Showing 153001 words to 156000 words out of 181007 words

Chapter 52 - kanwar maza 3 COMPLETE

12 Jul 2024

39260

hancinta.

Ta ɗaga kai ta kalli matar, matar fara sol kamar ka taɓa jini ya fito, wata ƴat gayu, ta sha baƙin glass, da English wears.

Ta nemi wuri ta zauna, ta kalli rumaisa ta ce "Hey, ina mutanen gidan?"

Rumaisa ta kalleta, tare da jinjina rainin wayo irin na matar,  ta ce "Mutan gida kamar wa kenan?".

Matar ta ce "Matar gidan, da kuma takawa"

Cikin rainin hankali ruma ta ce "Matar gida ni ce, takawa kuma is not available"


Ayshercool.
08081012143
[12/12, 7:33 PM] rahama Jos: Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please 🙏
Rumaisa na nan tsaye tana kuka, tawagar ta tashi, suka yi gaba.

Ammi sai rarrashin rumaisa take yi, laila ta ce "Wai ke ba kya jin kunya ne, wa ki ka fi iya soyayya, soyayyar da ko iya ta baki yi ba, ko Kunyar ammi ba kya ji".

Ammi ta ce "Babu ruwanki, mu ba ma wata kunyar sirikai".

Su Jamil suka ƙaraso, suka gaida Ammi, sai dai ammi ba ta san, meke faruwa ta takawa da su Jamil ba, dan haka normally ta amsa musu, kamar yadda suka saba.

Jabir ya dubi iman ya ce "Iman ko zaki zo in mayar da ke a mota ta?"

Ammi ta ce "Kar ka damu, kwa haɗu a gida, laila mu shiga ciki mu gaisa da mutanen gidan, tun da matafiya sun tafi"

Suka shiga wurin mama, sai wani cika take tana batsewa, sai dai duk da haka, ta shiga taitayinta ganin ammi tare da laila, dan kar ta san kar.

Ta dubi laila ta ce "Ashe kin zo garin?"

Cikin taƙama laila ta ce "Yeah, almost 2days"

"Yayi sannu da zuwa, wannan kamar matar takawa ko? Meya sameta take kuka?".

Laila ta ce "Abun mata da miji sai Allah, ga yarinta a kan ta, dole tayi kuka".

Mama ta ce "Mhmmm Allah sarki Aisha, har ta kai adam ya manta da ita, ya cigaba da rayuwarsa?"

Laila sarai ta gane magana matar turaki take nema, dan haka ta ce "Aka rasa iyaye ma a dangana, a cigaba da rayuwa ayi musu addu'a, rasuwar fulani ai mu aka yi wa, kuma babu yadda za ayi mu manta da ita, kuma takawa yana nan yana aiki tuƙuru a kan neman hakkinta. Kuma dan ya rasata baya nufin ba zai sake farinciki a rayuwarsa, da ya rasa soyayyar mahaifi ma bai mutu ba, dan haka dan Allah a daina kawo wannan maganar"

Laila ta miƙe ta ce "Ammi mu tafi"

Babu wanda ya kuma magana har suka fice.

Zee da tana falon aka yi komai a gabanta, shiru ta yi, dan kaɗan da aikin laila ka yi mata rashin kunya, ta kwaɗeka, saboda masifarta.

Takawa suna airport, ya kira iman, ya ce ta haɗa shi da rumaisa, ta miƙawa ruma wayar, sai dai ta yi shiru.

"Hello, mimi"

"Na'am"

"Ki yi mini Addu'a, nan da mintuna talatin jirginmu zai tashi"

"To Allah ya kai ku lafiya"

"Amma dai kin daina kukan ko?"

Murya can ƙasa ta ce "Na daina"

"Yauwwa buruwar mijinta, da kun koma gida, ki samu ki ɗan yi bacci, jiya bamu samu isasshen bacci ba. Sannan a gida akwai key ɗin wardrobe ɗina, na bar miki kuɗi a ciki, sannan zan din ga turawa laila kuɗi ko zaki buƙaci wani abun".

Ruma ta ce "To" daga haka ta bawa iman wayarta.

Su Fauziyya kuwa bayan sun gama kai wa samha rahoto, silalewa suka yi, suka bar gidan, suka bar ta da tension.

Zee ta tarar da Samha a zaune, abun duniya ya isheta, tamkar ta ɗora hannu a ka, ta fasa ihu saboda baƙin ciki, dan me Mummy za ta ce kar baba uwani ta din ga gaya mata abubuwa da suke faruwa a gidan Adam, sai wanda ta bayar da umarni?.

"Samha!" Zainab ta kira sunanta a karo na uku.

Samha ta ɗaga kai ta kalleta, "Sai magana nake kin yi shiru".

Ɗan guntun tsaki ta ja ta ce "Menene?"

"Labari ne mara daɗi bayan wanda su Fauziyya suka gaya miki. Laila ta dawo, sannan alamu sun nuna cewa yarinyar nan zaman lafiya suke yi da mijinta, kin ga zancen su Fauziyya ya tabatta".

Samha ta ce "Babar su Fauziyya ce banbar munafuka, wato hajiya jamila"

Cikin mamaki ta ce "Uwar ɗakin naki?"

"Zainab saboda tsabar matar nan ta mayar da ni ƴar iska, mun bawa wannan uwanin aikin, kawo rahoto a kan abubuwan da suke faruwa a gidan adam, ni burina auren adam, ita kuma hana shi sarauta. Ni yayi sarauta ko kar ya yi bai dameni ba, ni shi nake so. Meye haɗin aikinta da nawa, da za ta ce wa baba uwan wai kar ta din ga kawo mini bayanin abin da yake faruwa sai wanda ta yi mata umarni, ni zata mayar shashasha, na shanya baki na san na yi aiki tuƙuru a kansu, amma na yi sakacin da har shaƙuwa ta shiga tsakaninsu. To bari a gama watsewa, na je har gida na sameta".

"Ki sameta ki yi mata me ne? Ke kin san idan ki ka ce zaki yi fito na fito da ita, tafi ƙarfinki. Babarki ce a hatsabibanci, ki cigaba da abubuwan ki ba tare da ta sani ba, ki bita a haka, kar kuma sauya mata fuska".

"Ba zan iya jurewa bane zee, kawai ji nake idan ban zageta ba zan huce ba".

"Aikuwa ya zama dole ki danne, ko ta yi miki wani mummunan sharrin".

Samha ta yi ajiyar zuciya ta ce "Zainab na wuce yadda ki ke tunani, tun da ta ɓata nawa aikin, sai dai mu yi biyu babu, kuma son Adam yanzu na fara, sai na ga ƙwal uwar daka".

Rumaisa kuwa wuni tayi baccin dole, saboda koke-koken da tayi, kanta ya fara ciwo, dan haka tayi ta kwanciya tana bacci, surutun ma ya gagareta, ba ta taɓa zaton akwai wani abu da zai tsaya mata ya hanata walwala ba.

***

Mummy kuwa ta titsiye Mahmud a ɗaki, ta na tayi masa bala'i a ka, kamar ta ari baki, saboda tsan-tsar ɓacin rai da damuwa.

"Kai yanzu Mahmud dan Allah ba ka ji kunyar abun da ka aikata ba, matar da ba ƙaunarka take yi ba, ta fifita ƴaƴanta a kan ka, kai ka san ba ƙaunarmu suke yi ba, daga ita har ɗanta, amma dan abun kunya, kana jiran sarauta yana jira, dan me zaka tuƙa shi a mota, direbansa ne kai, ko saboda rashin sanin ciwon kan ka ne? Ko kuma dan ka nuna mini iyakata, ka nuna mini bani na haifeka ba?"

Yayi mata shiru yaƙi magana, hakan ya ƙara tunzurata, ta dungure masa kai da ƙarfi, amma cikin baƙin taurin kai, ko gezau bai yi ba.

Sai da ta zuciya ta yi hanyar fita, sannan ta tsinkayo muryarsa ya ce "Tambayar da rumaisa ta yi mini, ta jefa ni cikin damuwa, da taradaddin neman amsar, sai dai ban sani ba ko zaki tayani samo amsar?" Cak ta tsaya, ta waiwayo tana kallonsa.

Bai ɗago ba ya cigaba da cewa, bayan buɗar idona a hannunki, kin ginani a kan cewa, a duniya bani da babban maƙiyin da ya wuce giwa da kuma ɗan uwana Adam.

Na ginu a kan haka, a lokacin da na san gaskiyar wacece mahaifiyata kuma, sai ki ka nuna mini bata sona ne, ta zaɓi waɗancan ƴaƴan nata a kaina, shiyasa ke ki ka karɓeni ki ka riƙeni, kuma kin ce baki da wani buri da ya wuce na gaji kujerar babanmu, marigayi galadima. Na hau kan tarbiyarki da hanyar da ki ka ɗorani a kai, na sawa zuciyata tabbas mahaifiyata ba ta ƙaunata. Sai dai ko da rumaisa ta tambaye ni sau ɗaya me giwa ta taɓa yi mini, a zahiri da ya nuna bata ƙaunata? Sai kunya ta rufeni, a lokacin da na tuna kin yi mini shamaki da zuwa in da take, kuma kin koyar da ni ƙiyayyar ɗan uwana, ƙiyayyar da ta yi tasiri a tsakanin mu. A lokacin da rumaisa ta tunatar da ni, na sanya mahaifiyata kuka a lokacin da ta nemi alfarmata, ƙarƙashin umarninki, na ƙi yi mata, sai na ji a duniya bani da wani amfani.

Mummy ba ina nufin juya miki baya ba, bani da wata a duniya bayan ke, amma giwa na da hakkin haihuwata da ta yi, ba zan taɓa bari ki muzanta ba, sai dai ina fatan ganin tabattacen haɗin kai a cikin gidanmu, auro rumaisa cikin iyalinmu alkhairi ne mummy. Ban aikata hakan dan muzanta miki ba". Ya ƙarasa maganar cikin rauni.

Kuka Mummy take tamkar ta aminta da abun da ya faɗa, sa dai ƙasan zuciyarta cike yake da baƙin ciki da takaici, tare da aniyar sake ɗaura ɗambar, kawo ƙarshen giwa, da adam har da wannan annamimiyar ƴar tayin da ke barazana ga harƙalarta.

***

Wajen ƙarfe biyar na yamma, rumaisa na zaune zuruuu kamar mara lafiya, shi kansa sabir ba shi da karsashi, ya zo Jikinta ya kwanta, yayi shiru shi ma ko wasa baya yi.

Iman ta ce "Haba Anty rumaisa, takawa zai dawo, tafiya ba mutuwa ba ce, wannan damuwar ta yi yawa ai"

Iman ta ce "Hmm ba zaki gane ba, ni fa ban taɓa zaton zan damu ba, nayi-nayi kar ka damu na manta, amma na kasa".

"To ba ga waya ba, idan ya kira sai ku din ga video call".

Rumaisa ta ce "Ni duk ba wannan ne ya dameni ba" Iman za ta sake magana, Nusaiba ta yi sallama.

Suka amsa mata, ta dubi iman ta ce "Amaryar uncle, his royal highness jabir, is waiting for you".

Iman kamar ta saka kuka ta ce "In yi masa me?"

"Iman me yake damunki ne? Ban gane ki yi masa me ba? Ki je ki ji mana"

A daƙile ta ce "To, zan je" Nusaiba ta juya ta fita.

Rumaisa ta ce "Kar ki damu, in sha Allah babu abun da zai faru sai ikon Allah, wannan masifaffiyar babar ta sa ma, na san ba zata bari ba".

Rumaisa na cikin maganar, laila ta shigo, ta kalli iman ta ce "Iman, jabir fa yana jira" ta ƙarasa maganar tare da zama a kusa da rumaisa, ruma tana satar kallon fatar laila, kamar jikin tarwaɗa, gashi ko kunya ba ta ji, take tsukewa a cikin ƙananan kaya.

Iman kamar ta zubar da hawaye, haka ta tashi ta bar ɗakin.

Laila ta kalli ruma ta ce "Kina ji na ko?" Rumaisa ta ji kamar ta ce mata 'Da ni kurma ce?"

Amma a zahiri ta ce "Eh"

"Tun da yau mijinki ya tafi, dama ya bar sallahun kai ki makarantar matan aure, gobe in Allah ya kaimu za a fara kai ki, daga nan zaki kwaso kayanki na gidanki ki dawo nan. Ni na karɓi ragamar kula masa da ke kafin ya dawo, dan haka dole zaki din ga bin duk abun da na saka ki, bana son gardama ko rashin kunya, dan idan rashin kunya ce, sai dai ki koya a wurina. Idan kin dawo daga makaranta, zan din ga yi lesson da kaina, da kuma dabarun zaman aure.

Abu na gaba, zamu din ga gyaran jiki, naga kina da tsabta, kuma kin iya girki ma, amma dole zamu din ga shiga kitchen tare ki koyi wasu abubuwan.

Wannan fatar taki, so nake ta murje ta fi haka haske da kyau".

"Taɓ wallahi ba zan bleaching ba".

"Ni ma ba bleaching na ce ki yi ba, gyara za ayi, wannan gashin ma, ya ce ba kya son kitso, dole ya din ga shan gyara, ga iman nan, ita zata ja ragamar koya miki makeup"

"Ni gaskiya idan na yi wannan damɓare-damɓaren, fuskata ƙaiƙayi take yi, duk in ji ta ɗaure kamar ta tsohuwa".

Laila ta ce "To kar ki yi mana, kanki zaki yi wa, iyaka ya kawo wata matar mu shige masa gaba yayi wani auren, kuma dole ki koyi magana, ki daina yaɓawa mutane magana son ranki"

"Na iya magana, kawai sai an yi mini ba dai-dai ba, nake yaɓa maganar".

"Ke! Baki san komai ba game da rayuwa, shi kansa mijin naki, yadda ki ke yi masa magana, tun da ba sa'anki ba ne, ba haka ya dace ki din ga magana da shi ba, idan kin shirya zaman auren, sai ki bi instructions ɗin da zan din ga baki.

Abu na gaba dole ki ga maman Khadija".

Ruma ta yi ƙuri da ido tana kallon laila, wacecec kuma maman Khadija.

Kamar laila ta shiga ran rumaisa ta ce "Na san baki santa ba, amma zaki santa yanzu. Wannan ƙwailar da yake ce miki, a kankaro ki, kema ki shiga cikin sahun manyan mata".

Cikin zaƙuwa ruma ta ce "To ita maman khadijan me zata yi mini?" Dan a yanzu tana fatan su fito, a baya ne take zaton nono bashi da wani amfani a gareta, sai idan ta haihu za ta shayar, amma yadda ake gaya mata kalmar ƙwaila, yana ƙona mata rai.

Laila ta ɗora da cewa "Garin kunun sabayarta zan yi miki order, ki din ga amfani da shi kafin ya dawo, dan ni idan na saya, Canada ake tura mini shi, yana da daɗi, zai gyara miki fata da jikinki baki ɗaya, kuma ki ciko ki murmure sosai, idan kuma kin shirya cigaba da zama ana yi miki gori shikenan".

Ruma ta tuna iskancin da su Fauziyya suka din ga yi mata, wai a kalli ƙirjinta kamar plate, ga samha cikakkiyar mace, amma takawa ya aureta, ta gyara zama ta ce "To ita maman khadijan a ina take? Kuma yaushe zaki sai mini kokon nata".

Laila ta ce "Ni ban ce miki koko take sayarwa ba, garin kunun sabaya take sayarwa, amma ba a kano take ba, a zariya take, bayan federal palladan. Na daɗe ina harka da ita, kuma na haɗa mutane da ita sosai, na san ingancin kayanta. Zan yi waya da ita, a sayo, tunda tana tura kayanta ko ina, amma ba zan baki ba, sai na ga gwargwadon biyayyarki"

Rumaisa ta yi shiru tana kallonta, laila ta gama bayananta, rumaisa ba wani fahimta tayi ba, ita dai babban fatanta, a samo abun da laila ta faɗa na yin kunu, saboda ta sha ko ya fito ta huta gori.

(*INA UWAR GIDA DA AMARE, INA WANDA SUKA HAIHU, KO SUKA YI YAYE, INA MASU RAMA DA SU KE SON JIKINSU YA MURMURE SU YI ƘIBA, INA MASU YARA WANDA SUKE FAMA DA MATSALAR RASHIN GIRMA? SHIN KEMA MIJI NA YI MIKI GORI, KAMAR YADDA TAKAWA YAKE YI WA RUMAISA? SHIN KINA KUNYAR SHIGA CIKIN ƳAN UWANKI MATA, SABODA RASHIN NONO, KO KUWA ƊINKI NE BA YA ZANA A JIKINKI, SAI KIN HAƊA DA CIKO? RAMA CE TAYI MIKI YAWA, KO KUWA YAYE YA SANYA NONONKI YA ZUBE KAMAR BANA MACE BA. TO ALBISHIRINKU! KUKANKU YA ƘARE, HAKA ZALIKA KAKARKU TA YANKE SAƘA. MAMAN KHADIJAH TA SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYE, DA INGANTACCEN GARIN KUNUN SABAYARTA. BAYA CUTAR DA LAFIYA KO KAƊAN, ZAI GYARA MUKU JIKI, YA CIKO DA NONO, INA WANDA SUKA YI YAYE, KO SUKE SHIRIN YI, KU JARRABA WANNAN GARIN KUNU, ZAKU BAYAR DA LABARI, MAMAN KHADIJAH NA NAN A GARIN ZARIYA, BAYAN FEDERAL PALLADAN, KO KU TUNTUƁETA KAI TSAYE TA LAMBAR WAYARTA 08033411249*

Iman kuwa a sitting room ta iske jabir, ya wani hakimce yana danna wayarsa, tun da ta shigo ya kafeta da ido, kamar yadda ya saba. Ta nemi wuri ta zauna, tayi masa sbiru.

"Wai dan Allah iman me na yi miki ne? Meyasa ki ka tsane ni haka?"

Cikin mamaki ta ɗaga kai tana kallonsa, ganin yadda yake neman ya raina mata wayo, ya fi kowa sanin abun da ya sanya, ba ta yin sa, amma yake ta wani basarwa.

"Ke shikenan abu ba ya wucewa a wurinki ne?. Son ki nake yi da gaske, aurenki zan yi, magana ta riga ta yi nisa, na samu amincewar ammi, takawa kuma kan ya dawo ma wataƙila an riga an yi".

"Amincewata da ta mahaifiyarka ba ta da muhimmanci kenan?".

Yayi murmushi ya ce "Amincewar hajiya wani abu ne daban, ke kuma a kowane lokaci idan mun yi aure komai zai wuce, dan Allah ki daina taurin kai, ke kanki kin san ba ki da wani rufin asiri, da ya wuce amincewa aurena, idan ba haka ba, duk wanda suka zo a baya sun tafi, sun kasa ɗaukar kasada. Ni a nawa ganin zaɓe-zaɓe ba naki bane ba iman, kamata yayi ki gode mini, da na ce ni na ji na gani"

"Ko ba ka yi ɓoye-ɓoye ba, na san ni ba kowa bace ba, abun da ka ke son gaya mini kenan, amma kasancewata ba kowa ba, ba shi yake nufin zuciyata ba ta da ƴancin ta so ko ta ƙi wani abun ba, ina girmamaka a matsayin yayana, idan farincikin ammi in aureka shikenan, amma ni babu soyayya a raina".

Jabir ya ce "Haka ne, ammi ta yi iya ƙoƙarin ta a kanki, har keta billenta ta yi, ta nemi alfarmar ɗan ta ya aureki, amma ya ƙi hakan, dan yana ƙyamarki, na cancanci ki gode mini ne iman, ba ki ƙi ni ba a halin yanzu ba ki da zaɓi, aure shi ne mafitarki, idan ba haka ba kuwa wannan kyawun barazana ne a gareki"

Sannu a hankali jabir yake gasa mata munanan maganganu, amma ta yi iya ƙoƙarin ta, ta din ga haɗiyarsu, duk da yadda take ji, suna barazana ga zuciyarta.

Jin bugun zuciyarta ya fara ƙaruwa, kuma numfashinta ya fara sama-sama, ya sanya ta tashi ta koma ɗakinta.

Rumaisa na ta jin daɗi, tare da fatan, Allah ya sa laila da gaske take, za ta sai mata abun nan, Iman ta shigo, sai dai ba sai an gaya mata ba, ta san iman ɗin a cikin damuwa take.

Rumaisa ta yi shiru ba ta ce mata komai ba, ita ma ba ta ce mata ba, ta je kawai ta kwanta a kan gadonta.

Mintuna talatin ammi ta shigo, tana faɗin "Iman, ya ku ka yi da jabir ne, ba kya bani update?" Ta tarar da iman a kwance, kamar mai bacci.

Ammi ta ce "Iman ƴan kwanankin nan baccin nan ya fara yawa, duk in da ki ka samu sai bacci? Rumaisa ko ta gaya miki wani abu ne?".

Ruma ta ce "A'a ba ta ce mini komai ba".

Ammi ta ce "To shikenan"

Da daddare rumaisa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login