Showing 81001 words to 84000 words out of 124209 words
yau Alhaji ya ɗaura masa aure......”
“Aure kuma? Wai kina nufin ɗan wajen Hafsatu”.
“Aminiya inba shi ba wane shegen tantirin yaro ne ke bani wahala a gidan nan. Kedai shaidace akan kuɗin dana dinga kashewa ga al'amarinsa sai da ƙyar muka samu malamin nan na zuru yay mana aikin da ya ci. Yau kuma wai sai ga Alhaji da wannan mummunar labari, abu mafi ƙona rai ka ƴar masu garin Kanon fa......” ta kwashe komai ta sanar mata har halin da Smart yake a ciki yanzu.
Sosai Hajiya Naqiba ta jinjina al'amarin. Dan tasan aikin Malam na-zuru kam garanti ne. Cikin jimami da taya ƙawar tata takaici ta ce, “A lallai dole ki shiga ruɗani Hajiya Yahanasu. Kuma bamuga ta zama ba dole mu shiga Zuru a gobe. Ƴar gidan Alhaji Isma'il Jiƙamshi fa? Kin san kuwa wanene wannan mutum? Shahararren mai arziƙi ne wlhy balle kuma wai jikan Alhaji Sufi Garko masu juya ƙasar nan a yanda suke so. To banda masifa ma irin ta wannan hatsabibin yaron ina ma suka haɗu? Ai in har kuka bari wannan yarinyar ta tare to kun gama kaɗewa, dan Hafsatu ta gama yi muku fintinkau. Shi ko kinga ai batun wani ƙwallo ya ajiye kuma ga komai a gashe sai dai ci. Ai ko ƙasar nan bana zaton zai cigaba da zama kuma....”
“Aminiya kina ƙara rikitani wlhy. Bakiji yanda kaina ya ƙara ɗaukar zafi ba. Yanda na tsani mutuwata haka na tsani yaron nan a gidan nan dan na jima da fahimtar son da Alhaji ke masa. Ga abinda malamin can ya faɗamin a kansa tun yana ɗan ƙaraminsa.......”
“Kinga ki kwantar da hankalinki, kawai dai duk ma yanda za'ai kiyi gobe ki fito muje mu wajen Malam Na-zurun”.
“To shike nan. Bari naje kar a juya ba'a ganni ba kuma a zargi wani abun kin san dai munafukan matan gidan nan musamman ma shegiyar Fatin can (aunty amarya) da take abu kamar Hafsatun ce ta haifeta, na rasa mitai mata masheranciyar take mata irin wannan biyayyar itama shegiyar ta biyu”.
“Duk zamuyi maganinsu. Itama sai a kaita ai gobe a sabunta mana aiki a kanta kawai.”
Sosai Umma taji daɗin wannan shawaran. Dan haka ta ƙara jerama aminiyar tata godiya sannan sukai sallama jin Hannatu ƴarta na ƙwala mata kira da ga falo.....
(Ke kuma Umma haka kike ashe. ALLAH ya rabamu da ɓatan basirar zamowa mushrikai akan kishi da abin duniya🤦, duk abinda ka gani rubutacce ne da ga ƙaddarar mutum. Kai baka isa canjashi ko sakawa ba. Dan mi zakaita wahal da kanka da ɗorama kai zunubi ga asarar kuɗi. ALLAH ka shiryar damu dai🙏).
____________________
A falon Daddy Uncle Yousuf ya samu Mawaddat kwance, yanda tai lamo sai ya fahimci kamar kuka ma tayi. Tausayi ta bashi, dan zuwa yanzu ya ƙara fahimtar akwai wani tabo a zuciyarta da take ɓoyewa kuma ya kamata ace sun sani. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da aro murmushi ya azama fuskarsa yana kaiwa zaune da kiran sunanta. Idanunta da ke a lumshe ta buɗe tana kallonsa. Sai kuma ta tashi zaune fuskarta har yanzu da alamar damuwa ta ce, “Uncle You sai yaushe ƴan uwana zasu daina jin tsananta ne?. Na rasa mina musu da girma haka. Na rayu ba'a cikinsu ba, kullum cikin begen son ganinsu neke a zuciyata duk da basu taɓa zuwa inda nake ba sai a hoto idan ka nuna min su. Amma sanda na iso da zumuɗin ganinsu fuskar da suka fara tarbata da shi shine na tsana. Har yanzu kuma irin wannan tsanar nake gani a cikin idanunsu bata taɓa sauyawa ba. Su Amrah ne kawai ke sakewa da ni, suma a wasu lokutan nasha samunsu suna zagina sai dai ban taɓa nuna musu na sani ba. Kodai dan ba Mommy ta haifeni ba kamar su shiyyasa basa sona....”
Kai Uncle Yousuf ya dafe, sai kuma ya ɗago duk a lokaci guda yana girgiza mata kansa. “No Mawaddat ba haka bane ba. Amma ina so ki kwantar da hankalinki zamuyi magana a nutse. Ni yau ɗin ma naga duk kin zama kamar wata raguwa kamar bake ba. Bakin duk ya mutu kar fa Aliyu yay miki dariya idan ya ganki haka yay zaton kin karaya ne”.
Baki ta tura gaba tana yamutse fuska. “ALLAH ya kiyaye Uncle You. Ni kawai yau bana jin daɗin raina ne. Ni bari ma na shiryo na bika wajen Aunty Saliha nai weekend a can kawai”. Kafin yace wani abu harta fice a falon. Ya buɗe baki zai kirata Daddy da ke fitowa a ɗaki yace, “Yousuf barta kuje can ɗin kawai.”
“Yaya yanzu fa tana da aure. Kasan ko bai dace ba. Amma ina zuwa ”. Yay maganar yana zaro wayarsa. Idanu Daddy ya tsira masa cike da zargi, sai dai bai ce komai ba. Tsaf Uncle Yousuf ya lura da shi, amma yay biris ya cigaba da kiran no ɗin Smart. Sai dai har ta yanke ba'a ɗaya ba. bai gajiya ba ya sake kira. Maryam ce ta ɗaga, cikin nutsuwarta tai sallama tare da gaishesa. Sannan ta ɗora da faɗin, “Yayan baida lafiya ne”.
Cike da mamaki Uncle Yousuf yace, “Baida lafiya kuma? Aliyu fa nake nema”.
“Eh shi ɗin”. Ta sake faɗa da ladabi. A rikice Uncle Yousuf ya ce, “Ya salam miya samesa? Yanzu fa babu jimawa muka rabu da shi. Kinga ina zuwa”. Ya faɗa yana yanke wayar. Number Abba yay kira, bugu biyu kuwa ya ɗaga suka gaisa da sakema juna bangajiya. Sannan Uncle Yousuf ya ɗaura da tambayar abinda ke bakinsa. A nutse Abba yay masa bayanin komai, tare da ɗorawa da faɗin, “Al'amarin Aliy ya fara bani tsoro a wannan gaɓar, dan in har ba shafar junnu ba to lallai dole akwai sihiri mai ƙarfi jikin yaron nan. Dan sai a yau na sake fahimtar wani abu. Halan ma auren da muketa matsa masa yayi amma yaƙi duk akwai dalili, sai yau da ALLAH ya kawo iyaka akayin kuma yazo cikin bazata shine hakan ta kasance?”.
Numfashi Uncle Yousuf yaja mai ƙarfi. “Tun lokacin da Hameed ya bani labarinsa na fahimci makamancin hakan gaskiya. Kuma malamin nan dama ya faɗa cewar sihirine mai ƙarfi tattare da shi wanda aka ƙulle duk al'amarin rayuwarsa masu girma. Sai dai kuma addu'a tafi ƙarfin komai da kowa, wata rana duk ƙarfinsa zai zama ya warware in har aka cigaba da gayama ALLAH shi maji roƙon bayinsa ne. Kuma insha ALLAHU muna fatan warwarewar lamuranne suka fara zuwa”.
“To ALLAH ya tabbatar da hakan Yusufa”.
“Amin ya rabbi malam. In sha ALLAHU yanzu zan zo gidan tare da malam ɗin ku kwantar da hankalinku”.
Bayan Uncle Yousuf ya ajiye wayar yayma Daddy bayani. Shima ya nuna alhini da jin tausayin Aliyun. Sai kuma ya ɗora da faɗin, “Maganganinka sun sani a ruɗani fa akan yaron. Har kayi masa sani irin haka dama Yousufa?”.
“Yaya na san fiye ma da haka akan Aliyu. Sai dai yanzu bamu da lokaci, amma ka bini bashi wataran zan maka bayani insha ALLAHU”.
Daddy bai ja zancen ba kawai ya gyaɗa masa kai da ƙara yima Smart addu'ar samun lafiya. A haka Mawaddat ta dawo ta samesu. Bai mace mata komai ba sukai ma Daddyn sallama suka wuce. Ko a hanya bai sanar mata halin da Smart ɗin ke ciki ba ya kaita gida ya ajiye. Sai dai bai shiga ba ya koma shi ita kuma ta shige cikin cike da zumuɗin son ganin Deen ɗin ta. Dan tana matuƙar ƙaunar yaron ita dai...
Bayan sallar magrib kaɗan Uncle Yousuf da Hameed (Coach) suka iso gidan tare da Malam da sukaje har gida suka ɗakko. Har ɗakin Smart ɗin suka shiga bayan su Gwaggo Sa'adah sun fito. Malam ya ƙara masa addu'a sosai tare da kwantar musu da hankalin in sha ALLAHU komai zai dai-daita. Yau ɗin ma dai ruwan addu'oin nan ya sake basu da sake jaddada musu dage masa da addu'a shi kuma ya ƙara dagewa da yin azkar da sadaka. Har suka bar gidan Smart bai farka ba yanata barci, sai kusan ɗaya ya farka da azababben ciwon kan da dole sai da aka nemo wani ma'aikacin asibiti a anguwar saboda yanda yake ta complain kansa kansa kamar zai fashe. Dubasa yay da yi masa allura ya kuma saka masa ƙarin ruwa sannan aka samu wani barcin mai nauyi ya sake yin gaba da shi.........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
[9/18, 12:38 PM] +234 703 706 8372: 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣7️⃣
.......*_WASHE GARI_* da asuba da ƙyar Lulu ta iya tashi sallar da Uncle Yousuf ya sa aunty Saliha ta tadata yi. Dan kuwa dai daren jiya suna gama hira da Aunty Saliha ta shige ɗaki sakamakon dawowar Uncle Yousuf gidan a gajiye ta samu sirof ɗin ta da wani ya kawo mata a gidan bayan sallar isha'i ta fita a sulale ta amso bada sanin aunty Saliha ba har kwalba uku tasha. Dan yanda kanta yau ya ɗauki zafin nan ta tabbatar sai tazo kwanciya komai zaita dawo mata a rai ta kwana cikin damuwa. Sam bata buƙatar hakan kuma. Ga shi dama abin yazo mata a dai-dai wato weekend. Dan dama fa duk weekend kusan sune ranakun da tafi ƙwalewa son ranta ta sha barcinta. Kafin a gane tana shaye-shaye sai aita ɗauka gajiyar aiki ce ke sata mahaukacin barcin da take sha. Balle ma Daddy kan hana a tadota a cewarsa a barta ta huta. Hakan na bata dama ƙwarai da gaske ita kuma ta sha abinda take son batare da sun gane komai ba.
Sabon barci ta sake dasawa har kusan sha ɗaya sai da Uncle Yousuf nan ma yasa Aunty Saliha tadata. Tun a yanda ta fito ya fahimci wani abu ta sha a jiyan, bai ce komai ba kan haka duk da zuciyarsa tayi babu daɗi sai cemata da yay ta koma ta shirya yana jiranta zata rakashi wani waje. Kai kawai ta gyaɗa masa da komawa ɗakinta dan tana da ɗaki dama a gidan. Ta jima a toilet ɗin kafin ta fito tanata ƙamshin shower gal mai ƙamshin tsiya, dan anan bata da turarrukan wanka duk ta ƙarar da su ta kuma manta ta kawo ta ajiye dan bata iya cikakken sati biyu batazo nan ta kwana ba ko yin weekend. Tana tsaka da shiryawa Deen ya shigo. “Akku mai bakin magana kenan”. Ta faɗa tana kallonsa. Ai ko yay zaman dirshan ya fara tsiyaya mata surutu itako tana biye masa dan kaf ƙannen nata tafi ƙaunar yaron fiye da kowa. Shima kuma yana son aunty Lu ɗinsa. Sai da ta gama shirinta tsaf cikin doguwar riga ta atamfa da tai masifar lafe mata a jiki kamar wadda akaima fenti. Dan Lulu koda ta saka kayan hausawa irinsu lass atamfa material zaka samesu dai babu wani ɗinkin mutunci a tare da su. Shiyyasa ma kayan basa wuce fitet gwan ne. Dan ko skert da riga ba sosai ta cika yi ba, inma tayin zaka samu suma dai sai sun mata ɗamm kamar zatai nishi su yage. Kasancewar kuma tana da ƙyaƙykyawar sura sai sukan mata ƙyau kamar an haliccesu a jikin nata ne. Dan telan nata kam ƙwarone wajen iya ɗinkin shegantaka. Ba kuma kowa ya haɗata da shi ba sai Nadiya. Yau ma ko takan ɗan kwali ba'abi ba dan dama Amrah ce a mafi yawan lokaci kan mata ɗauri idan tai irin wannan dress ɗin. Sirrin mayafi milk color da ya shiga da zanen atamfar ta yana kawai bisa kai aka ɗora ƙaton google tare da dogayen takalmanta. Dan ƙyau kam tayi ƙyau ga wani mahaukacin ƙamshi mai ɗaukar hankali na tashi. Uncle Yousuf bai fito ba harta kammala breakfast da ba wani na kirki taci ba. Dan shaye-shaye ya gama cinye Lulu ko abincin kirki bata iya ci a rayuwarta. Barta da son cin chocolate kamar shazumamu, dan ko a handbags nata baka rabata da su bayan ƙwayoyinta na shaye-shaye. A tare aunty Saliha da Uncle Yousuf suka sakko da ga sama. Dan haka su duka suka zuba mata ido. Aunty Saliha ce ta fara faɗin, “Babyn Uncle badai da kayan nan zaki fita ba musamman ma ɗan mayafin nan?”.
Sosai mamakin furucin aunty Saliha ya sata waro idanunta manya da suka juye. Sai kuma ta kalla kanta. Dan tasan dai ba yau ta saba fita a kahaba ai. “Mamy miye laifin kayan nan kuma?”. Ta faɗa fuska a turɓune. Murmushin aunty Saliha tayi da faɗin, “Haba dai Mawaddat ai yau ba jiya bace. Ko kin manta yanzu ke matar aure ce”.
Wani mugun yamutse fuska tayi dan ita tama manta da wani batun auren. Musamman da ya kasance abinda tasha a daren jiyan ya mantar da ita duk wata damuwarta. Kamar Zatai magana sai kuma tai shiru jin Uncle Yousuf yay gyaran murya da faɗin, “Kinga barta kawai muje ai a mota ne, kuma babu inda zata fita sai a can”.
Sosai aunty Saliha ta zubama mijin nata ido da mamakin abinda ya faɗa. Dan abu ne da batai zaton ji daga garesan ba sam. Kasa sake magana tai har suka fice Lulu na mata bye ita da Deen da ya maƙale zai bita. Ta ja ajiyar zuciya da faɗin, “Ai masa sannu sai kun dawo”. Da kai kawai Uncle Yousuf ya amsa mata yana ficewa. Yasan abinda yay ɗinne ya ɗaure kanta. Sai dai shima yanada hikimarsa tayin hakan bawai bai san abinda yake yi bane.
A motar tuƙinsa yake tayi, yayinda ita da Deen suketa surutunsu da dariya. Dan indai Lulu da Deen ne kam babu mai shiga tsakani. Sai ya ƙulleta da haushi ta mammakesa da kiransa mai shegen surutu kamar akku. Sun tsaya a wani ƙaramin super market Uncle Yousuf ɗin ya fita shi ɗaya. Bai jima ba ya dawo, sai kuma a wajen masu fruits, nan kam da ga motar ma yay bayanin abinda yake so aka kawo masa ya bada kuɗin suka cigaba da tafiya. Lulu dai bata tambayi ina zasuje ba. Hasalima hankalinta gaba ɗaya naga Deen ne. Sai da motar ta tsaya ne sannan hankalinta ya dawo ga inda suken. Kallon anguwar take a ɗan yamutse, duk da ba wani datti bane ko makamancin hakan, hasalima titi ne shimfiɗe da ya miƙe samɓal kasancewar gidan su Smart na a farkon shiga layinne. Sai dai yanayin gine-ginen da kai kawon mutane dana ababen hawa riiiii yasa zaka tabbatar dai irin tamu ce dangin malam Shehu....
“Papa nan fa?”
Cewar Lulu a gatsine.
Maimakon bata amsa wayar da yake dannawa ya kai kan kunne. Ta daiji yana amsa gaisuwa, sai dai bata fahimci mi ake cewa da ga can ba. Sai kuma taji Uncle Yousuf ɗin na cewa, “Kai dai kaɗai ne a ɗakin ko? Okay gani nan shigowa”. Daga haka ya yanke wayar tare da buɗe murfin yace, “Oya ku muje”.
“Uncle.....”
“Shiiiii...” yay saurin katseta tare da mata alamar zip a baki. Dole ta haɗiye abinda take son fadar dan babu alamar wasa akan fuskarsa. Shi da kansa ya kwashi ledojin, ita kuma ta fito riƙe da hannun Deen tana ta faman yamutse fuska. Sauƙin ma babu kowa a ƙofar gidan. Wanda ke iya hango su kuma ba sosai suke iya ganinsu ba duk da harda masu leƙe saboda son gulma irin ta mutane. Soron ta dinga bi da kallo duk da shima dai fes yake gashi kuma lailaye da sumintinsa. Hakama koda suka shigo gidan ko'ina fes babu wani datti, ga gidan shiru babu yawan hayaniya sosai dan yaran sun wuce ismaliyya, sai ma matan anguwa da wasu a dangi dake ta faman shigowa yin ALLAH ya sanya alkairi da auren Smart ɗin da ba'a san da shi ba. Sai kuma wanda suka san baida lafiya na ɗorawa da jajanta yaya jiki musamman maƙwafta. Anan dai ta inda suke basu haɗu da kowa ba har suka shige sashen ɗakunan samarin gidan da ke a farkon shiga. Anan sun ɗan haɗu da wasu. Bakowa bane kuma sai Mubarak da kema Smart wankin kayansa na ciki, sai Abdull a gefensa yana kallon film a waya da eirpiese a kunnensa. Mubarak ya shiga musu sannu da zuwa cikin girmamawa dan ya gane Uncle Yousuf, itako Lulu dama kallo guda tai musu ta ɗauke kai gefe a ranta tana ƙunƙunin ina ne nan Uncle You ya kawosu. Duk da dai gidan babu wani makusa tare da shi a ɓangaren tsafta a ginensa dai na masu ƙaramin ƙarfi ne. Ita ba hakanne ya dameta ba, kawai bata cika son zuwa irin wajejen nan bane, shiyyasa ko aikinta ya ratsa da hakan zaka ganta cikin rashin sakewa da son a gaggauta abar wajen. Abdull da Mubarak ya zungura shima ya shiga gaishesun. Duka dai Uncle Yousuf ne ya amsa da tambayarsu ko Aliyu na nan? Duk da yasan yana nan tunda dai yayi waya da shi. Sun amsa masa da girmamawa Abdull ya tashi yay musu iso.
Tunda Uncle Yousuf ya ambaci Aliyu ta kafesa da idanun son jin ƙarin bayani, sai dai bai kulata ba yay gaba dole suka bisa a baya. Yana zaune a saman