Showing 51001 words to 54000 words out of 181007 words
"A'a babu ruwana, kai maimakon ka saita yarinyar nan, ku bi komai a sannu amma kana yi mata huɗubar tsiya, Nuraini har da kai fa kake zigata take rashin ji, babu ruwanka da mutumin nan ku fita sabgarsu, ni ba zan iya tashin hankali da mutane ba".
Usman ya miƙe ya ce "Mama irin masu haƙurinki ake cuta, komai ki ce ayi haƙuri a barwa Allah, da haƙurinki muka ɗauko, muna zaune za a fille mana wuya ki ce mu yi haƙuri"
Dariya rumaisa ta yi, mama kuwa ta rarumi takalmi, ta jefawa usman, ya goce tare da shigewa ɗakinsu.
Ruma ta ce "Allah ya biya yaya usy nawa, Allah ya bar mini kai".
"Ki cigaba rumaisa, yayi ta ɗoraki a keken ɓera ya kai ki ya baro, tun da ke dai ba namiji bace ba".
***
Ko da ammi ta koma gida, Nusaiba da Iman suka tareta suna tambayarta yaya suka yi da turaki?
Nan ta kwashe komai ta gaya musu, iman ta ce "Allah ya tabattar da alkhairi, ya sanya mai girma turaki ya shawo kansu komai ya tafi cikin sauƙi, ni dai ina sonta wallahi"
Nusaiba ta ce "Mhmm, ni kam kawai yadda za ayi zaman nan nake hangowa, ba fa sa shiri ammi, kin ga ita tana da tsiwa, shi kuma akwai faɗa"
Ammi ta ce "Ke rabu da shi, rayuwar aure ta fi ƙarfin wasa, idan suka zauna za su nutsu, sannan a rayuwarsa da ita akwai wani darasi da nake fatan ya koya, kuma kan ayi auren ai dolensa ya dinga zuwa wurinta su saba"
Iman ta yi murmushi ta ce "Akwai rikici kenan?"
Ammi ta ce "Ta bani tausayi ɗazu da muka yi waya, wai an ce ta yi cikin shege, ana yi mata kallon ƴar iska, saboda ta zo da sabir, idan ban saka takawa ya aureta ba, shikenan an yi mata mummunan tambari, mutane ɗa idan ba na su bane ba, sun din ga janyo masa jafa'i kenan"
Nusaiba ta ce "Haka ne, Allah ya shirya, ya tabbatar da alkhairi" suka amsa da amin.
Baba uwani da take laɓe ta ji hirar ta su sama-sama, sannan bakomai ta ji ba, amma a abun da ta jin, ta ƙudurce za ta je ta sanar da Mummy.
Rumaisa mita a cikinta, kamar an yi mata gori, yau wuni ta yi tana cigaba da mitar abubuwan da ake yi mata a unguwar nan, mama tun tana yi mata nasiha tana cewa ta bar wa Allah, har ta yi mata banza ta ƙyaleta, Abdallah ya sakata a gaba yana cigaba da kunnata, tana mita. Bayan fitar Abdallah rumaisa ta shiga ɗakinsu, ta duba wurin da yake ajiye fensiransa na zane kasancewar sa architect.
Ta zauna ta nutsu sosai, ta hau zane-zane.
Mama ta ce "Uban me ki ke yi musu a ɗaki, ki ka shiga ki ka yi shiru?"
Rumaisa ta ce "Bakomai"
"To fito musu daga ɗaki, tun basu dawo sun tarar da ke ba"
"Mama zan fito ina zuwa"
Sai da ta gama abun da Allah ya nufeta da yi, sannan ta fito ta fice ba tare da sanin mama ba.
Maƙwabciyarsu ta zana, kuma zanen ya fita sosai, ta yi headline da munafukar unguwa, a ƙasa ta rubuta by Rumaisa Mahmud ƙanwar maza. Ta je ta liƙe a ƙofar gidan matar, ta nausa ta tafi gidansu Habiba, ba tare da mama ta san ta fita ba ma.
Ayshercool.
paid book ne, ₦500 via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143[12/12, 7:33 PM] rahama Jos: *PAID BOOK NE, ₦500 NE VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA, 08081012143*
Gaba ɗaya ji yake duk wani girma da mutuncinsa sun zube, kamar shi ace wai zai je wurin wata ƴar yayyiyar yarinya yayi zance da ita, wai zai aureta, ko aurensa na fari aisha ta kammala deegree ya aureta, wannan shi ba ya tunanin ko primary ma ta gama.
Mama kuwa kwana ta yi ba barci, sai addu'a kawai da take yi, ji take tamkar ta rufe rumaisan da duka, dan bayan gama ƴan koke-kokenta tuntsirewa ta yi ta hau bacci.
Mama ta kalleta ta girgiza kai ta ce "Allah ya shiryeki, ya ganar da ke"
Da asubar fari, bayan rumaisa ta idar salla, ta tafi ɗakin su mai sunan baba ta yi sallama, suka amsa mata.
Ta leƙa ta ce "Yaya usy jiya kun dawo da yaya aliyun?"
Abdallah ya ce "Wuce ki bawa mutane wuri, duk ba ke ki ka janyo ba, karfa kawai"
Mai sunan baba ya kalli Abdallah ya ce "Kar ka kuma gaya mata haka, bai dawo ba a can ya kwana, duk saboda ke, gaba idan ki ka sake, ke zan kai musu in karɓo shi, dan mun fi son sa a kan ki, mara kai kawai"
Sumi-sumi ta juyo za ta fito, ta fuskanci kowa haushinta yake ji yau.
Usman ya ce "Wallahi yau da na ga malam shamsun nan a masallacin asuba, ji na yi kamar na ɗaga shi na wurga shi cikin kwalbati, shi ne babban munafukin da ya je ya kai wa ƴan sanda"
Mai sunan baba ya ce "Ba ruwanka da shi, ku bari mu kashe wannan case ɗin tukuna".
Abdallah ya ce "Ni malam lawan mai shago na kusa kifawa mari, ya biyo ni wai rumaisa ta yi masa asarar ƙwai cret huɗu, wai in zo in biya, na ce masa sai dai mu yi kokowa ya ɗiba, gaba ɗaya mutane fuska biyu ce da su".
Rumaisa da take tsaye tana jin su da sauri ta ce "Wallahi ko kret ɗaya bai yi ba, bai fi guda shida ba fa"
"Au laɓe ki ke yi mana ko?" Abdallah ya faɗa yana nemo abun duka.
Da gudu ta shige ɗakin mama, sai dai irin kallon da maman ta yi mata, ya sanya ta rasa in da zata saka ranta.
Haka ta tsuguna ta takure, da duku-dukun mama ta shiga kitchen, ta girka abinci, gari na yin haske, ta ce lallai mai sunan baba ya taso su tafi station ɗin.
Mai sunan baba ya ce "Mama, idan kin je wurin nan babu abun da zaki iya a kai, ki bari zan je ni da Usman"
Mama ta ce "Ni dai ka ƙyaleni na je na ga a yaya ya kwana?"
"Lafiya ƙalau ya kwana, kuma in sha Allah zamu dawo miki da shi, ki yi haƙuri" da ƙyar mama ta yadda, ta basu abincin suka tafi.
Rumaisa ta ce ita ba zata tafi makaranta ba, sai yaya Aliyu ya dawo.
Mama ta ce "Aikuwa ba ki isa ba, sai kin shirya kin tafi, wataƙila kan ki dawo na huce, dan da na kalleki haushi nake ji, haka kurum saboda ke kin saka an kulle mini ɗa, mara jin magana" shiru rumaisa ta yi tana kallon mama, kenan yanzu mama ta daina son ta?.
Jiki a sanyaye ta shirya, mama ta hanata kuɗin makaranta, ba babban abun da ya sake ƙular da mama, irin yadda rumaisan ta zauna ta naɗi abincinta, kamar abun bai dameta ba sosai.
Haka ta tafi makaranta, tana tunani kala-kala, amma har ga Allah abun ya dameta.
Kamar yadda ammi ta buƙata, da safe Adam ya je gidan, a lokacin su iman duk sun tafi makaranta.
Ya ɗau sabir yana yi masa wasa, sai dai ƙememe yaron nan yaƙi dariya, sai bin sa da yake da kallo.
Ammi ta fito suka gaisa, ta ce "Yanzu wurin aikin zaka tafi?"
"Eh, na biyo na karɓi saƙon ne".
Ammi ta ce "To, tun da baka tambayeni ba, ni bari na gaya maka yadda muka yi da turaki".
Ya sunkuyar da kai yana wasa da hannun sabir.
"Mun tattauna da shi, ya ce mini in bari ya dawo daga umara, zai yi magana da su wambai, dan na san akwai ƙalubale, tun da rumaisa ba jinin sarauta ba ce, ko ƴar wani sananne ba, dan haka zai yi muku Addu'a a can, da ya dawo aka daidaita kuɗin aure za'a kai, bayan salla idan Allah ya kaimu za ayi"
"To, Allah ya wuce mana gaba".
"Amin, wai da ce mini yayi, Jamil ya ce ko za'a maye gurbin Fulani da samha, ni dai ban ce komai ba na shigar da maganar rumaisa, dan ita ta fi kwanta mini"
Adam har mamakin ƙaunar da Ammi take yi wa rumaisa yake yi, tabbas da so samu ne, Samha ta maye gurbin aisha, dan ita ta isa mace da hankalinta da iliminta, kuma Samha ta daɗe tana son shi, ya san hakan, amma ammi ta dage a kan wannan ƴar yayyiyar Yarinyar.
Ya numfasa ya ce "Allah ya kyauta"
Ammi ta miƙa masa leda ta ce "Gashi nan, sabuwar jakar makaranta ce, da litattafai da turare, ka kai mata ka ce ina gaisheta"
Adam ba yadda ya iya, ya karɓa ya amsa da to.
Ya fita riƙe da ledar kayan a hannunsa, ya san zuwansa wurin Yarinyar nan, ba abun da zai ƙara masa sai raini.
A harabar gidan ya tarar da Mahmud, tun da ya dawo yana ganin shige da ficen motocinsa, amma basu ta ɓa haɗuwa ba sai yau, yana tsaye a wurin parking space ɗin Adam, kusa da in da zai ɗau motarsa.
Adam bai kula shi ba, shi ma bai kula shi ba, ya je ya buɗe motarsa ya kunna, ya ɗan jima a ciki, amma ya ga Mahmud ba shi da niyyar matsawa, ya din ga danna horn, amma Mahmud ya yi burus, ba tare da wani ɓata lokaci ba Adam ya bawa motar wuta, yayi reverse, ai kuwa ya buge Mahmud, ko kaɗan Mahmud bai kawo Adam zai yi masa haka ba, kan ya ankara ya ga Adam yana ƙoƙarin bi ta kansa, ba shiri ya mirgina, Adam ya ja motar da gudu ya bar gidan.
Ma'aikatan gidan suka yo kan Mahmud suna yi masa sannu, suna ƙoƙarin ɗaga shi, sai dai ciki gwasalewa ya nuna musu shi zai iya tashi, sai dai abu kamar wasa, da ya miƙe ɗin ƙafa taƙi takuwa.
***
Rumaisa tana hanya tana addu'a, Allah ya sanya yaya Aliyu ya dawo, Allah ya sa komai ya wuce, sai dai ko da ta iso gida, ta tarar da Usman da mai sunan baba amma babu Aliyu. Cikin damuwa ta ce "Yaya usy ina yaya Aliyun yake?"
"Ke, case ɗin nan fa maƙabcinmu malam shamsu, ya yi uwa yayi makarɓiya yana ta kambama abun, gaba ɗaya ma sun ƙi saurarmu a station ɗin, wai sai DPO ya zo, DPO na zaci wanda ku ka yi case ɗin nan ne kwanaki, ashe an canza wani, sun kafi wai sai an je state cid tun da aka yi iƙrarin kisan kai".
Rumaisa ta ce "Na shiga uku, ba fa yaya Aliyu ne ya ce zai kashe shi ba, shi ne ya ce zai kashe shi".
"Koma menene ba ke ki ka janyo ba rumaisa, duk abun da mutum zai gaya miki sai dai ya shiga ta kunnen dama ya fita ta hagu, saboda wautarki kin jefa ɗan uwanki a wahala"
Usman ya ce "Dan Allah mama ki daina faɗar haka, ƙaddara ce"
A fisace mama ta ce "Rufe mini baki, ko na make ka, ai duk gidan nan babu mai koya mata rashin ji irin ka"
"Allah ya baki haƙuri, ba ri mu yi salla mu koma".
Adam kuwa ko kaɗan bai ji babu daɗi ba abun da ya yi wa Mahmud, dan a lokacin nan yadda ya hasala, da ya samu dama sai ya taka shi da mota uban kowa ya huta, ya sauke masa wannan girman kan da rashin mutuncin da yake ji da shi.
A haka yake wurin aiki, ya gama abun da yake yi ya fito, yana da niyyar zuwa gidan gona, sai dai dole ya je ya kai wannan saƙon kan mama ta ɓata ranta.
Mahmud kuwa ƙarshe, sai ka shi sashin Mummy aka yi, a rikice take tambayarsu maiya same shi, suka gaya mata Adam ne ya buge shi da mota.
Nan da nan ta hau ta fara bala'i "Wannan wane irin wulaƙanci ne, anya Adam bai fara shaye-shaye ba? Ko dai haryanzu haukar ce a kansa, tayaya zai taka ka da mota? Wallahi ba zan lamunta ba sai na ɗau mataki"
Mahmud ya ɗan cije lips ɗin sa ya ce "Ki rabu da shi zan rama ne, yanzu ni dai ƙafata zafi take yi ki yi wani abu a kai"
"Wallahi ba zan ƙyale ba, Fauziyya ɗauko key mu tafi asibiti kawai, Allah ya sa ba wani abun ne ya samu ƙafar ba"
"Mummy, dan Allah ki rabu da shi, am just testing his anger, ashe yana nan a yadda yake bai canza ba" yayi maganar cikin zolayar Mummy.
Cikin fushi ta ce "Ka rufe mini baki, this is an serious issue, ba zan bari ba" ganin yadda ta ɗau zafi ya sanya shi yin shiru yana kallon ƙafarsa.
A ƙofar gidan su rumaisa, Adam ne a tsaye, yake kiran wayar Aliyu, amma shiru bai ɗauka ba, wayarma a rufe take, ya kira har ya gaji, ya aika yaro ya ce ace ana sallama.
Usman ne ya fito, domin duba waye, ya tarar da Adam a tsaye, ya ƙarasa yana wani basarwa, suka gaisa sama-sama.
Adam ya ce "Aliyu nake nema, na kira wayarsa ba ta shiga"
Usman ya kalleshi, ya lura ta su ta zo ɗaya da Aliyu sosai.
Ya ce "Ya ɗan haɗu da tsautsayi ne" ya bashi amsa a taƙaice.
"Wane irin tsautsayi kuma?"
"Eh waccan yarinyar ce ta tsokano ɗan daba, ya je tare mata, kuma dama ta yi rigima da maƙwabta, shi ne mai gidan ya saka aka kama su, tun jiya muke zuwa police station, an ƙi sakinsa, yanzu ma komawa zamu yi"
Mamaki ne ya sha kan Adam, duk rumaisan ita kaɗai ta janyo wannan tarzomar.
Cikin mamaki ya ce "Wai duk ita wannan Yarinyar ce ta yi faɗa da ɗan daban?"
Usman yayi wani irin murmushi ya ce "Wannan ta wuce tunaninka, ka san ƙanwar maza ce, bamu raineta da tsoro ba"
Adam har cikin ransa ya ji babu daɗi kama Aliyu da aka yi, ya ji da rumaisan aka kama ita da ta janyo abun.
Ya ce "Ko zan iya magana da maman?"
Usman ya ce "Ok, bari na yi mata magana".
Bayan an yi wa Adam iso ya shiga gidan, ya tarar da rumaisa a takure a falon mama, sai rarraba ido take yi, suka gaisa da mama ya sanar mata da Usman ya gaya masa abun da ya faru"
Mama ta ce "To, yakamata ka sake tunani a kan auren nan naku, ku gidan sarauta ba kwa son shirme, rumaisa kuma Allahn da yayi ta ba ta ji ko kaɗan, faɗa da maƙwabta faɗa wai har da ɗan daba, yaron da har kisan kai yake yi"
Adam ya kalli in da rumaisa take, ta haɗe rai saboda yadda mama ke kwance mata zani a kasuwa, ya ce "Me ya haɗaki da ƴan daba, har aka kama Aliyu?"
Shiru ta yi tana wulƙita ido, mama ta ce "Zaki yi bayani ko sai na mareki?"
Ƙasa-ƙasa da murya ta faɗi abun da ya faru, ta wani fannin tana da gaskiya, a kan me zai aiketa sayen sigari.
Adam ya ce "Ba damuwa mama, bari mu je a fito da shi, ba wani state CID, wani station ɗin ne?"
Usman ya ce "Dama yanzu zamu koma da mai sunan baba sai mu tafi gaba ɗaya " wani mugun kallo da mai sunan baba ya yi wa Usman ya sanya yayi shiru, Sarai Adam ya ganshi, dan haka ya ce "Bari mu je da wuri, kuma dole ita ma a tafi da ita".
Mama ta ce "Idan ma sun ƙi yarda, ku basu ita ku dawo mini da Aliyu" sanin ba ta da gaskiya ya sanya ta sunkuyar da kai ta yi shiru.
Mama ta so bin su, amma kasancewar yanzu magana ake ta siriki, mama ba zata iya shiga motar Adam ba.
Bayan tafiyarsu mai sunan baba ya ce "Amma ba kya ganin yawan shigarsu cikin al'amuranmu da yi mana alfarama, ba zai saka nan gaba su cigaba da kawo buƙatunsu ba, kuma ba yadda muka iya sai mun bi ba?"
Mama ta ce "Babana ka san na fi kowa taka tsantsan da gudun duniya, bana jin hakan, shi ya sanya na amince"
Ya ɗan rausayar da kai ya ce "Shikenan, bari na bi su a napep"
Suna tafe Adam yana kallon rumaisa ta mudubi, sai wani gyatsine baki take yi, tana harare-harare kamar mai shirin iskokai.
Cikin station ɗin suka shiga, aka yi musu iso wurin DPO, cikin sa'a suka tarar da malam shamsu a station ɗin yana ta cigaba da zigar kai su Aliyu CID.
Adam ya ce "Case ɗin ƙanina na zo mu yi magana a kai, na san shi ba mai laifi ba ne"
Malam shamsu ya ce "Ta ina, yana mana iƙirarin kisan kai a cikin unguwa"
Usman ya ce "Wai kai malam shamsu meye yake damunka, meye ribarka idan an rufe Aliyu ne?"
Mai sunan baba ne yayi sallama ya shiga, suka amsa masa ya nemi wuri ya zauna.
Adam bai ko kalleshi ba ya cigaba da magana ya ce "Da ku ka caje Aliyu kun same shi da makami?" DPO ya ce "A'a"
"Good, ɗayan fa, abokin rigimar ta sa"
"Eh, mun kama shi da wuƙaƙe da tabar wiwi"
Suna cikin maganar aka shigo da su Aliyu.
DPO ya kalli rumaisa ya ce"Ni mamakina ma da wai duk a kan wannan Yarinyar ce ta haɗa faɗan, ke meye ya haɗaku?"
Ta cunkusa baki ta ce "Cewa yayi na sayo masa sigari, kuma ni ba ƴar iska ba ce ba da zan taɓa sigari ina ƴa ma ce mai mutunci "
Adam a ransa ya ce "Ko wa ya tambayi jinsinta kuma oho'
Malam shamsu ya kada baki ya ce "Ƴar iska kum ta nawa, zance da ya cika unguwa"
Zabura rumaisa ta yi ta ce "Yaya usy ka ji ko? Yanzu idan na yi magana ace ba na jin magana, da kunnenka ka ji yana ce mini ƴar iska, ni fa bar ƴar iska ba ce ba, bana wasan banza da maza, meyasa ake ce mini ƴar iska?" Ta yi maganar hawaye ya wanke mata fuska.
Malam shamsu ya ce "Ke da aka ce an yi garkuwa da ke, ki ka dawo da ɗa, ai ba abun mamaki bane ba, tun da kowa ya san a unguwar nan ba ji ki ke yi b.... Mai sunan baba ya daki tebur da ƙarfi ya ce "Ya isheka malam"
DPO ya ce "A gaban nawa, da rashin mutunci da rashin sanin darajar doka".
Malam shamsu ya ce "Tuba muke Yallaɓai".
Usman yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Uban waye ya saka ki yi kuka a gabnsa, salon ya rainaki, idan ya kuma gaya miki ki ce kin yi