Showing 93001 words to 96000 words out of 181007 words

Chapter 32 - kanwar maza 3 COMPLETE

12 Jul 2024

39277

take sauke numfashi ka san ta gaji da yawa.

Sidi ya ce "Sir amarya ta gaji da yawa"

Adam ya ce "Gashi har ta yi bacci"

Sidi ya ce "Allah mai iko, ba zan manta scene ɗin da ku ka yi making, ranar da ku ka fara haɗuwa ba, and she's now your wife"

Adam ya ce "Shhhhh, a daina tayar da wannan maganar"

"Sorry sir"

Adam ya gyara mata kwanciyarta, ya ɗaukar pose ɗin ta, ya buɗe, ga sababbin kuɗi nan a ciki, fal. Ya girgiza kai ya riƙeta a hannun sa.
Rumaisa kuwa jin ta take kamar a kan katifarta, har da gyara kwanciya.

A ƙofar gida ya tarar da yayyenta, suna jiran su ga ta ina za su ƙaraso, ya sauke glass ɗin motar, gaba ɗaya suka ƙaraso.

"Ta yi bacci fa" ya faɗa yana kallon Usman.

Usman ya ce "Ai haka take, da yin magariba take bin bango, a bata ta ci ta yi bacci, kamar ƴar kaza".

Adam ya ɗagata zaune da niyyar ya tasheta, amma ina baccinta kawai take yi.

Mai sunan baba daga in da yake tsaye, yana hango cikin motar, rumaisa ba ta san ma me ake yi ba. Haka nan ya ji wani irin kishi ya taso masa, ƙanwarsa a kwance a jikin wani ƙato. Takawa ya ɗaga kai suka haɗa ido da shi, ya wani cukule fuska.

Aliyu ya zura hannunsa, ya ɗauko rumaisa gaba ɗaya, ya nufi gida da ita,, da gayya Adam ya fito daga motar, ya ce "Kai Ali ka yi a hankali, kar ka yi mata rauni fa, a kawo mini nakasashshiyar amarya gobe, ba zan karɓa ba, da na san bacci za ta yi daga nan ai gida zamu wuce kawai"
Aliyu ya ce "Tuba nake, zan kula sosai"

Juyawa mai sunan baba ya yi, ya shiga gida, ƙasan zuciyarsa istigfari, da tunanin meye nasa na jin haushi kuma, bayan komai daɗewa dole wataran ta zama matar wani.

Aliyu ya shimfiɗe rumaisa a katifar mama, Gwaggo cewa take "Wannan an yi shashasha amarya, haka take da wannan nauyin bacci haka, ta bar mutane da dakonta".

Mama ta ce a tasheta ta yi sallar isha'i, lawisa ta ce sun yi salla a gidan kwalliya, kafin su tafi.

Tana magagin, mama ta dafa ruwa, ta kaita banɗaki ta wanke mata fuska, ta yi mata wanka tas, ta lulluɓota ta kawota ɗaki, ƴan biki na ta yi mata dariya, sai dai har a cikin ranta ji take ruman ba ta wuce wankan ba, ƙaddarar aure zata rabata da ƴar da take matuƙar ƙauna.

Ɗakin samarin nan kuwa, kusan kwana suka yi babu bacci, suna ta ɗan tattaunawa, a kan biki, da kuma jajanta rabuwa da tilon ƙanwarsu, kuma kallabi a cikin rawunansu.

Mai sunan baba kuwa ya naɗe, ya lumshe idanunsa ya yi shiru, ba abun da yake ganowa sai kai wa da komowar iman a wurin nan, da yadda suke yawan haɗa ido. Tsaki ya ja ya nemi wuri ya kwanta, sai dai tunanin gobe dai-dai lokacin, rumaisa na gidan wani, ya hana shi bacci, ya din ga yi mata addu'ar shiga gidan miji a sa'a.


Bayan idar da sallar juma'a, aka ɗaura auren rumaisa da adam, ƴan unguwar da basu san waye mijin ba a ranar suka ji.
Unguwar ta cika da dawakai, da manyan motoci na alfarma, duk in da ka kalla, jami'an tsaro da kuma masu rawuna ne.

Sai dai tun da aka ɗaura auren nan, rumaisa jikinta yayi sanyi, take ta uban kuka, duk yadda aka so rarrashinta abun ya gagara.


Tuni hotunan biki suka zaga duniya, kowa da abun da yake tofawa, na alkhairi da akasin haka.


Samha kuwa kaiwa take ta yi tana komowa a ɗakinta, tana fatan aikin da ta bayar ayi mata, ya yiwu ba tare da samun wata matsala ko akasi ba, dan ta riga ta ƙudirce wa kan ta ɗaukar fansa, ko da tsiya ko da arziki.

Ammi a wani event center, ta shirya taron wunin bikin, sai dai abu ya so ya zama rigima, in da facalolinta da masu goya wa mummy baya, suka din ga ci mata mutunci, wai saboda Aisha ba ƴar ta ba ce, ta shirya irin wannan biki haka, kuma aka samo yarinya mara galihu ta aurawa mahaukacin ɗan ta.
Duk yadda ammi ta so jurewa sai da ta kusa zubar da hawaye, Nusaiba ba ta da hayaniya, balle iman, Laila ce masifaffiya dama, kuma ba ta ƙasar da ita kaɗai ta ishi duk wani mai bakin magana.

Da la'asar mama ta kira ammi, ta ce mata za a kawo rumaisa nan wurinta, ta gaisheta ta yi mata faɗa, sannan a wuce da ita gidanta, ammi ta ce ba sai an kawota ba, saboda wasu dalilai, zuwa magariba zata turo da waɗanda zasu ɗauki rumaisa.

A yammacin aka yi kilisar dawakai, takawa ya haɗe cikin kayan sarauta, rumaisa ma aka yi mata ado da alkyabba, aka yi ta musu hotuna.



Da magariba rumaisa ta yi wanka, ido duk ya kumbura saboda kuka, Yasir da ya shiga ya fita ya ga tana kuka, shi ma sai ya fashe da kuka, ta tashi ta saka kaya ma abu ya gagara mama sai daurewa take yi, amma hawaye ya cika mata ido.

Jiki a sanyaye mai sunan baba ya shiga ɗakin, ya tarar da ita a zaune, tana kuka mai taɓa zuciya.

"Rumaisa" ya kira sunanta, ta ɗaga kai ta kalleshi.

"Tashi ki saka kayanki, kar dare yayi sosai".

"Dan Allah mai sunan baba ku yi haƙuri, wallahi na fasa ni ba zan tafi na barku ba, mama dan Allah ku yafe mini ku barni na zauna a gida, ni ba zan iya rayuwa babu ku ba" tayi maganar cikin kuka.

"Tom, mun ji, amma fara saka kayan" da ƙyar ya saka kaya, ya ciro turare a aljihunsa ya fesheta da shi, mata sai rangaɗa guɗa ake yi.

Ta riƙe mama tana wani irin kuka.

Ya saka hannu ya cire nata daga jikin mama, ya ja hannunta yayi waje da ita.

Suna fita mama ta shiga ɗaki, ta fashe da kuka, dan an kai in da ba zata iya jurewa ba.

Suna tafe a mota tana kwamce a jikin mai sunan baba, tana ta kuka, kamar ta shiɗe.

"Am sorry, kiyi haƙuri haka lamarin aure yake, da haka kowace mace take tara nata iyalin, Ubangiji Allah ya baku zaman lafiya, ya sanya alkhairi. Ban da rashin kunya da raina miji, mijinki ne ibada zaki je ki yi, ki nemi aljanna na san duk an gaya miki, ki girmama mahaifiyarsa, matar nan ina ganin mutuncinta saboda son da take yi miki. Sannan kuma Sabir ko Allah ya baki naki ɗan, kar ki canza soyayyar da ki ke yi masa, ki yi haƙuri ki saka a ranki, ƙofar sabon ƙalubale zaki buɗe ki shiga. Duk da ƙanƙantarki nauyin aure ya hau kanki sai haƙuri, kiyi haƙuri, ki yi haƙuri, ki jure ki daure duk ƙalubalen da zaki fuskanta wataran sai labari, ina yi miki addu'a Allah ya sassauta miki jarrabawar gidan aure, don babu auren da babu jarrabawa"
Haka ya din ga yi mata nasiha, har suka je gidan, gida ya tsaru kamar ba na rumaisa ba, ko ina ya ji kaya.

Ana kai rumaisa wata ƙanwar ammi, ta sake saka mata alkyabba a kan kayanta, suka din ga yi mata guɗa a ka, amarya ƙanwar maza, dan su suka kawota ɗakin ma.

Sun daɗe tare da rumaisa, kowa da irin faɗan da yake yi mata. Sai da kowa ya watse, Tawagar angwaye suka ƙaraso, gida ba kowa sai tsirarin mutane da zabga-zabgan ƙarti.

Suna zuwa mai sunan baba ya tashi ya ce su tafi.
Rumaisa ta riƙe rigarsa ta tashi tana kuka "Dan Allah yaya umar, kar ku tafi ku barni, ku tafi da ni, ko ku zauna da ni a nan ɗin, dan Allah yaya. Yaya usy, yaya Abubakar, dan Allah duk ku zauna, Abdallah kar ku tafi, Yasir dan Allah" mai sunan baba duk ya kaɗa musu kai alamar su tafi.

Iman tana cikin waɗanda suka rage, gaba ɗaya tausayin rumaisa ya cika mata zuciya.

A hankali ya fincike rigarsa daga hannunta, ya juya, ta sake riƙo rigarsa.

Ya juya a kausashe ya ce "Wuce ki je ki zauna" a razane ta saki rigar ta sa tana kuka.
Yana juyawa sai hawaye, karo na farko da abu ya daki zuciyarsa ya saka shi kuka. Ya saka hanky ya goge, ya kalli Adam ya ce "Ga ta nan amana ce, marainiya ce, ko ka ci, ko kula da ita" yayi maganar wasu hawayen na cika masa ido.

Adam har mamaki yake, wace irin soyayya suke nuna wa rumaisa haka.

Bashir ya ce "Za a riƙe amana in sha Allah. Yallaɓai aje a rarrasheta dan Allah, tana cikin damuwa".

Adam ya ce "Sai ma ka faɗa? Ba daga ni sai ita zaku tafi ku bari, wannan kuma ya rage nawa" dariya abokansa suka yi, suka yi musu addu'a sannan suka watse.

Ya koma ya shiga ɗakin na ta, tana tsaye tana ta kuka, ya ƙare mata kallo sannan ya ce
"Yau sarki mai koriyar alkyabba, ya baki alkyabba saura ɗana ki a kan doki. Sannan ke kuma ki cika alƙawarin sanya shi durƙusa miki a kan gwiwoyinsa".


What's app only please 🙏
Ayshercool.
08081012143
[12/12, 7:33 PM] rahama Jos: *Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*


Rumaisa kasa cewa komai ta yi sai jinjinawa ammi kai, baba uwani kuwa har da shewa tana juyi, tana yi wa ammi godiya da karamcin da ta yi mata, a matsayin wadda za ta je ta yi guiding ɗin ma'aikatan gidan takawa.

Ammi ta yi wa Adam alamar ya bi ta, ya tashi ya bi bayanta ɗakinta, ta kalleshi ta ce "Takawa, na san auren nan ba son ka bane, zaɓina ne amma dan Allah ina sake roƙon alfarmarka, ka yi haƙuri da yarinyar nan, komai zai wuce zaka yi alfahari da auren nan, ka ga yarinya ce ƙarama, dole za ta yi ta koke-koke na rabata da gida da ka yi, dan Allah ka yi haƙuri da ita. Ko dai wani abun ka yi mata?"

Ware ido ya yi ya ce "Ba abun da na yi mata wallahi".

"A'a takawa, dan Allah ayi haƙuri a bata lokaci, yarinya ce sosai sai ka yi haƙuri"

Adam wata irin kunya ce ta kama shi, ya ji tamkar ƙasa ta tsage ya nutse don kunya, ya girgiza kai ya ce "Ban yi mata komai ba"

"Na ji ba wai ina son jin sirrin aurenku ba ne, amma dan Allah ka kula da ita, next week idan Allah ya kai mu za a koma makaranta ko?"

Ya ce "Eh, na biya komai ma, ana komawa zan kaita sai kuma na samo direban da zai din ga ɗaukota idan bana nan"

Ammi ta ce "To shikenan, Allah ya ƙara buɗi"

Suka fito, Ammi ta ce a zubawa su takawa abinci su tafi da shi.

Ammi dai ta lura gaba ɗaya jikin rumaisa a sanyaye yake, har ta fara tunanin ko takawa dai yayi mata wani abun ne.

Ammi ta zauna a kusa da ita, ta yi ƙasa da muryarta ta ce "Rumaisa, ko akwai wata matsala ne?"

Ruma ta girgiza kai alamar a'a.

"To ki yi haƙuri kin ji, zaki saba ne haka aure yake, ki yi haƙuri, duk abun da yayi miki wanda bai yi miki ba ki gaya mini. Sannan su nusaiba sun gaya mini abun da ya faru washegarin kai ki, shi ma ki yi haƙuri ki kawar da kanki, na san zaki fuskanci ƙalubale, amma ki dake. Kar ki yadda da duk wata mata da zata nuna tafi kowa ƙaunarki ko ta shiga jikinki, kuma kar ki sake ki gaya wa wani sirrin aurenki, duk abun da zai yi miki, ba zai yi wanda zai cutar da ke ba, na ja masa kunne sosai da sosai, idan yayi miki abun da ba dai-dai ba, ki gaya mini. Kar ki saki jiki da kowa, sai mijinki ko kuma ni da ƙannensa zama a masaruta sai ka iya allonka, ki yi haƙuri kin ji rumaisana".

Ruma ta ce "To Ammi, in sha Allah "

Har gaban mota ammin ta rakasu, suka shiga suka tafi.

Tun kan su yi nisa ta fara sana'arta ta barcci, ya taɓata ya ce "Idan ki ka yi bacci, sai dai ki kwana a mota, dan ba ɗaukar ki zan yi ba" da haka suka ƙarasa gida ta yi sallar isha'i, ko abincin ba ta ci ba ta kwanta.

Washegari da safe, ta tashi tana ɗan goge gogenta, ta fito falo tana ta goge tiles ɗin.

Adam ya fito cikin suits da jakarsa, da alama aiki zai tafi, ta yi masa ƙuri da ido, ba ta yi magana ba.

"Baki iya gaisuwa bane?"

Ta ɗauke kanta daga kallonsa ta ce "Ba amsawa ka ke yi ba"

"Yes, ba kya gaisheni yadda ya dace ne, ki bar wannan aikin babu wanda ya saka ki, anjima masu aikin da ammi ta ce za su zo, idan da wani abu su gyara miki.
Ga breakfast can a kan dining, in anjima zasu fara aiki, zan sayo kayan abinci, ko kina buƙatar wani abu?"

Ta girgiza masa kai alamar a'a.

"To ki zauna wuri ɗaya, banda taɓe-taɓen abun da ban saka ki ba".

"To sai yaushe zaka dawo?".

"Lokacin da Allah ya yi".

"Ni dai ka dawo da wuri, tsoro nake ji"

***
Gidansu rumaisa kuwa, mama ce ta hana kowa zuwa gidan, saboda ta san halin rumaisa, ta ce idan suka je kuka za ta yi ta ce zata biyosu. Sai dai ba a cikakken awa guda, ba ayi zancenta ba a gidan.

Kasancewar bayan mai hoton da ɓangaren su Adam suka ɗauko, Abdallah ma ya ɗauko mai hoto, aka turo masa hotunan bikin rumaisa, bai yi ƙasa a gwiwa ba, ya tura su group ɗin su, na ƴan gidan.

Mai sunan baba yana kasuwa, da yake bayan makaranta ya kan ɗan shiga kasuwa, hotunan suka shigo.
Suna da yawa ya sauke su, ya fara buɗewa yana kallo, yana kallo yana murmushi yana jin yadda ya yi kewar ƙanwarsa.
Babu tsammani ya ci karo da hotonsa shi da iman, rumaisa kuma a gefensu, ya wuce hoton da sauri, amma ya kuma karo da hoton iman ɗin, na ranar bridal shower, ta yi wani irin kyau na musamman.
Zuciyarsa ta tsananta bugawa, kuma ya kasa wuce hoton nata, ba shiri ya rufe wayar, ya saka a aljihunsa yana ajiyar zuciya, kamar wanda ya yi gudu.

***
"Wallahi Adam na yi mamaki da har ka iya ɓoye mini al'amari mai girma kamar wannan, menene a ciki idan na san wannan yarinyar zaka aura" Jabir yayi maganar cike da ƙorafi.

Adam ya ce "Koma menene bai kamata ka ji haushi ba, yanzu ba gashi ka ji ba, ko da yake gara kai a kan Jamil, ni Jamil zai ɗauki gaba da ni, yaƙi zuwa wurin ɗaurin aurena, ni na karɓi ƙaddarata dan meyasa shi ba zai ɗauka ba".

Jabir ya ce "A'a takawa, so so ne fa, amma son kai ya fi, Samha ƙanwarmu ce ga ta gida, amma ace ka auro wata a waje, wadda ba ta kaita komai ba, babu daɗi".

"Amma har ya kai ayi gaba da ni saboda hakan? Meye aibun rumaisa idan aka kamanta shi da abun da ta yi mini na sadaukarwa, bai kamata gaba ɗayanmu idonmu ya rufe ba, idan akwai rabo a gaba sai ka ga na aureta, amma a yanzu ban zaci haka daga Jamil ba, amma zan shiga wurin aiki, zamu haɗu da shi mu yi magana"

Jabir ya ce "To shikenan, har ka gama amarcin kenan ka fito, bai yi wuri ba komawarka aiki ba kuwa?"

Adam ya yi murmushi ya ce "Bai yi ba, ita ma sai a bar ta ta huta. Kai ni har mamaki nake yi yadda kai  ba a saka maka ido ba, ko auren fari ba ka yi ba, amma ba ruwan wani da kai, duk mu aka sanya wa ido"

Jabir ya yi dariya ya ce "Bayan ka ce ba zaka bani iman ba, ai ni na zaci kai zaka aureta"

Adam ya ɗan ɓata fuska ya ce "Please mu bar wannan zancen"

Jabir ya ce "Shikenan, tun da baka so"

***
Rumaisa ta rasa abun da yake yi mata daɗi, zaman shirun nan duk ya isheta.

Ta saman benen take kallon harabar gidan, da gidajen da ke maƙwabtaka da nata, duk manyan gidaje ne, sannan kowane gida a rufe yake, ko gilmawar mutane ba ka gani, sai dai a cikin mota.

Mai gadin ta ga ya tashi ya buɗe gate, nan da nan ta fara murna ta yi baƙi.

Ta koma ɗakinta da sauri, ta saka hula a kanta, ta fito, sai dai ta yi turus lokacin da ta ga baba uwani, da wasu matasan mata guda biyu.

Jiki a sanyaye ta ce musu "Ina wuni?"

Baba uwani ta yi murmushi ta ce "Ranki ya daɗe ai mu zamu gaisheki, barka da wannan lokaci? Mun same ki lafiya?"

"Lafiya ƙalau" ta amsa a ɗan tsorace.

"To kamar yadda giwa ta yi miki bayani jiya, ga ma'aikatanki nan, sannan kuma ni ce cikon ta ukun, zamu zauna tare da su a nan, na din ga lura da yadda zasu gudanar da aikin".

Rumaisa ta ce "To sannunku".

Baba uwani ta ce "Yauwwa, wani ɗakin zamu zauna, da kayanmu muka zo".

"Ku zaɓi duk wanda ku ke so" rumaisa ta yi maganar tana kallonsu.

Ta nemi wuri ta zauna a falo, baba uwani ta zaƙe ta fara dudduba ɗakunan da suke saman benen.

Ta shiga ɗakin rumaisa, ta ƙare masa kallo, ta fito tana faɗin "Allah ya taimake ki, ashe an shirya miki kayan, ko takawan ne ya shirya miki su?"

Rumaisa ta ce "A'a ni na yi"

"Masha Allah, to bari ɗauki wancan ɗakin, tun da na ga ɗayan kamar babu kowa a ciki"

Ita dai rumaisa ba ta ce komai ba, ta ƙare ta shiga kitchen tana dudduba kayan kitchen ɗin Rumaisa.

Ganin sun isheta da kallo, sauran mata biyun da ko sunayensu ba ta sani ba, ya sanya ta tashi ta koma ɗakinta.

Ta buɗe window ta cigaba da kalle-kallenta, ta hango baba uwani a bayan gidan, tana waya. Ba ta jin mai baba uwani take cewa, sai dai da alama kamar wayar ta ta ta sirri ce.

Baba uwani kuwa cikin ladabi take waya da Samha.

"Ki buɗe kunnenki da kyau ki saurareni, bana son a samu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login