Showing 156001 words to 159000 words out of 181007 words

Chapter 53 - kanwar maza 3 COMPLETE

12 Jul 2024

39278

ta ce A ɗakin iman za ta kwana, duk da ammi ta bata ɗaki, amma ta ce a wurin iman za ta kwana.

Cikin dare iman ta tashi ta yi salloli, sannan ta zauna ta ɗauki wayarta tana dubawa, rumaisa na kallonta, a haka bacci ya kwasheta.

Da safe rumaisa na baccin safe, laila ta shigo da system a hannunta, ta tashi rumaisa.

Ruma ta buɗe ido ta kalleta, "Kin manta hau zaki fara zuwa islamiyya ne? Tashi mijinki zai yi magana da ke"

Rumaisa ta kalleta ta ce "Da computer zan yi wayar?"

Laila ta dungurarwa da ruma computer a gabanta, tana kalla ta ga fuskar takawa.

Ta ce "Laaa video call a computer"

Yayi murmushi ya ce "Hi little mimi".

"Iyee daga zuwa turai har ka koma bature, irin...." Sai kuma ta kalli laila ta yi shiru.

Yayi murmushi ya ce "Ba ki tashi ba ne? Yau zaki fara zuwa islamiyya fa, ki tashi kiyi breakfast, ki shirya a kai ki"

Ruma ta yi miƙa ta ce "Shikenan weekends ma ba zan huta ba".

"Ki yi haƙuri, ina boy, bai tashi ba ko?"

"Eh, bacci yake shi da anty iman, kai har ka karya? Waye ya dafa muku abinci?"

"Har ɗaki aka kawo mana, na karya"

"To yaushe zaku fara taron?"

"Sai Allah ya kaimu anjima" ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Mimi meyasa ki ka bani abun da zai sakani kuka?"

Jiki a sanyaye ta ce "Ba dan kayi kuka na baka ba, ni ba dare ba rana, abun ci mini rai yake, amma ba na ce maka kar ka tambayeni komai a kai ba, sai anjima, bari na ɗan ƙara rage bacci".

"Mimi tsaya ki ji".

"A'a gaskiya sai anjima" ta ture system ɗin ta kwanta.

Laila ta daki ƙafar ruma ta ce "Ke wace irin mashirirciya ce ne?" Ruma ta yamutsa fuska ta kalli ruman.

"Ya tafi wata ƙasar, kuna waya ki kashe? Babu wani abu mai jan hankali, ba rausaya murya ba karairaya, wai ce miki aka yi dan kika ƙanwar maza, ki din ga abu kamar namiji, you are not romantic at all, mijinki matashi ne, kuma kema kin san yana da masu son sa, ko dai ki gyara ko ki ga abun da ba kya so. Ki tashi ki yi wanka ki zo ki karya"

Ta ɗau system ɗin ta, ta bar ɗakin, rumaisa ta zumɓura baki sannan ta tashi.

Laila kuwa komawa tayi, tana jinjinawa takawa. "Takawa i salute your effort, Wannan matar taka, zan iya saka bulala in zaneta wataran, she's very stubborn, beside she's much more than how i expect, ba ta ji ga taurin kan tsiya".

Adam ya ce "Haba madam, duk ita kaɗai, ki yi ta haƙuri kema, halinku ne ya zo ɗaya shiyasa ba kwa jituwa, da ɗaya daga cikin ku na da haƙuri, zaku zauna lafiya, idan ku ka saba shikenan".

"Anya zan iya jurewa? Ba ta ji fa"

"Tuba muke, ayi haƙuri dai".

Rumaisa ta shirya cikin dogon hijjabi, hatta jakar islamiyya da litattafai adam ya sai mata komai, sidi ya ɗauke ta suka tafi makarantar.

Ya je ya gabatar da ita, mai makarantar ta ce ta san da zuwan rumaisa, aka kai ruma aji.

Mamki ne ya cika su kansu ƴan ajin, ganinta sanye da hijjabi irin na islamiyyar, suna mamakin kar dai matar aure ce.

Mai makarantar ta gabatar da rumaisa a wurin malamar da take ajin, zungu-zungui ta wuce ta je ta zauna, tana jin haushin kallon da suke yi mata.

Ajin duk manyan mata ne, dan da yawa sun haifeta, wasu kuma sun yi ƙanwa da ita sosai da sosai.

Aka yi lesson ɗin da za ayi a ka gama, har lokacin tashi ba ta kula kowa ba, sai da aka tashi suka din ga tambayarta ko matar aure ce ita, sai dai ta din ga bin su da ido, taƙi magana.

Sidi ya zo ya ɗauketa, amma ta ce masa ita ɗorayi zai kai ta wurin mama, ya ce ai ammi ba ta sani ba, ruma ta ce ba ruwansa, idan ba zai kaita ba, ya ajiyeta ta je ta hau napep.

Haka ya juya kan motar suka tafi ɗorayi.

A ƙofar gidan yara suka tsatstsaya suna kallon uwar motar da aka kawota a ciki, har da maƙwabciyarsu shamsiyya a leƙowa, tana ɗagowa ruma hannu.

Ruma ta ce 'Lallai matar nan, saboda ta ganni a mota, har da ɗago mini hannu, nan gaba a daidaita sahu zan din ga zuwa, in ga ko za samu masu kulani'.

Ta kalli sidi ta ce "Ba sai ka dawo ɗaukata ba, zamu yi waya da uncle Mahmud" ta shige cikin gida, bakinta ɗauke da sallama.

Gidan shiru, sai Aliyu da yake girki a kitchen.

Ya amsa mata ya ce "Koma bamu san da zuwanki ba, daga tafiyar mijinki jiya, yau kin fara yawo".

Ta ce "Ai da yake ba wurinka na zo ba ehe" ta shiga ɗakin mama, mai sunan baba yana kwance a kusa da mama, yana kallon tv.

Mama ta ce "Ke daga ina?".

"Makarantar matan aure wai ya saka aka kai ni, mai sunan baba ina kwana"

"Lafiya ƙalau"

Ba ta tsammaci wata magana sama da haka ba daga gare shi ba dama, dan haka ta zauna ta ce "Mama jiya ya tafi fa".

"Haka Aliyu ya ce mini, ina mai gidan nawa, ina ƴa ta iman, ki ka zo mini ke kaɗai?"

Mai sunan baba ɗan gyarawa yayi, yana jiran jin amsar da rumaisa zata bayar, a kan iman.

"Mama, ni in koma kenan?"

"Gaskiya dai, ba iman ba mai gidana, sai ke fitinanniya"

"Ai shikenan, gara na koma wurin ammi. Sabir yana nan ƙalau, iman kuma gari ba daɗi, tsoro nake ji kar ciwonta ma ya tashi"

A fuskar mai sunan baba ta ga razana, amma saboda azabar miskilanci yayi kamar bai san me suke faɗa ba.

Mama ta ce "Subhanallah, me yayi zafi haka, yara ƙanana da ku, har kusa abu ya dameku a rai".

"To ammi kin san familyn na su sai a hankali, sun takura mata da yawa, kin san ba ammi ce ta haifeta ba, sau kusan huɗu ana yinƙurin aurenta, wannan muguwar Mummyn tana hanawa, tana cewa mutane ba ta da uba, wai ammi ce garin tsince-tsincenta ta tsinto ta"

Cikin rashin fahimta mama ta ce "Ke kin sani a duhu, kina nufin ba ita ta haifi iman ba?"

"Hmm mama baki san badaƙalar da ke cikin gidan nan ba" nan ruma ta warware mata komai, sannan ta ce "Yanzu kuma wannan jabir ɗin ya ce son ta yake zai aureta, ammi tana ta murna, tun da shi ya san halin da ake ciki, ita kuma iman ba ta son shi sam, akwai wani wanda take so daban, amma ba za ta iya gayawa ammi ba, saboda ammi ta amince jabir ya nemi auren ta, ba wanda ta gayawa sai ni abun tausayi, kuma tsoro take ji kar wanda take so ɗin, ya ji labarin ga a halin da take ciki ya ce baya son ta".

Mama ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, lafiyayyiyar yarinya mai mutunci kamar wannan, babu wanda zai ce ba ita ta haifeta ba, ni cikin yaran nan, da da wanda yake da ƙwari sosai, ai da an auro mini ita, to sai dai ba matar talaka ba ce, ni dai ina ƙaunar yarinyar nan fisabilillahi".

Cikin son sai ta yi pressing ɗin mai sunan baba rumanta sake cewa "Bari kawai ammi, kuma fa baki ga uban samarinta da suke sonta a haka ba, masu kuɗi ta ce ta daina soyayya, kawai ta zo ta fara son wani, amma taƙi gaya mini waye, ba ƙaramin son sa take yi ba. Amma wannan jabir ɗin, ya biyo kai tsaye ta wurin ammi, kuma yana daf da zuwa wurin mai girma wambai, shi kuma wannan wamban ba ɗaga ƙafa, dama yana ta yi wa ammi kashedi, ta aurar da ita ko ta mayar da ita in da ta ɗaukkota, cikin dare ina jin tana ta kuka".

Tsaki mai sunan baba ya yi ya tashi ya bar ɗakin, rumaisa kuwa ta yi wani guntun murmushi, ta tura saƙon yadda yakamata.

Aliyu ya shigo da plate ɗin indomie, ya ce "Me aka yi masa na ga ya fita yana tsaki?"

Mama ta ce "Shi wannan sai an yi masa wani abu ma?".

Ruma ta ce "Za mu ci indomie"

"Ai ko mayya ce ke, sai dai ki ci kan ki"

Tashi ta yi ta koma kusa da Aliyu, ta ce "Dan Allah zan ci".

"Wai ke da mijinki yake ajiye miki komai, ki zo ki saka mini rani".

Ruma ta ce "Allah sarki mijina, ya tafi ya barni, papa saurayina"

Aliyu ya ce "Ke fa baki da kunya ko?"

Flashing aka yi wa Aliyu, ta leƙa wayar ta ga an rubuta "Baby Hibba".

"Ohhh ni ƴa su, yaya Aliyu soyayya?"

Ya harareta, ya kira wayar "Hello my haidar".

"Kuɗin wayar sun ƙare ne ake mini flashing?"

"A'a ba su ƙare ba, bana son ka ɗaga su ƙare ne, kuma ka sake saka wasu, shiyasa na yi maka flashing"

Yayi murmushi ya ce "An taso daga tahfiz ɗin ne?".

"Eh, yanzu na shigo gida ma"

"To shikenan, in ajima zan zo in sake jin haddar. Bari yanzu abinci zan ci"

"To my haidar, ka gaida mama, ka ci ka ƙoshi da yawa".

Rumaisa ta ce "A gaban maman ka ke waya da ƴan mata?"

Daƙuwa ya yi wa rumaisa, ta hau tafa hannaye.

"Yaya Aliyu, habiba ce ta koma sweet hibba?".

"Uban wa ye ya ce miki ita ce"

Rumaisa ta ce "Na rantse da Allah muryar habiba ce, munafuka, habiba take soyayya da yayana, ba tare da tana biyan subcidy ba, dole na je gidansu habiba, mama a gabanki ake soyayya?".

Mama ta ce "Ya ce zuwa za ayi ma ayi masa tambaya, nan da shekara biyu"

Ruma ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Su mai sunan baba ba su yi aure ba sai kai"

"Uban wa ye zai bari kansa ya kulle kamar su? Yaya Abubakar ma kuɗin aure za a kai masa, yana gama service. "

"Innalillahi, yaya Aliyu habiban da ka ke zanewa saboda ni"

Aliyu ya doke mata ƙeya ya ce "Ƴar rainin hankali ba, duk ke ki ka ja, na daki mata ta".

Mama ta ce "Too har an yi auren kenan" da sauri Aliyu ya ɗau plate ya fice daga ɗakin yana dariya.

Wani irin zullumi mai sunan baba ya shiga, ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya kasa gane tausayin iman yake ji, ko tashin hankali ya shiga jin wani na neman aurenta, wani irin kishi ne ya taso masa, tabbas ya fi jabir komai, sai dai jabir ya fishi kuɗi, sannan kuma wa iman take so

Yaya usy ne yayi sallama, rumaisa ta tashi da gudu ta tare shi, ta ce "Mussaman saboda kai na zo gidan nan yaya usy".

Ya ce "Ƙarya ki ke yi".

"Wallahi da gaske, zo mu zauna daga nan"

Ba tara da ta bari ya shiga ko wurin mama ba, ta ja shi kitchen ta rufe ƙofa, sannan ta ce "Yaya usy wani abu ne yake damuna, na ga kaine abokin shawarata, na ce bari na gaya maka".

Ya ce "To ina jin ki"

"Yaya usy, dama...dam..mm"

"Wai meye haka ne?"

"Kunya nake ji ne, amma shawara nake nema. Ka ga dama takawa ne kan ya tafi, yake yi mini abun da bai dace ba, kuma"

"Kuma me? Wane irin abu ne da bai dace ba".

"Yaya usy kiss yayi mini kuma, ba zan iya faɗar sauran ba dai, kuma kaga bai dace ba, bana son mama ta gane, ya ce mini wai ai ba komai, in tambaya in ji, wai tun da ihu nake idan ya taɓa ni, zai ƙara aure, kuma ni bana son ya yi mini kishiya. Dan Allah yaya usy ya zan yi, bana son ɓata tarbiyya ta, idan mama ta sani za ta yi fushi da ni, kuma bana son yayi mini kishiya"

Ayshercool.
08081012143
[12/12, 7:33 PM] rahama Jos: Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please 🙏


Matar da mamaki take kallon ruma, "I don't get you, he is not available like how?".

Maimakon rumaisa ta amsa, sai ta sake kashingiɗa ta ce "Elizabeth ma ta ci ubanta, haka ta gama turancin ta mutu".

Cikin isa matar ta cire gilashin fuskarta ta ce "Kin san wacece ni kuwa?".

"Ina ruwana da ke wacece? Ko da ban san ki ba, na san ba zai wuce kema a danginsu ki ke ba, masu zuwa su ci mini mutunci, ni kuwa dai-dai nake da kowa, wallahi duk wanda ya zageni ramawa zan yi ehe".

"To yanzu zagin ki na yi?"

"Ai na san tatsuniyar gizo, ba ta wuce ƙoƙi, kun saba zuwa ku yi mini wulaƙanci, na sani ko kema abun da ya kawo ki kenan, daga shigowarki sai kallon banza ki ke yi mini, kuma dan raini ki ke tambayata wai ina matar gidan. To ban sani ba ko nayi kama da ƴar shara da wanke-wanke"

Matar ta riƙe haɓa, sannan ta jinjina kai ta ce "Anyway, na ji kece matar gida, kuma ban zo na ci mutuncin ki ba, i want see ma brother please"

Rumaisa ta ce "Ban iya turanci ba"

"Ohh ikon Allah, ina son zan ga ɗan uwana ne, wurinsa na zo".

"To bacci yake yi, idan zaki jira shi to, bai daɗe da kwanciya ba, amma ina fatan ke ba ƴar uwar wannan samhan ba ce ba?"

Matar ta yi murmushi ta ce "No, am not" ta saka hannu a jakarta, ta ciro waya, cikin harshen Ingilishi take magana, da accent ɗin da rumaisa ba ta iya fahimta, ta ajiye wayar.

Bai fi mintuna takwas ba, sai ga takawa ya fito.

Da sauri matar ta miƙe, ta nufe shi, kamar zasu rungume juna, suka yi musabaha, ta sumbaci hannunsa ta ce "Takawarka lafiya ranka ya daɗe, gaba salamun baya salamun"

Adam yayi murmushi ya ce "Ke dan Allah yaushe ki ka sauka? Kuma da safen nan na je gidan mai girma turaki, na ji kasala nake ji, ban ƙarasa gidan ba, kuma jiya fa har 5pm muna gidan.

"Around 11 na ne gida, na cewa ammi kar ta gaya maka, yau na ce ammi ta saka a kawoni, na zo na ganka na ga amarya, and i met this little arrogant creature, screaming at me that why should I ask for you. She even claims that she's your wife, but i doubt  she is the one in the pictures. She looks innocent and matured in picture".

Takawa yayi dariya ya ce "She's the one, rumaisa kenan maman sabir".

Jiki a sanyaye ta ce "Adam, na ga yaron fulani, so cute, yaron kyakykyawa da shi".

Rumaisa da ba ta kula su ba, ta ce "Tubarkallah".

Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ruma ya ce "Mimi, ga Anty Laila, cousin sister ɗina, da muka tashi tare, kuma uwar ɗakina. Tana aure a canada da mijinta da yaranta".

"Au ai ban santa ba, kuma da ta zo ba ta gaya mini ita ce ba, na zata kawai ƴan uwanku ne masu zuwa gida, su yi mini wulaƙanci, shiyasa ban kulata ba".

"To ai ba duka ƴan uwan mu ne, masu yi miki wulaƙancin ba, ku gaisa mana".

"To ita kuma ya ake gaisheta, kar in yi ba dai-dai ba ta ƙi amsawa, ba zan sake gaisheta ba"

Yayi murmushi ya ce "Ita wannan baturiya ce ai, kowace irin gaisuwa ki ka yi mata zata amsa".

Rumaia ta sake kallon laila sannan ta yi murmushi ta ce "Sannu da zuwa, ina wuni? Ya hanya ya iyali, sannu da zuwa"

Ta ce "Yauwwa thank you"

Ta tashi tsaye ta je ta kawowa laila ruwa da lemo, ta kawo mata kayan shayi ta ajiye, ta haɗo da cornflakes duk ta ajiye mata.

Laila ta ce "Ya zan yi da duk wannan kayan, kar ki takura kanki, na ƙoshi ni".

"A'a kar ki je ki ce, kin zo gidana ba a baki abinci ba. Na san lokacin breakfast ya wuce, amma dai ki sha shayi, ko cornflakes, akwai fruit ma, yanzu zan je na ɗora girki".

Laila ta ce "Girki kuma? Ba naga akwai maids ba, na ga baba uwani ma na nan, kar ki ciwo a kitchen fa".

Rumaisa ta ce "Ai da yake a unguwar ɗorayi nake, na iya duk wani girki da yakamata, ni ba ƴar masu kuɗi ba ce, kar ki damu da yarinta ta, na iya abinci gidanmu ba ƴar aiki".

Adam ya ƙunshe fuska yana dariya, rumaisa kuma ta nufi kitchen, tayi ƙasa da murya ta ce "Yenyenyen, ta wani shaƙe murya tana turanci, har da saka wando, babba da ita wai ita baturiya, Elizabeth ma ta gama saka wandon da mini skirt, aka haɗa da ita da turancin aka binneta".

Laila kuwa ruma na barin falon ta ce "Bros yanzu da gaske this is your wife?"

"Yeah, ta canza miki ne, ita ce dai ki ka gani a hoto".

Laila ta ce "Taɓɗijan, amma ba ta da kunya, a tsaye take, amma tayi ƙarama takawa".

"Haba dai, yanzu ai ta ciko, ta yi ƙiba, rigima kam akwai ta har da ta sayarwa ma, sai dai duk da haka bamu fi wata ɗaya ba, na fara jin daɗin zama da ita. She's very intelligent, fiye da yadda ki ke zato, wauta da ƙuruciya ne dai damuwarta".

Nan ya bata labarin yadda rumaisa ta dawo da sabir, da yadda aka yi har ya aure ta, zuwa yanzu da suke tare, da abubuwan da take ta hasaka masa, a zamansu.

Laila ta yi ajiyar zuciya ta ce "Well, amma ba ta da kunya gaskiya, a haka ku ke zaune?".

Ya ce "Ya ki ke zagar mini mata ne, zaki shiga sahun Black list ɗin mu fa".

"Am serious matarka ba ta da kunya takawa"

Sai ya tuna abun da ya faru jiya, ya ce "Kin san family ɗin mu sai a hankali, gida suka zo suke yi mata rashin mutunci, ta rama. Kin san ƙanwar maza ce ba tsoro. Haka nan muke lallaɓawa muke tare, ake rainonta kan Allah ya sa ta gama hankali, ko me za ta yi, ta cancanci ayi mata uzuri, kuma in kula da ita, abun da ta yi mini, ko duniya na bata ban biyata ba"

"Haka ne, amma ban gane ake lallaɓawa ake rainonta ba, haka ku ke zaune kana kallonta tana kallonka"

Yayi dariya ya ce "Ina ruwanki ne?"

"Babu, amma tun a hotonta nayi mamakin yadda ka auri ƙaramar yarinya haka,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login