Showing 45001 words to 48000 words out of 124209 words
sosa masa zuciya da tsaya masa a rai. Ammah dake zaune a falo Nasreen a cinyarta tana shan kunu kallo ɗaya tai musu ta maida hankalinta ga Nasreen ɗin. Zama yay kamar yanda Hawwah da ke sharar hawaye itama ta zauna. Idanu ya ɗan zuba mata tare da furzar da huci kaɗan. “Shi wannan kukan babu amfanin da zai miki, bakuma zai gyara abinda yake faruwar ba. Kisama ranki haƙuri da nutsuwa, dan bazaki koma wannan gidan ba har sai tasan darajarki. Idan kuma kina ganin ba'ai miki gata ba a hakan dan naga k da mijin naki duk shashashu ne ga hanya nan zaki iya binsu” Daga haka ya miƙe.
“Kayi haƙuri Yaya ni banga laifinka ba, kuma nagode da ƙoƙarinka a kaina”.
Komai baice mata ba, sai duban Ammah da tai kamar bata ɗakin da yay. “Ammah ni zan koma”.
“ALLAH ya tsare ya bada sa'a”. Tace masa batare data ɗago ba. Da Amin ya amsa yana ɗan lakatar kumatun Nasreen da itama tai masa a dawo lafiyar. Da ga haka ya fice abinsa badan yasan ina ya kamata ya dosa ba tunda boss ɗin tasa ta korosa yau.
Sai da ya fito gaba ɗaya da ga layin nasu zuciyarsa ta kwaɗaita masa zuwa ma ya duba trainers ɗinsu. Dan kwana biyu basuga juna ba. Waya ya ciro tare da ɗan ƙura mata ido kamar mai tunani, sai kuma ya ɗan ɗage kafaɗa tare da kai wayar kunnensa bayan yay dailing number daya lalubo. Bugu uku aka ɗaga, yay ƙaramin murmushi da faɗin, “Barka da hantsi sir”. Amsar da aka bashi da ga can ta sakashi sakin murmushi. Sai kuma ya ɗan shafo kansa alamar jin kunya tamkar yana gabansa. “Am sorry Sir na ɗauka laifina. Yanzu ma ina son zuwa gaishekanne shiyyasa nace bara naji inda kake”. Ya ɗan yi shiru alamar saurare. Sai kuma ya amsa da “Okay gani nan zuwa in sha ALLAHU”.
Tafiyar mintuna ƙalilan da bai wuce ashirin ba ta kaisa babban stadium ɗin da coach ɗin nasa yace masa yana acan. Wajen ya ƙayatu matuƙa. Babu yawan hayaniyar mutane sai isu-isu ƴan wasa da ke ta tsalle-tsalle alamar training sukeyi saboda wasan sada zumunci da suke shirin zuwa kudancin ƙasar. Tunda ya shigo wajen ɗaya da ga cikinsu da ya fara ganinsa ya saki wani irin fito daya jawo hankalin sauran suma. *_“Capten!! Carpten!!”_* suka shiga faɗa cikin ihun da ke nuna tsantsar farin cikin ganinsa. Murmushin Smart ne ya sake faɗaɗa, shima ya shiga ɗaga musu hannayensa duka biyu har ya ƙarasa gaban Trainers ɗin nasu da ke kallonsa shima da murmushi. Har cikin rai yana matuƙar son yaron, ya kuma ci buri a kansa dan Smart ya iya gara ƙwallo mai suna ƙwallo ta gaske, dan ma mun kasance a ƙasa irin ta Nigeria da mai alfarma yafi ma'iyi da tuni wani labarin ake akansa ba wannan ba. Amma duk da haka shima ya damu wasu dama na barin ƙasar ƙaddara ta toshe su. Sai dai ALLAH mai hikima duk da tarin damammakin da yaron ya samu tun yana da shekara goma sha takwas komai yaƙi motsa kansa a inda yake. Hannunsa ya kamo da ga hanashi risininawar da yay niyyar yi, “Yarona irin wannan ƙiba haka anya kuwa kana motsa jiki?”.
A yanda coach ɗin yay maganar ya saka Smart yin ƙaramar dariya da shafa kai yana ɗan dudduƙar da kansa da faɗin. “Sir ina nan a yanda ka sanni girman rigane kawai”.
“Bari nace to. Amma badan na yarda ba. Ykk to ya kwana biyu? Tunda ka samu aikin nan ka ɓuya gaba ɗaya ko?”. Ya ƙare maganar yana jan hanunsa suka ƙarasa kan wasu kujeru da ke gefe kaɗan. Smart da har yanzu bai bar murmushi ba ya ce, “Sir aikinne bai barin motsin kirki. Amma kuna raina sosai”.
“To Alhamdullah babu dai wata matsala kuma ko?”.
“Da sauƙi dai Sir”.
“A cigaba da haƙuri, komai yay farko zaiyi ƙarshe. Fatanmu dai ALLAH ya warware mana abinda bamu da ilimin sani akansa”.
“Amin Sir”. Ya faɗa cikin damuwa idanunsa akan teammate ɗinsa da ke ta tsalle-tsalle su har yanzu. Hira suka cigaba da yi da oga wani kaso na hankalinsa na ga teammate ɗin nasa dai. Kiran wayar coach da akai ta sakashi miƙewa ya ɗan matsa a wajen. Dai-dai nan ɗaya daga cikin ball ɗin da suke training ɗin da ita ta gangaro wajen filin har inda Smart ke zaune. Kamar wanda aka tsikara ya miƙe da alamar tsumin ya motsa. Cikin wani irin salo da iya ƙwarewa a harkar ya buga ball ɗin tamkar abin almara bata sauka ko ina ba sai cikin raga. A take wajen ya ruɗe da ihunsa, kamar waɗanda ake juyawa da remote suka raba kansu yanda ƴan ƙwallo kanyi a cikin fili yayin wasa. Ƙarasa shigewa cikin filin yay shima cikin zafin nama da jin shauƙi a ransa, dan da gaske ball itace hubby na Smart. Tana sakashi karsashi da nishaɗi maƙurar ƙurewa.
Juyowar coach da ya kammala waya ya sashi waro idanunsa waje sosai na ganin abinda ke faruwa. Sosai ya rikice dan yasan da wahala a wanye lafiya... Ilai kuwa kafin ya kai ƙarshen tunaninsa da yay dai-dai da sake saka ƙwallo ta biyu a raga da Smart yayi ya wani ƙwalla ƙara hannayensa duka biyu dafe da kansa. Kafin su isa kansa ya zube ƙasa a sassanƙame. Hankalin coach idan yay dubu ya tashi, haka ma sauran teammate ɗin nasa duk sun rikice. Babu ɓata lokaci suka fiddashi a filin coach na musu faɗan miyasa suka barshi ya shiga tunda sun san matsalarsa. Su dai basu da tacewa dan mai afkuwa ta riga da ta afku kuma. Sai fatan a kiyaye na gaba dai.
Duk wani kalan taimakon da sukan masa idan matsalar ta samesa ita Hameed yay masa, sai dai kamar yanda aka saba babu alamar za'a samu kansa a yau ɗin. Sosai ya sake shiga damuwa, ina daɗi da ga zuwansa gaishesa a rarraɓesa a kaima iyayensa shi a haka. Dole yay kiran ƙaninsa Ahmad aboki ga Smart ɗin kenan akan yazo suje gidan su Smart ɗin. Da mamaki Ahmad ke tambayar yayan nasa ko wani abu ne ya faru? Bai wani tsaya kwana-kwana ba ta sanar masa. Hankalin Ahmad ya tashi, babu shiri ya baro office ya nufo stadium ɗin.
Yana ajiye wayar kiran babban amininsa Yousuf Ibrahim Jiƙamshi na shigo masa a waya (Uncle Yousuf) kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin dan sunyi da shi zasu haɗu shi shaf ma ya manta sai da yaga kiran. Furucin Uncle Yousuf da ke faɗin, “To baban ƴan tamaula ALLAH yasa dai ka gama da yaran naka dan bana son zuwa nai zaman jiranka zan koma office saboda baƙi da nake tsumaye bayan azhar”.
Cikin damuwa coach ya ce, “Wlhy ni nama manta da da batun zuwan naka ina nan a rikice”.
“A rikice kuma a kan mi?” Uncle Yousuf ta faɗa cikin mamakin aminin nasa.
Shima amsa ya bashi da faɗin, “Wlhy Aliyu ne yazo mu gaisa fa na ɗan tashi amsa waya ban san yaya akai ba ya shiga cikin fili ka gansa nan sharɓan babu alamar rai tare da shi”.
“Ya Arrahaman! Aliyu dai Aliyu nawa Smart Mawashi?”.
Sai yanzu ma shi coach ya tuna ashe Aliyu a ƙarƙashin abokin nasa yake a yanzu. Dan haka ya bashi amsa da cewar, “Yess! Yes! Shifa wlhy”.
“Ya Salam gani nan a hanya”.
Kusan a tare Uncle Yousuf da Ahmad suka iso wajen. Kowanne ya fito a motarsa da sassarfa zuwa inda suke zagaye da Smart da ke kwance a ƙasa kansa bisa jikin coach da ke faman shafa masa ruwa yana fatan ya farfaɗo, dan bai son su kai shi gida a wannan yanayin musamman daya tuno irin tashin hankalin da Ammah ta shiga last da abin ya faru da shi. Har rige-rige ake tsakanin Uncle Yousuf da Ahmad, sai dai kowanne ya samu nasarar kai hannunsa jikinsa. Ganin yanda aketa faman saka masa ruwa babu alamar zai farfaɗo Uncle Yousuf ya cema coach “Hameed muje asibiti kawai dan banga alamar zai farfaɗo ba a hakan nan”.
Cikin damuwa coach ya dubesa shima da bashi amsa da “Yousuf zuwa asibitin nan babu abinda zai canja. Dan mun gwada yin hakan a baya sai dai mu gama zaman banza dan su amsa ɗaya ma suke bamu zuciyarsa ta tsaya da aiki. Al'amarin nasa ne fa kamar abin sihiri gashi nan dai. Gida kawai ya kamata mu kaisa duk da gaskiya hakan na sakani fargaba dan tayarwa iyayensa hankali kawai zamuyi”.
“Gaskiya kar a kaishi can Brother” Ahmad ya faɗa cikin damuwa. Bai jira cewar kowa ba ya cigaba da faɗin, “Mizai hana muje wajen mutumin nan da ya taɓa bashi magani sanda abun ya takura masa”.
“Shawara mai ƙyau Ahmad, da ni duk nama rikice wlhy hakan bai zo min a rai ba. Kunga ku kamashi kusa a mota”.
A bayan motar Uncle Yousuf aka saka shi kamar yanda ya buƙata, shi da coach suka shiga gaba Ahmad a baya ya riƙe Smart. Kai tsaye ƙofar ruwa suka nufa, gudun da coach keyi ya sakasu isa cikin ƙanƙanin lokaci. Gidane irin na talaka mai ƙaramin ƙarfi, sai dai da ga waje shafe yake da siminti tsaf da shi da milk ɗin fenti. Da ga gaban gidan kaɗan islamiyya ce ta ƙanan yara da keta karatu kasancewar akwai ta safe zuwa ƙarfe ɗaya. Tsaiwar motar ta saka wani saurayi da ke tsaye da ga jikin barandar Islamiyyar matsowa garesu yana musu sannu. Basu wani tsaya jan maganar ba suka buƙaci ganin Malam. Kafin ya basu amsa sai ga malam ɗin ya fito da ga gida..........✍️
_Yau dai Smart ɗin ku ya ɗan bani tausayi🥲_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
[9/7, 1:56 PM] +234 813 110 8969: 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣8️⃣
_Ya rabbi ka gafartama *Sheikh Abubakar Giro Arugungun*. Ka yafe masa kurakuransa, alkairan da ya isar garemu na wa'azantarwa da koyarwa kasa ya amfanar da mu duniya da lahira. ALLAH ya albarkaci zuri'arsa. Suma iyayenmu ALLAH ka gafarta musu, damu baki ɗaya 😭✍️_.
........Wata nannauyar ajiyar zuciya Smart ya saki mai ƙarfin gaske lokacin da malam ya shafa masa ruwan addu'oi da yayi tofi a ciki, sautin karatun suratul Naazi'aat da ɗaliban malam ce ta fara shiga cikin kunnensa da wani irin ƙarfi tamkar a iya cikin kunnen nasa akeyi. Ya sake sakin ajiyar zuciya sai kuma ya kai hannunsa ya dafe goshinsa dan kansa wani irin ciwo yake kamar zai tarwatse. Uncle Yousuf ne ya fara ambatar sunansa, dan haka ya sake yunƙurin buɗe idonsa a karo na biyu sai dai ya kasa. A rikice duk suka dubi malam. Ya karkaɗa musu kansa da faɗin, “Kamar yanda na faɗa muku tun wancan karon ku sake jajircewa wajen addu'a da sadaka akansa, dan al'amarin nasa akwai ruɗani kamar na sihiri mai ƙarfi. Sai dai ban tabbatar ba dan UBANGIJI shine kawai masanin gaibu. Amma gaskiya al'amarin nasa yana nuna kamar bugewar junnu ne. Na fara baku ruwan addu'oi a wancan karon amma sai aka daina zuwa a karɓa kwata-kwata, dama ba komai bane face addu'oin karya sihiri wanda ya kamata ma ace duk musulmi kan dingayi a gidansa domin shi da iyalinsa koda lafiya lau ake dan rayuwa kake baka san mike biye da al'amarin ka ba. Koba sirihi akwai baki (kambun baka) da yafi sihiri kaifi a wasu lokutan. Koda ma bazaku juri zuwa nan ɗin a karɓa ba to ku dage da yi masa a gida dan ALLAH”.
A tare suka amsa da “In sha ALLAH malam” sai kuma suka ɗora da godiya. Ganin yanda Smart keta faman jujjuya kansa malam ya ƙara masa addu'a tare da basu umarnin kaisa asibiti mafi kusa. Godiya sukai masa dan a wancan karon ma haka yay musu. Suka ajiye masa sadaka shi kuma ya basu ganyen magarya da ayoyin da zasu karanta da ga cikin Alkur'ani mai girma. Kai tsaye asibitin suka nufa kuwa, inda aka bashi gado dan a kallo ɗaya idan kai masa dole ne ya baka tausayi, kai kace ba a yanzu kaɗai ya kasance a kwance ba yanda yay sharɓan. Sun bashi taimakon gaggawa har sai da ya samu barci suka ɗan samu nutsuwa. Sun yanke shawarar sanar da gidansu amma sai coach ya ce adai ɗan dakata idan basu sallamesa zuwa yamma bane sai a sanar musun. Hakan ya musu, dan haka sukai yunƙurin fitowa aka barsa da Ahmad ya zauna da shi kafin suje su dawo.....
★★★★★
Duk yanda taso cigaba da gudanar da al'amuran gabanta na wannan yinin hakan sai ya nema gagararta. Ba ƙaramin tsaya mata a rai abinda drivern nata yay mata yayi ba. Dole ta hakura da tattara bayanan case ɗin da zata fara tunkara a safiyar litinin kan dukiyar wasu marayu da wan mahaifiyarsu ke ƙoƙarin handamewa dan zuciyarta a cinkushe take matuƙa. Steering da take murzawa ta kaima duka a karo na babu adadi. Ta cije lips da masifar ƙarfi da faɗin, “Sai na koya maka hankali!”. Kalmace data ambatata yafi sau shurin masaƙi. Ga takaicin daren jiya da ma na cigaba da ci mata rai dan a duniya tai masifar tsanar wani namiji ya raɓeta da sunan taɓata ko soyayya. Shiyyasa shima Tajuddeen lissafinsa ya shiga cikin jerin lissafin abubuwa masu ƙuna da ajiyewa a kudin tarihinta na wannan yinin da take ganin yazo mata a birkice. Office ta koma, inda ta tarar da baƙi kashi-kashi na jiranta. Tabbas batajin magana, sai dai a ɓangaren aikinta ita ɗin jajirtacciya ce, dan ma ɗabi'arta ta shaye-shaye na matuƙar maidata baya a lokuta da dama, dan badan wata hikima ta UBANGIJI ba da Lulu ta jima da daina zuwa wajen aikin ma gaba ɗaya ne. Mummunar hallayya mafi muni tattare da Mawaddat shine sakaci da addini, sam babu abinda ta sani akan addininta sai abinda ba'a rasa ba sakamakon karatun ta na lawyer. Bata san a kira salla ta tashi tayita akan lokacinta ba, to idan ma tayin babu maganar yinta a yanda MANZON ALLAH ya koyar damu. (Kuyi haƙuri ba Lulu kaɗaice a wannan matsalar ba. Wlhy da yawan mutane sunayin salla ne ba'a yanda MANZON ALLAH ya koyar ba. Dan bawai fa muna nufin Lulu bata san salla ba, a'a itama ta tashi ne a yanayin yanda akeyi kawai nakeyi batare da samun ilimin yinta ba kamar yanda da yawa mutane suka kasance. Mafi yawanmu idan da zaman tsayawa akan ibadarmu ta salla za'ai tun daga tsaiwarta ma zamu fara samun gyara. Please Dan ALLAH a wannan gaɓar kowanmu ya nutsu ya kalla sallarsa da kuma bincike akan yaya ake salla kamar yanda MANZON ALLAH S.A.W ya koyar mu gani ko zamu ribantu da gyarawa). Sanda ta gadama take salla, tana kuma yin tane a yanda kawai taga anayi kasancewar karatun addinin ma gatan mahaifinta ya zame mata cutarwar da bata samesa ba. Masifarta kam wannan halitta ce, wani mai haƙuri wani saɓani haka. Sai ɗabi'ar shaye-shayen data jima tana binnewa wanda har yanzu bamu san tushen farawarta ba ko dalilinsa. Wulaƙanta mutane da takasu a duk yanda taso kuskuren mahaifinta ne da ya ɗorata a turbar komai take so zata samu. A duk sanda ka nunama yaro komai yake so zai samu tofa kansa zai ƙara girmane da tunanin yafi kowa daraja da power a rayuwa, sannan akan komai shine sama da kowa. (Iyaye sai mu kula hakan ba soyayya bace)....
Yanda ta zube wayoyinta da zama jagwab cikin lallausar kujerar office ɗin nata ya sake bayyanar da ɓacin ranta akan fuska. Hand bag dinta ta jawo tare da fiddo key ɗin drower ɗin jikin decks ɗinta da bata yarda kowa ya taɓa saboda abinda take ajiyewa a ciki ta lalubo. Tana ƙoƙarin buɗe drower ɗin sakatariyarta ya shigo office ɗin da sallama. Wani takaici ya sata ɗago idanunta da suka kaɗe da gajiya. Sai dai gaba ɗaya tama kasa mata masifar da ta saba yi mata a duk sanda tai mata kuskure. Da sauri sakatariyar ta ce, “Please am sorry maa. Wlhy abinda matar can tazo da shi ne yay matuƙar tayarmin da hankali. Jiya ma tazo nace mata ta dawo yau dan kina up 2days sai yau ne zakiyi res.....”
Hannu Lulu ta ɗaga mata alamar gajiya da saurarenta. Murya a shaƙe ta ce, “Zainab ba wanda zan iya saurare a yau koma minene akazo da shi. Ki sake bama duk wanda ya dace sabon appointment banda yau da gobe. Duk case ɗin da kuma kika sani bani da buƙatarsa a teburina karma mai shi ya shigomin office ok”.
Zainab da damuwa ta bayyana ma a fuska ƙarara ta gyaɗa kanta da ke ƙasa. Sai kuma cikin rawar murya dan har ta fara hawaye ta furta, “Aunty matar can fa mijinta ne yayma yarinyarta da taje agolanci da ita gidansa fyaɗe. Kuma yarinyar shekararta tara kwata-kwata. Sunje asibiti da yarinyar amma anƙi karɓarsu tun jiyan wai sai da ƴan sanda. Taje police station ɗin kuma ƴan sandan nata mata yawo da hankali. Wlhy bakiga a yanda sukazo da yarinyar ba a jiya da yamma abin babu ƙyan gani....”
Wani irin matse idanu da damƙe kujera Lulu da jikinta ya fara tsumar mazari tayi. (Mawaddat calm down. Mawaddat calm down. Mawaddat calm down). Wani sashe na zuciyarta ke