kusa da ita kake sosai ba bazaka taɓa iya fahimta ba...

       _(Kai jama'a shaye-shaye baiyi ba. Shaye-shaye kan zubar da mutuncinka kowane matsayi ka taka. Yana maidaka baya komai ƙarfin ikon ka. Yana ƙasƙantar da kai komai darajarka. Ga lafiyarka kaima da ɓarnar kuɗi. Miyasa ƴan uwa? Mike birgemu? Mike ruɗarmu?. Kuɗi? Ƙawaye? Abokai? Samari? Gata? Kokuwa son zuciya?. Idan duk sune mu tabbata masu ƙarewa ne kamar ba'ai ba. Masu zama labarine kamar basu zo ba. Shaye-shaye wafce mana dukkan muhimman damammaki yake na cigaban rayuwarmu ta duniya da lahira. Kuduba ku gani, duk shekaru irin na Mawaddat bama tasan minene addininta ba, duk da tarin damammakin rayuwa da ALLAH ya bata wannan illar ɗaya take ta shaye-shaye da ke tare da rayuwarta na ƙoƙarin maidata baya. Tun tana ganin tana kiyayewa akan aikinta gashi ta fara kuma a cikin lokacin aikin, mi kuke tunani? Wataran aikin ma sai ta gagara yinsa gaba ɗaya. Da ga sanda ta rasa wannan damar kuma shike nan ta ƙarasa rushewar baki ɗaya sai jiran ta fara bin bola kuma duk da gatan ta😭. ALLAH ka shiryemu ka shiryar mana da zuri'armu da duk masu wannan mummunar ɗabia)._

     
      ★★.....

       Bayan sallar la'asar Daddy da Uncle Yousuf suma suka shiga jerin ƴan sannu da zuwa ga Alhaji Sufi Garko. Ya nuna farin cikin ganinsu. Dan mutum ne da ya san mutuntawa. Kallo yake musu suma irin na ƴaƴa tun kan aurattayya ta shiga tsakanin ɗiyarsa da Daddy balle yanzu ga Mawaddat ta ratsa duk da babu ɗiyar tasa data zama sanadi a duniya. A hirarsu ne ma suke jin cewar Mawaddat ce ta ɗakkosa da ga airport, yana ƙyautata zaton ma har yanzu tana a gidan tare da ƴan uwanta. Daddy yaji daɗin hakan har Uncle Yousuf ma kansa. Basu nemeta bata suka cigaba da hirarsu hankali kwance. Shigowar Alhaji Sulaiman (mahaifin Tajuddeen) ce ta saka Daddy yin shiru, sai kuma ya dubi Alh. Sufi Garko da suke kira da Baba cikin girmamawa ya ce, “Baba inaga bara mu wuce ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne”.
       Alh. Sufi ya tsatstsare Daddy da idanu batare da ya amsa ba, sai kuma ya maida dubansa ga ɗansa Alh. Sulaiman da ya koma can gefe zai zauna. Cikin bada umarni ya ce, “Isma'il koma ka zauna”. Babu musu Daddy ya koma ya zauna ɗin. Ya maida dubansa ga Alh. Sulaiman da faɗin, “Kaima zonan”. Gaba ɗayansu a gabansa sukaje suka zauna kowa na hararar ɗan uwansa kamar wasu ƙananan yara.
      “Ku yanzu kuna ganin wannan rayuwar bazaku ajiyeta ba. Ko a tinaninku har yanzu ku yarane? Ku duba gashin kawunanku furfura duk ta gitta a ciki. Tunda kun gagara faɗamin matsalarku a tsahon shekarun nan ni bazan cigaba da damuwa da sai na sani ba. Sai dai ku sani idan har abinda ya shafeku kuka bari ya shafi zuri'arku bazan yafe ba. Ku shaida hakan ko bayan ƙasa ta rufe idanuna ne”.
    (Anzo wajen) cewar Alh. Sulaiman a zuciya. Dan haka ya gyara zama cike da makirci ya sake raunana muryarsa. “Baba ni ba laifina bane, tunda kowa shaidane na biyo hanyar da zamu sasanta da shi a shekarun baya amma ya koma bayan fage ya zuge yarinya komai ya sake rushewa. Shine ya sakama ransa ni maƙiyinsa ne kawai. Shiyyasa naso haɗin auren Tajuddeen da Mawaddat dan ya tabbatar ba hakan bane ba. Kuma ko a yanzu in har zai amince ya cire komai a ransa ni a shirye nake komai ya zama labari. Mu kuma dunƙule ƴaƴanmu waje guda matsayin ma'aurata dan ƙara danƙon zumincinmu”.
        Wani irin kallon ɓacin rai Daddy ke masa. Sai dai baice komai ba. Alh. Sulaiman da ke masa kallon ƙasa-ƙasa ya saki wani irin makirin murmushi da kashe masa ido ɗaya. Ƙara tunzura zuciyar Daddy tai amma sai ya danne dan jin Baba ya fara faɗin, “Ni kaina zanso wannan haɗin zumincin, zan kuma so ya zama sanadin canja wannan gabar taku. Sai dai kuma bazan so ya rikiɗe daga manufarmu ya koma abinda bashi muke fata ba zumincin ya taɓarɓare ma fiye da yanzu....”
       “Amma Baba ai yaran suna matuƙar son junansu. Dama tun farko matsalarmu ce ta tilastasu haƙura a wancan karon ma”. Alh. Sulaiman ya faɗa yana sake sakin makirin murmushi. Baba da ba ganin abinda ke faruwa yake ba ya kai dubansa ga Daddy da baice komai ba. “Isma'il bakace komai ba. Abinda ɗan uwanka ke faɗa gaskiya ne?”.
          Murmushin mugunta Daddy dake ƙulla murtanin da zai maida ga Alh. Sulaiman ya saki. Cike da sake girmamawa ga surukin nasa kuma ogansa ya jinjina kansa. “Baba duk ina saurarensa. Sai dai na tafi wani tunani ne, kenan Mawaddat ƙarya tamun ko kuwa rashin jin nata ne ya sata kawo min wani a matsayin miji alhalin suna tare da Tajuddeen har yanzu...”
        “Miji?”.
    Alh. Sulaiman ya faɗa kamar a ɗan razane. Shiko Baba murmushi yayi da faɗin “Miji Mawaddat ɗin ta fitar?”.
   “Eh Baba. Dan dama dawowarka muke zaman jira muzo maka da batun. Saboda yanata ma damuwar turo magabatansa amma ina dakatarwa da cewar har sai ka dawo tukunna”.
        “Wlhy ƙarya kake Isma'il! Wannan makirci ne ka ƙulla dan kar Mawaddat ta auri Tajuddeen, an gaya maka tsoronka nakeji wai ne da na gagara ɗaukar mataki a kanka tun a baya”. Alh. Sulaiman ya faɗa yana miƙewa zumbur. Gaba ɗaya falon suka zuba masa ido. Sai kuma duk ya daburce dan fahimtar yana neman yin ɓaran ɓarama fa.
   “Ka ɗauki mataki a kansa! A wane dalili Sulaiman?”. Baba ya katse shirun. Kame-kame Alh. Sulaiman ya fara, hakan ya bama Daddy damar sakin murmushin mugunta. Sai kuma ya dubi Baba. “Baba ƙyalesa kawai shirmensa ne. Kasan shi Sulaiman idan ya fusata akan abu baida fahimta. Sannan ya iya sakin duk maganar da tazo masa a baki koda ba hakan bane a ransa. Ni dai ba ƙin haɗin auren Mawaddat da Tajuddeen nake ba. Kawai shashancin da tayi ne na kawo min wani matsayin miji da har na sanar da nawa dangin dama jiranka kawai muke ka dawo a tsaida biki alhalin tana tare da Tajuddeen kuma ne yasa ma harna faɗa. Amma ayi haƙuri ni zanje ga babanta Yousuf mu sameta a nutse na mata tambayoyi dan nasan halinta bajin magana take ba. Kaga idan Tajuddeen take so ni bazan hana ba, sai nasan dabarar yi wancan ya janye a rabu lafiya mutuncin kowa bai zube ba....”
       “Mizai hana w kirata yanzu ayita ta ƙare”.
   Cewar Alh. Sulaiman. Shiru kamar Baba bazaice komai ba. Sai kuma ya nisa a hankali da faɗin, “Ku dukanku kunzo da shawara mai ƙyau kuma duk na gamsu da maganarku. Sai dai muyi haƙurin goben sai a zauna a nutse kan maganar. Amma yanzu ina son a kiramin Mawaddat da Tajuddeen”.
      Sosai hankalin Daddy ya tashi, amma ya danne a ransa yana mai addu'ar ALLAH yasa kada Mawaddat ta watsa masa ƙasa a ido. Dan shifa bazai taɓa yarda ya haɗa zuri'a da Sulaiman ba. Shi kansa Uncle Yousuf zancen Yayan nasa ya sakashi a ruɗani. Duk da yasan akwai ƴar tsamar da har yanzu bai san tushen ta ba tsakanin ɗan uwan nasa da Alh. Sulaiman bai san dalilinsa na ambaton wani ba matsayin Mawaddat ta kawo bayan yasan ba hakan bane ba. Kusan a tare suka saki ajiyar zuciya shi da Daddy lokacin da ɗan aiken ya dawo ya tabbatar musu ai Mawaddat ance ta tafi tunma ɗazun. Alh. Sulaiman kuwa bai so haka ba. Amma baice komai ba, sai dai a ransa yana ƙudurta duk Daddy yayi ya gama a wannan karon sai Mawaddat ta zama matar Tajuddeen.....

        😂Anayi muna cin tuwon masara miyar kuka🤪.

              ★★..★★

     Yau gaba ɗaya a gida ya yini saboda tun daren jiya Uncle Yousuf ya ce masa karfa ya fito aiki yau ɗin ya bari har sai yaji ƙarfin jikinsa. Hakan ya saka shi yin zamansa tunda dama sunyi faɗa da ogar tasa. Ɓoye kansa yay a ɗaki ya sha barci, hakan yasa babu wanda yasan yana gidan ballema ya tuhumesa tunda bai sanar musu abinda ya samesa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login