Showing 9001 words to 12000 words out of 36102 words

Chapter 4 - MATAR SHEGE HAUSA NOVEL

28 Mar 2025

3647

uku,ni dai ina ta raba ido da fargaba,tunda na ga abun zab'a ake yi,kuma na ga kwalliyata duk ta fi tasu kyau,hakan ya b'ata min rai kad'an.Me kiran mutanen ya na sake shigowa kiran wata na yi sauri na tashi ina fad'in"kai! Ni ce zan je"

Ya ce"ai ke da Oga na yiwa tanadi,amma taho idan kin matsu"

Na yi saurin komawa na zauna na ce"a'a,shikenan zan je wurin ogan"

Ba a jima ba kuwa ya ce na fito,Oga ya k'araso.Na tashi na bi bayansa,sai kuma na ji wata fargaba ta dira a zuciyata,na fara hasashen watak'il Salim ya na ganina zai koreni daga aikin,wannan tunanin ya sanyaya min jiki,haka dai mu ka k'arasa har wani d'aki,ma'aikacin ya ce na shiga yanzu zai shigo

Na hau bin d'akin da kallo bayan na shiga, kujera ce zaman mutum uku,sai wani k'aramin firji da kuma wata loka y'ar k'ara,ga tebur a gaban kujerar me d'auke da k'aramin faranti me kyau sai walwali ya ke,wanda na ke kyautata zaton shi ne na zuba tokar tabar,sai da na kalli teburin da kyau sannan na lura da zanen harafin (J) me kyau sai k'yalli ya ke yi,na kai hannu na tab'a ina tunanin abin da J d'in take nufi.

Ina jin motsin bud'e k'ofa na yi saurin zama a k'asa,nan gaban teburin ina sauraron yanda zuciyata take bugu.

"Assalamu alaikum" Ya yi sallama ya na shigowa,na amsa cikin kashe murya wai ko zan burgeshi

Bai kalli inda na ke ba ya zo ya kwanta rigingine a kujerar,ya fara danna waya

"Ina wuni" Na gaishe shi.

Sai ya juyo ya na kallona,ko so ya ke ya ganeni oho,ya min kallon sakanni ya juya ga wayarsa sannan ya ce"lafiya k'alau".

"Za a kawo wani abun?" Na tambaye shi a d'arare.

Ya yi shiru kamar bai ji ba,sai can kuma ya ce"ina zuwa".

Ganin ya bawa banza ajiyata ya na ta harkar wayarsa sai nima na zuge jakata,na d'akko wayata,na tank'washe k'afa na shiga y'an danne-danne na

Wajan minti talatin mu na haka,sannan ya tashi zaune ya ajiye wayar ya kalleni ya ce"bud'e lokar can ki d'akko min sigari"

Na tashi tsam,na je na bud'e sigarin ce a ciki da yawa,da maganin tari suma kala-kala,sai wasu k'ananun robobi masu murfi,wanda ban fahimci abin da yake ciki ba,gida d'aya na d'akko,na duk'a na ajiye a teburin cike da ladabi

Ya d'auka ya zaro d'aya,ya kunna ya fara zuk'a,ni kuma na d'auki farantin na matso kusa da tebur d'in sosai,sannan na sunkuyar da kai. Ni sai na ji kamar hannuna ya ke ta kallo,ko tsarguwa na yi oho!

Sai da ya shanye su duka,ya na kad'e tokar a farantin,hannuna duk ya sage amma hakan bai sa na ji ina son barin kusa da shi ba

Kamar daga sama na ji muryarsa"Zinatu ki ke ko?"

Gabana ya fad'i,don da na yi zaton bai ganeni ba,ashe ya gane.Na d'ago na kalle shi a d'an tsorace na ce"na'am".

Sai ya kalmashe yatsun sa wuri d'aya sannan ya ce"me yasa ki ke bibiya ta?"

Na yi saurin fad'in"na rantse da Allah ba bibiyarka na ke yi ba Salim,ka fahimceni".

Ya kalleni na y'an sakanni,sannan ya ce"ta ya zan yarda ba Junaina ce ta turoki ba?"

Na ji dam! Na fara nazarin wacece Junaina? Sai kawai sunan na shi ya fad'o min (J.S) to ko dai J d'in ta na nufin Junaina,amma wace ita d'in? Kuma meye alak'ara su?

"Ki na shirya k'aryar da za ki fad'a kenan...". Ya katse min tunani

Bai rufe baki ba na yi saurin fad'in" a'a wallahi,ni ban san wata Junaina ba, kuma ba ni da wata alak'a da ita,babu wanda ya turo ni".

Ya jinjina kai sannan ya ce"ok! To ko dai so na ki ke yi?"

Na ji wani dam! Har numfashina sai da ya tsaya na sakan d'aya,to meyasa zai min wannan tambayar haka kai tssye? wannan ai k'ure ne kuma wace amsa ya kamata na ba shi? Na fad'a masa an kusa aurena,ko kuma na ce masa son shi na ke yi? Kai! Ba zan yi masa k'arya ba,ni dai burgeni ya ke kawai,amma ban sani ba fa ko ya ya kamu da so na ne,kar na je na yi abin da zan yi danasani

Muryarsa ta katseni
"Da ke na ke magana"

"Eh" Na fad'a a tak'aice.

Sai na kalle shi, jin ya yi shiru,na ga hannuna kawai ya zuba wa ido,ban ankara ba na ji ya rik'o hannun nawa me d'auke da zanen J.S,ya k'ura ido ya na kallo na y'an sakanni sannan ya wurgar da hannun ya fara magana

"Me yasa d'azu kika yi min k'aryar burgeki kawai na ke yi? Ba ke ce kika fara furta min kalmar so ba,amma na yi mamakin salonki,kin san meyasa?"

Ni dai na yi shiru kaina a k'asa,na kasa ba shi amsa

Ya ce"ok! Shikenan,ba sai kin ji ba".

Na yi saurin d'agowa na kalle shi,saboda har ga Allah na so na ji dalilin,amma kamar an d'aure bakina na kasa yin magana

Ya tashi tsaye ya na jan d'an bak'in gemunsa da ya k'ara masa kyau ya fara magana"ba na sonki,kuma ba zan tab'a son ki ba"

Na ji wani dum! A k'irjina

Ya d'ora"ke ba ma ke ba,duk duniya babu wata mace da zan so bayan Junaina,ita kawai na ke so kuma ita kad'ai ce matata in sha Allah! Ko na auri wata macen sab'anin ta to fa sai dai ta yi zaman amsa sunan matar aure kawai,don ko gangar jikina ba za ta samu ba bare kuma zuciyata".

Ban san lokacin da na fara kuka ba,sai da na ji d'and'anon gishiri a bakina,na ji wani dunk'ulallen abu ya zo ya tare min mak'oshi,raina ya b'aci sosai,zuciyata ta yi bak'a k'irin,cikin y'an sakannin na fahimci tabbas son Salim na ke yi,da kuma kishin sa me k'arfi.

"Kin gama aikin ki,za ki iya tafiya"

Ya fad'a ya na d'aukar wayarsa,ya saka a aljihu zai fice

Da k'yar na tattaro yawon bakina na had'iya,wai ko zan iya had'iye abun da ya tokare mak'oshi na,sai na samu damar magana.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*


Page 8



"Na yarda zan yi zaman amsa sunan matar auren,in dai aurenka ne!". Na fad'a kamar wanda ya bani zab'i

Sai ya juyo ya min wani kallo me kama da harara,ban damu ba na d'ora da fad'in" ban damu da gangar jikinka ba,ko ban samu zuciyarka ba babu matsala,ganinka ma kawai zai wadatar da ni".

"Don Allah!" Na fad'a ganin ya tsaya kallona.

Sai kawai ya buga tsaki ya bar d'akin.Na jima zaune a wurin ina hawayen rashin gaskiya,to rashin gaskiya mana,idan ba haka ba har yaushe na fara son Salim da zan ji yanda na ji yau don ya fad'a min ba zai tab'a so na ba? Duka fa ban dad'e da sanin shi ba, ko gidansu ban sani ba bare iyayenshi.Kuma ni da na ke shirin yin aure nan da sati shida me ya kaini jefa kaina a irin wannan matsalar?

"K'addara!" Zuciyata ta ba ni amsar da ta gamsar da ni

Ina nan zaune a wurin manager ya turo k'ofar ya shigo d'akin,ya buga min wata kafirar harara kafin ya ce"wallahi yau da kin sa an kore mu daga aiki sai mun sa an rushe gidan ubanki! Shegiya me bak'ar k'afa,daga zuwanki yau kin b'ata ran Oga,har ya na zancen zai rufe gidan..."

Bai k'arasa ba na zabura na mik'e,hankad'ani aka yi? Tsalle na yi,iska na bi,duk ban sani ba amma ni dai idan na ce k'arasawa ta wurin shi na yi sakan d'aya na yi k'arya,na wanke shi da wani zazzafan mari,don har hannuna sai da ya d'auka,ina huci kamar zakanya na ce"k'arya ka ke yi wallahi! Ubana ya fi k'arfin ka,kuma kai k'aramin d'an iska ne,iskancin lungu ka ke yi,ka biyo ni eriyata ka gani don ubanka!".

Ina gama maganar na fice daga office d'in,zuciyata na tafarfasa,ni na yi zaton ma zai biyoni wallahi,amma sai na ji shiru,watak'il hak'uri ne da shi,ko kuma ya ji tsorona ne oho! Shi dai ya sani

Adaidaita sahu na tare na shiga na fad'a masa inda zai kaini,duk da hasken da ke titi tarwai bai hanani gane dare ya yi ba,na share hawayen da suka zubo min,na kifa kaina da guiwa ban d'ago ba har sai da me adaidaita ya ce min an k'araso

Sauka na yi,ina shirin duba jaka na d'akko masa kud'insa,jaka ta ce d'aukeni inda ki ka ajiyeni,sai yanzu na tuna ko jakata ban tsaya d'auka ba,tana office d'in Salim,takaici ya rufeni kamar na saka kuka na kalli me adaidaita na ce"ka ga na manto jakata a inda na je,don Allah ka yi hak'uri na tsallaka,naje gida sai na d'akko maka".

"Kutt! Amma dai kin san ko yaro ba zai yarda da wayon ki ba ko? Malama sallameni tun ranki bai b'aci ba!" Ya yi maganar ya na fitowa daga ciki ya murtuke fuska

Muna tsaye muna jayayya sai ga hannu d'aya ya zo wucewa.Hannu d'aya abokina ne,tsabar k'arfin sa ne yasa ake ce masa hannu d'aya,don ance duka d'aya yake wa mutum ya baje

Na yi farinciki kuwa,na k'wala masa kira daga inda muke,ya k'araso cikin takunsa na masu k'arfi ya na k'ara bubbud'ewa ya ce"kai! Zinatu tamu,me ki ke yi a ta nan da daddare?"

Na kwashe duk yanda muka yi na fad'a masa

Ya yi wa me adaidaita wata dank'a,ya matse wuyansa ya ce"kai! Har ance maka za a kawo maka kud'inka amma ka tsaya ja da ta wajanmu?"

Ya fizge daga rik'on ya ce"ai hakki na ne,dole ta ba ni,ba wani shege wallahi!"

Hannu d'aya ya ce"kai! To da alama ba ka da iyalai,idan kuma akwai to maza ka musu waya ka sanar da su inda za su zo su kwashe ka"

Sai ya karkace ya zaro wuk'a y'ar k'arama ya cakumo shi

"Na shiga uku! Ni fa ban saka ba don Allah kar ka sa caka masa"

Na fad'a cikin rud'ewa,don har rik'e hannunsa na yi.

Mai adaidaita ya rud'e ya shiga ba shi hak'uri, sai ya hankad'a shi kusa da ni ya ce"au! Ka ce kai shege ne? To duk'a ka bata hak'uri".

Ba shiri ya zube a gabana ya na bani hak'uri, har abun ya bani dariya,na shiga yinta

Hannu d'aya ya ce"za ka ware ko sai na maka d'ayan? Don dai hakkin ka ne da yau babarka ba za ta ganeka ba,k'aramin d'an iska!"

Shi dai bai tanka ba ya shiga mashin d'in ya ja shi a miliyar.Wannan abun shi ya d'an wanke min zuciya ya rage min damuwa,muka jero da Hannu d'aya ina fad'a masa inda na je.


Na yi mamakin ganin gidanmu a bud'e,tunda na san Baba da wuri ya ke rufe k'ofa,na tura na shiga da fargaba.A tsakar gida na tadda Baban ya na zaune ya zuba tagumi,na yi sallama na zo zan wuce shi sum-sum

"Zinatu!" Ya kira sunana da alamun fushi

Na dawo ina d'an rage tsayina na ce"na'am Baba".

Ya ce"daga ina kike?"

Na yi shiru kaina a k'asa

Ya nisa can ya ce"wata rayuwar kuma ki ke shirin shiga ko Zinatu?"

Lokaci d'aya na gane inda zancen sa ya dosa,kuma na ji babu dad'i a raina,da k'yar na bud'e baki na ce"a'a Baba,daga wurin aiki na ke wallahi".

Bai kulani ba ya shige ya je ya rufe gidan,ya dawo ya shiga d'aki.Ni ma na yi d'akina,ko kaya ban canza ba na kwanta ina tunanin ta yanda zan samu jakata da wayata.

Ni dai ba zan koma wurin ba,musamman yanda na mari manager, sai dai na tura Hannu d'aya ya amso min,amma kuma ina tsoron manager ya sa a kama shi fa,da dai wannan zulumin bacci ya kwasheni.

Da asuba bayan na idar da sallah,na je na gaida Babana,ya amsa babu yabo babu fallasa,har zan tashi ya na ji muryarsa ya na cewa"Zinatu! In dai na isa da ke,to daga yau kar ki sake fita ko k'ofar gida,har sai ranar aurenki,ko Habibu ne ya zo ya shigo cikin gida".

Gabana ya yanke ya fad'i,nan take zuciyata ta shiga bugu don kuwa na ji Baba ya na bani umarnin da ba zan iya yi masa biyayya ba

"Amma Baba jiya na manta wayata a wurin aiki,yau zan je na karb'o". Na fad'a kaina a k'asa.

Baba ya min shiru kamar bai jini ba,har tsawon lokaci,ganin haka na san ba zai yi maganar ba,watak'il ya amince ne ko kuma ya yi fushi da maganata,ni dai na tashi na koma d'akina na kwanta ina ta nazari.




Salim gida ya wuce kai tsaye,zuciyarsa na tafarfasa,ya kwana biyu bai shiga irin wannan halin ba,ya na takatsantsan da duk wani abu da zai sa ya tuna farkon had'uwar shi da Junaina,shi yasa ko kad'an ba ya shiga sabgar wata macen.Duk da Junaina ta na cikin rayuwar shi har yau,har gobe ma amma ba ya son tuna farkon k'ulluwar alak'ar shi da ita

Baby ce ta shigo d'akin,kallo d'aya ta yi masa ta san ya na cikin damuwa,ta k'araso ta zauna a kujera ta ce" akwai matsala ne Bros? Me ya ke damun ka?"

Ya yi shiru ya na kallonta,sai ta d'age kafad'a ta ce"ai na sani,wannan yarinyar ba za ta tab'a barinka ka ji dad'in rayuwa ba,ta hana ka aure,kuma ita ta k'i ta aureka! Ka duba fa ka ga yanda ta maida kai,ta na son haukata ka,ta maida kai d'an maye,amma ka k'i rabuwa da ita,meyasa?"

Ya sauke numfashi da k'arfi ya ce"a'a Baby,da gaske na rabu da Junaina,farincikin ki shi ne nawa.Wata ce yanzu ba ita bace".

Baby ta share hawayen da ya zubo mata ta ce"da ka damu da farinciki na da tuni ka yi aure Bros.Ka fito Ammi ta na kiranka".

Daga haka ta bar d'akin ta na hawaye,ya tashi ya bi bayanta ya na jin damuwa sosai da hawayen y'ar'uwar tasa.


K'arfe takwas na safe Ummi ta aiko wata y'ar mak'otan su,na zo ta na kirana,na d'an tsorata da kiran,ina tunanin watak'ila an fad'a mata an ganni jiya da daddare,haka dai na shirya wajan k'arfe goma na tafi gidan

Tun zuwana jikina ya yi sanyi,ganin damuwa a fuskar Ummi,na gaisheta ta amsa babu yabo babu fallasa,na tashi na je d'akin Umma na gaishe ta,wai ko zan d'an y'antu a wurin Ummi,na dawo na zauna na sunkui da kai kamar a gaban malamina na ke.

Shiru na d'an lokaci,sannan Ummi ta ce"wai ke Zinatu me yasa ba kya jin magana? Ni fa gabad'aya na rasa inda ki ka sa gaba,ban san me ki ka d'auki rayuwa,ki fad'a min abin da ya ke ranki!"

Na yi shiru,idona ya ciko da k'walla.Ta d'ora da fad'in"jiya Ummaru ya ke fad'a min ya ganki a kamfani wai kin je neman aiki,da wa ki ka yi shawara Zinatu? Ko mahaifinki ne ya tura ki?"

Sai na ji sanyi a raina,tunda ba laifin jiya da daddare bane,ni har na manta ma mun had'u da Kawu Ummaru,dama na san bakinsa ba zai yi shiru ba,na tausasa murya na fara magana

"Don Allah Ummi ki yi hak'uri, ban yi da wata manufa ba,ni na je neman aikin ne saboda na rage muku wani nauyin akan auren nan,amma tunda ba ko so ba,na bari in sha Allah".

Ummi ta ce" haba Zinatu! Waye ya fad'a miki ba za a yi miki komai ba? Kuma ko za ki nema da kanki tun da ba ki yi ba sai yanzu da aski ya zo gaban goshi? To ki kiyayeni Zinatu,abun naki ya isheni haka!".

Tuni hawaye su ka zubo min,na dinga ba ta hak'uri, har sai da na ga alamar ta hak'ura sannan na ce mata zan tafi, ba ta bari na tafi ba sai da ta bani abin kari na ci na k'oshi.


Mai hali dai ba ya fasa halinsa,ina fitowa daga gidan su Ummi kai tsaye laundry d'in Salim na wuce,yau ma da na je ban sha wuyar ganin wannan ma'aikacin da ya bani bayanan Salim ba,mu ka gaisa na rok'e shi ya kwatanta min wurin gyaran jikin Baby k'anwar Salim

Tiryan-tiryan ya kwatanta min,na yi masa godiya na kama hanya.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*


Page 9



K'arfe goma sha d'aya a shagon Baby ta yi min,na shiga wurin da sallama,ba wani girma ne da shi sosai ba,akwai ma'aikata su na ta aikin su,da tsirarun mutane da ake yiwa gyaran jiki,na ja kujera na kame ina raba idon ta inda zan ga k'anwar Salim d'in,duk da dai ban tab'a ganinta ba, amma na san idan na ganta zan ganeta,tunda jini ba ya b'uya

"Hajiya me za a yi miki? Gyara,ko kwalliya?". Wata ma'aikaciya ta tambayeni

Na d'an ji dam! Don kuwa dubu d'aya da d'ari biyu ne a jakata,don duka kud'ina su na cikin jakata da na manta ta a d'akin Salim,don haka ban shirya wani gyaran jiki ba

"Amm...Baby ba ta shigo ba?" Na tambaye ta,don ni dai burina na ga yarinyar

Ta ce"ai ba ta zuwa da wuri,da yake ita kwalliya kawai take yi,kin ga kwalliyar an fi yin ta da yamma,sai k'arfe uku take zuwa.Mu mu na yin kitso,k'unshi,wankin kai,da kuma gyaran jiki".

Na sauke numfashi na ce"ga shi kuma kwalliyar na ke so,unguwa zan je kuma sauri na ke yi,don Allah ko za ki kirata ta yi min?"

Ta ce"to bari na gwada,Allah yasa ta na free"

Ta d'auki waya ta kirata,ta yi mata bayani,sai ta kalleni bayan ta gama wayar ta ce"lallai kin yi sa'a,ta ce ga ta nan zuwa".

Na ji sanyi a raina,na yi mata godiya ina gyara zama

Babu jimawa ta zo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login