Showing 36001 words to 39000 words out of 181007 words

Chapter 13 - kanwar maza 3 COMPLETE

12 Jul 2024

39262

su jabir.

Wayarsa ta cika masa kunne, duk da gandar da yake ji, da ya gaji da jin rurin wayar, sai da ya tashi ya ɗauko wayar ya duba.
Kakin rundur ƴan sanda ne cp baba habu yake kiransa, adam ya ɗaga wayar tare da yin sallama.
Cp ya amsa masa suka gaisa sannan ya ɗora da cewa "Adam kana garin nan kuwa? Wai ba zaka fito ka yi magana a kan abun da yake faruwa ba, sai sharri ake yi maka kala-kala kai kuma ka ƙi magana"

Adam ya yi ajiyar zuciya ya ce "Me zan ce? Ko na faɗa ba za a yarda da ni ba, ƙanin mahaifina ya fito ya wanke ni, amma ba a fasa surutu ba, me zan ce? Su yi ta yi idan sun gaji za su daina ne"

"Kana nufin ba zaka ce komai ba?"

"Ko na ce ba za a daina ba, ka ga maganar ba ta da amfani"

Cp ya ce "Ai shikenan, ɗazu mun yi magana da commissioner, saboda sabon posting ɗin da gidan jaridar nan ke cigaba da fitarwa, na yi magana da manema labarai, na sanar musu hukumar ƴan sanda mun san da case ɗin, sai dai abu ne na sirri da ba ya buƙatar a fito ayi ta yayatawa, shi ya sanya muka yi shiru muka yi ta bincike, kuma haryanzu muna kan yi ma."

Adam ya nemi wuri ya zauna a gefen gadonsa ya ce "To shikenan yallaɓai, na gode sosai da sosai"

"Kar ka damu, ai hakkinmu ne baka kariya, kuma abun da muka faɗa hakan yake ai, Allah ya tsare, wannan ba wani abu bane ba duk aikin maƙiya ne, kuma ba za su yi nasara ba"

Adam ya ce "Haka ne, na gode sosai"

"Masha Allah, Allah Ya ƙara tsarewa"

"Amin ya rabb sir, na gode" daga haka ya kashe wayar. Yana gama wayar ya ji zaman ɗakin ya ishe shi, dan haka ya fita domin ya gaida ammi ya ɗan fita.

Duk a falon sashen ammi ya tarar da su, har ammin, ana koyawa Sabir zama an shiryashi cikin wasu kaya masu kyau, an zaunar da shi a gefen kujera, cikin dabara iman tana taje masa sumar kansa, sai kai hannu yake yana turewa alamar ba ya so.

Adam ya fara gaida ammi, sannan ya ɗau sabir ya zauna da shi a jikinsa.

Adam ya karɓi brush ɗin hannun iman, ya cigaba da taje masa kai, amma ya cigaba da kai hannu yana turewa yana son yin kuka.

"Kai rigimamme, baka son gayu?" Adam yayi maganar yana murmushi tare da kallon ɗan nasa cike da ƙauna.

Sabir yayi shiru yana kallonsa.

"Yi mini dariya mana, an ce kana dariya amma ba ka taɓa yi mini ba"

Ammi ta ce "Kai ai wannan ɗan naka kai ya yo, babarsa kawai yake washewa baki gaba ɗaya yayi mata dariya, har mamakin irin soyayyar da ke tsakaninsa da ita nake yi, da ya ganta har wani ƙara nutsuwa yake yi".

A ransa ya ce 'Aikuwa ba zan ba ta riƙonsa ba, ya tashi a sangarce da rashin kunya kamarta ba' ya ɗaga kai yana kallon ƙwayar idon sabir, take aisha ta sake faɗo masa a rai, dan suna ɗinar kama da sabir, duk da ya fi kama da shi.

Ammi ta ce "Ina ta magana ka yi shiru, tunanin me ka ke yi ne?" Yana ɗago ido Ammi ta ga hawaye kwance a idonsa.

Cikin damuwa ta ce "Lafiya kuwa?"

Yayi murmushi ya ce "Lafiya lau ammi"

Ammi za ta yi magana, hadimarta ta shigo, ta durƙusa ta ce su Samha ne suke neman iso.

Ammi ta ce, ace su shigo.

Samha ce da ruƙayya, suka shigo tare tana ganin adam sai da ta yi hamdala a zuciyarta, ta wani lumshe ido, wata irin ƙaunarsa da soyayyarsa na sake ratsata.

Suka ƙarasa, suka gaida ammi ta amsa musu cikin fuska, samha ta kalli adam ta ce "Yaya ina kwana?" Ta yi maganar cikin rausaya.

"Lafiya ƙalau, kuna lafiya?"

"Lafiya ƙalau, sabir na zo gani, ammi yaushe za'a kai mana shi ne? Na gaji da jiran na kasa jurewa".

Ammi ta ce "Banda abunki samha, yaron ai haryanzu jariri ne, ba a haɗaku da jego ba".

"Haba ammi, tun da muka rasa fulani ai shi ne madadinta"

Ta matsa kusa da adam, za ta ɗau sabir a hannunsa, sai da ta taɓa shi, wani irin kallo take masa ji take kamar ta rungume shi, ko ta samu sassauci a kan abun da take ji game da shi.

Ta ɗauki sabir tana yi masa murmushi, wanda a ƙasan zuciyarta ji take kamar ta buga shi da ƙasa, dan yadda ba ta ƙaunar uwarsa shi ma ba son sa take yi ba.
Miƙa sabir yayi ya hau kuka, duk yadda ta so ta rarrashe shi yaƙi yin shiru, ya cigaba da kuka ba shiri adam ya karɓe ɗan sa, ta ji tamkar ta dunƙule hannu ta daki kan yaron ko ta huce.

Cikin iya siyasa ta ce "Ammi wai har ya iya ƙyuya ne?"

"To gashi dai ya yi miki, ɗan na ku ne ɗan ganin dama, ko dariyarsa babarsa kawai yake yi wa"

Da sauri samha ta ce "Wace babar ta sa?"

"Rumaisa, yarinyar da ta zo da shi"

Jin an ambaci labarin da Mummy ke son ji ya sanya ruƙayya cewa "Ai ammi haryanzu tana nan?"

"Tana nan mana, ina za ta je?"

"To ammi zuwa take ta ganshi?"

Kan ammin ta bata amsa samha ta ce "Ai an ce mini an kai ta wurin turaki rannan ko?"

Ammi ta ce "Eh"

Ruƙayya ta sake cewa "To ammi gidan nan take zuwa?"

Maimakon ammi ta ba ta amsa sai ta ce "Ruƙayya an ce mini Mahmud ya zo gari ko?"

"Eh ya dawo"

Ammi ta ce "To masha Allah"

Iman ta ɗauko baby carrier ta ce "Yaya kawo na saka shi a Carrier ko zai koma barci, na ga yana ta rigima dama yau da wuri ya tashi"

Adam ya ce "Zo ki ɗau abunki iman, na fuskanci duk abin da na yi iman sai kin nuna mini ban iya ba, ni ban san a ina ki ka koyi raino ba, tun da mu dai ba jariri ne da mu ba"

Iman ta yi dariya ta ce "Ni na isa?"

"Gashi nan kuwa" yayi maganar cikin sigar wasa. Ya bawa iman sabir ya tashi ya bar falon, a rayuwar duniya samha ba ta kishi da aisha kamar yadda take yi da iman, saboda akwai alaƙa mai kyau a tsakanin takawa da iman, ga iman da kyau tamkar ita ta yi kanta.

Suka gama zamansu, daga bisani suka tashi za su tafi, Samha ta ajiye wata leda cike da kayan sawa da na wasa, wai sabir ta kawowa, ammi ta yi mata godiya sannan suka tafi.

***
Ba kowa a gidansu rumaisa, kowa ya fita da masu makaranta da sauransu, sai mama itakaɗai, kasancewar ta ji sauƙi, ya sanya ta ɗora abincin rana, dan ba ta son su dawo ba ta kammala abinci ba, yanzu ƙaramarsu babbarsu za ta zo ta fara kwanciya da tura baki ita yunwa.
Sai dai babu tsammani ta ga kiran ammi a waya.

Ta ɗaga wayar suka gaisa, ammi ta kuna yi wa mama ya jiki.
Sun ɗan taɓa hira sannan ammi ta ce "Yauwwa maman rumaisa wata magana nake son mu tattauna da ke, duk da kamata ya yi na zo ƙafa da ƙafa, ina da wasu baƙi ne da zan yi yau, kuma maganar yakamata mu yi ta"

Mama ta nutsu ta ce "To ina jin ki, Allah ya sa lafiya".

"Yauwwa, zuwa wannan lokaci tun da Allah ya riga ya haɗamu, mun riga mun zama ɗaya, tun bayan da na baro ku, nake ta tunani a kan maganar da ki ka yi mini a kan rumaisa, da kuma wasu dalilai na makomar jaririn nan, shine na yanke shawarar mai zai hana adam ya auri rumaisa, kin ga maganar wata gulma da ɓacin suna ya ƙare, kuma kin ga za ta samu cikakkiyar damar kula da sabir kamar yadda take buƙata, amma me ki ka ce?"

Jiki a sanyaye mama ta ce "Aure kuma rumaisan? Shekararta goma sha uku fa, kina ganin yadda ake fama da ita, ga kuma karatunta".

Ammi ta ce "Maman rumaisa ba zai gagara ba, mu ma duk da ƙuruciyar aka yi mana aure, kuma ba abun da zai samu karatunta, za ta cigaba idan aka yi auren nan ni da adam za a yi wa alfarma kuma ina tabattar miki in Allah ya yarda zai zama alkhairi, yanzu amsarki nake jira, zan kai maganar ga magabatansa, tun kan ace za a bashi wata matar, ban san wa za a bashi ba, ko dan makomar rayuwar marayan nan".

Mama ta yi ajiyar zuciya ta ce "Haka ne, amma gani nake rumaisa ba za ta iya raino ba, ita ma ba hankali ta cika ba"

Ammi ta yi murmushi ta ce "Babu damuwa, ai ba sakar mata rainon za a yi ba, ya zamana dai ta samu kusanci da shi sosai yadda take so".

"To, bari yayyenta su zo mu tattauna, abun da suka yanke shikenan"

Ammi ta ce "To, Allah ya sanya mu ji alkhairi, ina saurarenku dan da wuri nake son ayi komai a gama"

"To shikenan, duk yadda muka yi zaki ji ni" tun da suka yi sallama mama ta kashe wayar take zullumi. Ayi wa rumaisa aure ta je ta yi me a gidan auren? Yarinyar da ban da zunzurutun ƙuruciya da wauta ba abun da yake damunta.

A haka mama ta ɗora girkin nan, take aikin jikinta duk a sanyaye.

Rumaisa ce ta yi sallama, ta shigo da jakar makarantarta a ka, tana yamutsa fuska.

Mama ta kalleta ta amsa mata, rumaisa ta jefa jakarta ɗaƙi, ta cire hijjabinta ta kalli mama ta ce "Mama ki aika aje a yi wa mai ice warning ba ruwansa da ni, me na yi masa da idan na zo wucewa zai din ga cewa gata can, sau biyu yana yi mini, kar na yi abun da ba shikenan ba a zo ace na yi tom" tana gama maganar ta ɗau buta ya wuce banɗaki.

Bayan ta fito ta kalli mama a taɓare ta ce "Mama wai ba a gama abincin ba, ni fa yunwa nake ji" mama ta bi ta da kallo tana hango rumaisa da aure.

Ta gama taɓararta mama ta kammala girki, ta ci ta tafi makaranta, sai da yamma da mai sunan baba ya dawo, mama ta yi masa zancen.

Aikuwa ya haɗe rai ya ce "Dama na san ɗawainiyar da suke yi da ita, dole a ƙarshe su nemi wani abu, wane irin aure yaushe aka haifi rumaisan da har za a wani ce a aureta, mutumin da faɗa suke yi ba sa shiri, kawai ki ce musu ba zai yiwu ba su yi haƙuri".

Kasancewar usman yana nan ya ce "A'a fa ayi tunani, yarinyar nan kuna ganin abun da take yi a kan yaron nan, me ake nema a aure ne ba mutum na gari ba, kuma in da za a iya riƙeta ba, idan ta amince kawai ayi musu fatan alkhairi a nawa ganin, mussaman yanzu da ƴan unguwa suke ta ƙananan maganganu a kanta, wataƙila ana yi mata auren ta nutsu"

Wani mugun kallo mai sunan baba yayi masa, dan haka yayi shiru, kuma tun da ya kafe a kan ba ya so, ba zai canza magana ba.

Gaba ɗaya hankalin mama ya rabu biyu, kowannensu yana da gaskiya, ita kanta ba ta shirya rabuwa da rumaisa yanzu ba, dan Allah ya sani rumaisa ba za ta iya ɗaukar ɗawainiyar aure a yanzu ba, dan a sangarce take, sai dai kuma tana matuƙar jin nauyin ammi ta ce mata ba zata basu auren rumaisa ba.

Ayshercool.

08081012143
[12/12, 7:33 PM] rahama Jos: *MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR  DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1.  Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2.   Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3.  Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4.  Supplements na karawa fata kyau da sheki  glowing skin*

*5.   Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6.   Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7.   Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8.  Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9.  Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10.  Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11.  Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12.  Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13.  Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14.  Supplement na whitening/glowing skin*

*15.  Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

*Littafin kuɗi ne, ₦500 ne, via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*






Cikin tsananin farinciki ammi ta ce "Da gaske rumaisa kin amince?"

Ruma ta jinjina kai, ammi ta ce "Alhamdilillah, Alhamdilillah Ubangiji Allah ya yi muku albarka, Allah ya sanya muku albarka, in sha Allah tarayyar nan za ta zame muku alkhairi, Allah ya albarkaci rayuwarku".

Mama ta amsa da amin.

Mai sunan baba kuwa, yana so ya shigo iman tana tsaye a hanyar da zai wuce, sai waya take cike da iyayi da shagwaɓa, ya ɗan jira ta gama ya wuce, amma ba ta da niyyar gamawa dan ba ta ma san ya zo wurin ba.
Ga ƙamshin turaren da take yi duk ya cika masa hanci, yana neman ya sanya shi atishawa.

A ƙarshe dai ya ƙule cikin dakakkiyar muryarsa ya ce "Ke! Bani hanya zan wuce!"

A razane ta saki wayar ta ja da baya, zuciyarta na bugawa da sauri da sauri. Cikin hanzari ta durƙusa ta ɗau wayarta da screen ɗin ya tsatstsage.

Ammi tana ta zuba addu'a, amma jikin rumaisa ya yi sanyi, sai dai duk da jikinta ya yi sanyi, bai hana ta yin dariya ba.
Ammi ta ce "Rumaisa, ya na ga kina dariya kuma, meya baki dariya ne?".

Rumaisa ta ce "Mai sunan baba ne ya tsorata miki ƴa da wannan muryar ta sa"

Tana rufe baki sai ga iman ta shigo jikinta yana tsuma ta ce "Ammi wayata ta fashe".

Ruma ta ƙunshe baki tana dariya ta ce "Sorry, haka yake, ya daɗe yana jiran ki gama waya ya wuce, baki matsa ba, shi ne yayi miki tsawa".

Ammi ta ce "Subhanallah, maman rumaisa haka baban nan naki yake, daga baƙunta sai faɗa, bai san autar tawa matsoraciya ce ba, ai shikenan bari mu fita sai a sai wata wayar".

Mama ta ce "Hmm mai sunan baba ai sai dai Allah ya shirya, ƴaƴa ne gasu nan kowa da halinsa, ki yi haƙuri kin ji iman, ban ji daɗi ba wallahi"

Adam ya ce "Ammi lokaci fa, ina son yau zan kwana a gida, zan yi wani aiki".

Ammi ta ce "Haka ne, dare ya fara yi, rumaisa, ba zan fasa godiya ba, ubangiji Allah ya saka da alkhairi, Allah ya sanya muku albarka, sauran magana duk yadda ake ciki zan yi magana in Allah ya yarda.

Suka fito tsakar gida, takawa ya kalli rumaisa wani takaici ya ƙule shi, wannan fitsararriyar abar ce zai aura.

Yaya Abubakar ne ya shigo, ammi ta kalleshi ta ce "Malam faruku kai ne ka razana mini ƴa ko? Kuma ka ce baka son in haɗa auren ƴaƴana haba mai sunan baba laifin me muka yi haka ne"
Abubakar ya yi murmushi ya ce "Ina wuni"

"Lafiya ƙalau ya gida ya ƙoƙari?"

"Alhamdilillah"
Iman ta ɗan ƙura masa ido, kamar ba wannan ne mai muryar nan ba.

Mama ta ce "Ɗan uwan mai sunan baba ne, shi gashi can a bayanki yana jinki, wannan dattijon arziki kenan malam habu"

Ammi ta ce "Au, ashe fa ƴan biyu ne ai ni duk kama suke yi mini" ta waiwaya ta kalli mai sunan baba ta ce "Mun zo neman aure gidanku ka hana, a sassauta adawar nan ba a san in da rana za ta faɗi ba, ina da tarin ƴan mata a gidana kar ka zo neman aure nima na rama".

Suka yi dariya gaba ɗaya, mai sunan baba ya ɗan sunkuyar da kai be ce komai ba.

Ammi ta ɗora da "Dan Allah ayi mana addu'a,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login