Showing 3001 words to 6000 words out of 36102 words
Ya sake jan wani tsakin ya ce"kin kirani ne don ki koya min sunanki? To na haddace,menene wai?"
Gabana ya d'an fad'i,na shiga tunanin abin da zan fad'a masa,don ni kaina na san ba ni da wani dalili me k'arfi,na yi ta maza na ce"amm...jiya na ganka za ka shiga laundry,sai na ga ka burgeni,na so na yi maka magana ban samu dama ba,to kuma da daddare..."
K'itt! Na ji ya kashe wayar,tun kafin na k'arasa,na yi saurin sake kira amma sai na ji ta k'i shiga,ina dai zargin a blacklist ya sakani.
Na yi shiru ina nazarin yanda zan yi,kamar wadda aka min umarni, na fara rubuta masa sak'o kamar haka,
_"Idan ba ka ji dad'in maganata ba ka yi hak'uri don Allah,in sha Allah ba zan sake yi maka makamanciyar wannan maganar ba"_.
Ina ta jiran amsar shi amma shiru,kamar an aiki bawa garinsu,ina nan zaune ina nazari har aka kira la'asar ,na tashi na gabatar sannan na yi wanka na saka hijjabina har k'asa na fita waje,kai tsaye gidan su Hamza na yi,na tsaya a k'ofar gida na yi sallama da shi,a nan dakalin k'ofar gidan mu ka zauna mu na ta fira kamar abokai,sai magriba na tafi gida,don Habib ya fad'a min ana sallar isha'i zai shigo.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 3
Habib d'an'uwana ne,mahaifinsa da mahaifina uwa d'aya uba d'aya suke,a unguwar Tudun wada gidansu ya ke,kuma shi ne babba a gidansu,ya na da k'annai mata harda sa'anni na,amma ba ni da wata mu'amula da su,sai dai idan mun had'u a sabga ta y'an'uwa mu gaisa.Ya na so na tun ina cakuikuya ta,tsananin son da ya ke min ne ma ya sa ya fara bani tausayi har na ke sauraron shi,don idan na ce ina son Habib na yi k'arya,sai dai zan iya cewa ya na burgeni da kuma k'auna ta jini.Shi likitan ido ne a asibitin Nasarawa,ba k'aramar wuya ya ci ba wurin shawo kaina har na amince da auren shi,kuma sosai ya ke bin duk wani sharad'in da na gindaya masa kamar mahifiyarsa,duk wata sai ya k'irga dubu goma ya bani,ya ce na yi k'ananun buk'atuna,duk dan kar abun hannun wani ya hure min ido,nasiha ba ranar banza sai dai idan bai zo ba.
Tun ranar da aka saka ranar auren mu,ya tare abokaina Anas da Hamza,wanda na fi shak'uwa da su duk cikin abokaina,ya yi musu gargad'in babu su babu ni,kar ya sake ganin sun kula ni.
Anas ne ya zo har gida ya ke fad'a min,aikuwa nan take na yi wa Habib kiran gaggawa.Aikuwa ya sha madarar bala'i ranar,sosai na nuna masa muhimmancin abokaina,na gargad'e shi kan ko kallon banza ya yi wa wani daga cikin su,to a bakin auren shi,don wallahi a ranar zai kar'bi kud'in auren shi.Nan ya yi ta bani hak'uri, duk ya rikice,har ya so bani tausayi ya ce ya ji,ya yarda,babu ruwan shi da su.
Bayan isha'i ya zo,mun d'an jima muna fira har ya ke sanar min wani satin za a kawo kayan lefe,shirin sa kawai ya ke cikin zumud'i,da farinciki.Ni kuwa tsakanin farinciki da akasin sa ban san wanda zan ce ina ji ba.
K'arfe goma na dare na sake gwada lambar Salim amma har yanzu ba ta shiga, ni sai yanzu na ga ragon azanci na,da ban tambayi wurin da aka ce ya ke aiki ba, sak'o na aika masa kamar haka _"Amincin Allah ya tabbata a gareka,ina yi maka fatan alkhairi,da kuma fatan dawwamar farinciki a zuciyarka,murmushi ya tabbata a kyakkyawar fuskarka har abada"_,
_"Daga Zinatu"_.
Na yi murmushi kamar ina da tabbacin ya gani,na yi addu'a na kwanta da tunanin sa.
Salim ya na zaune ya na chatting sak'on ya shigo wayarsa,ta'be baki ya yi bayan ya gama karantawa,ya na jinjina haukan wasu matan.
Washegari tun da safe na aika masa sak'on fatan alkhairi,kuma na sake gwada kiran layin nashi bai shiga ba,don haka na fita na siyo sabon layi, ina saka shi a waya,ban yi sanya ba na loda kati nadoka wa Salim kira,lokacin k'arfe goma da rabi na safe,har ta katse bai d'auka ba,hakan ya sa na sake danna wani kiran,sai ya d'aga da sallama, na tashi zaune k'irjina yana bugu,don ban shirya abin da zan fad'a masa ba,tunda ban yi zaton zai d'aga ba,haka na daure na amsa sallamar sannan na gaishe shi,ya amsa kafin ya ce"da wa nake magana?"
"Zinatu ce,don Allah ka saurareni". Na fad'a ina fargabar zai saurareni ko zai kashe wayar?
Guntun tsaki ya yi kafin ya ce"to ya aka yi? Ki na ta takura min fa,za ki fara shiga hakkina!".
Da d'an fad'a ya yi maganar,hakan ya sa ni nutsuwa,na d'an yi nazari na y'an sakanni,can na tuna me adaidaita sahun nan... ya fad'a min shi ne yake kula da kamfanin su na Sharad'a,sai na yi saurin fad'in"e... dama akan kamfanin ku ne,na Sharad'a..."
Na d'an dakata don na ji yanda zai d'auki zancen,amma sai na ji ya yi shiru,alamar ya na jira na cigaba
Cikin in'inar da ban san ina da ita ba sai ranar na ce"e da dama, shi ne na ke son...na yi siyayya".
"Siyayya ta me?" Ya tambayeni.
Nan fa k'irjina ya bada ras! Na rasa abin fad'a, tunda ban san sunan kamfanin bama,bare na san abin da ake siyarwa,wannan fa shi ne ga k'oshi ga kwanan yunwa,ga shi ya bani lokacin sa,kuma damata ta na neman kufce min,to aiki ne na fara shi sama ta ka babu shawara...
"Ina da abin yi fa" Muryarsa ta katse min tunani.
Dabara ta fad'o min na ce"idan babu damuwa mu had'u a office mana?"
Ya ce min"ai dole sai na ji yanayin cinikin naki,idan babu yawa ba sai kin ganni ba ma,don yau ina hutu ba na zuwa kamfani".
Na d'an tsorata,don ba na son ya taro jirgina,hakan yasa na yi ta maza na ce"gaskiya da yawa,don za mu yi wajan mota uku".
Sai da na kai k'arshe kuma na ji tsoro,yanzu idan gwalagwalai suke siyarwa fa? Shi ne zan siyi mota ukun? Lallai na iya tarar aradu da ka!
"Zan iya ganinka?" Na fad'a, jin ya yi shiru.
"Ok,gobe litinin sai ki shigo k'arfe d'aya na rana"
Ya katse kiran,bai jira amsata ba.
Hmmm! Na sauke ajiyar zuciya,ina tunanin yanda goben za ta kasance,can kuma sai na zaro ido da na tuna ai ban ma san kamfanin ba,ya ilahi! Yanzu kuma idan na tambaye shi adreshin kamfanin ai na kwafsa,sai ma ya d'agoni,na san dai Sharad'a da girma take,ta ina zan fara neman wani kamfani? Phase 1 zan je,ko phase 2,ko kuma 3 d'in zan yi? Da na san sunan wurin ne ma to da sauk'i,amma gaskiya ba zan tambaye shi ba,don wannan babbar damar da na samu ba zan bari ta kufce min ba.
Da tunanin mafita na yi wunin ranar,ko k'ofar gida ban fita ba,jikina duk ya yi sanyi,ina jiran zuwan gobe.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 4
K'arfe goma sha biyu na kammala shirina tsaf,har da kwalliya na yi,na baza turare,na yi kyau sosai kuwa,da kuzarina na yi shirin,duk da idan aka kira tafiyar tawa da sauri ba wurin zuwa ba a yi k'arya ba.Ko girki ban tsaya yi ba,don haka na fara biyawa ta gidan Ummi ko zan samu wani abun
Girki na tarar ta na yi,na gaisheta ya amsa ta na tambaya ta inda zan je,na ce mata babu inda zan je,na zo gaisheta ne kawai
Ta ce"to tashi ki daka min yaji,dama ba son dakan nake ba".
Na d'an kalli agogo,na tashi na ajiye mayafina na hau dakan,ina ta sauri kar lokaci ya yi ban k'arasa ba,bayan na gama ma sai da ta bani yankan salak,abincin ma kad'an na ci,saboda sauri,na ce mata gida zan koma akwai aikin da zan yi.
"Sharad'a" Na fad'a bayan na shiga adaidata sahu
Sai da muka d'au hanya na ji ya ce"phase 1?"
Na ce"ka san wani kamfani a can? Sunan me kamfanin Salim"
Ya ce"na meye kamfanin?"
Na furzar da iska na ce"wallahi ban sani ba"
Ya ce"ai dole sai na san ko na meye,kafin na san sunan me wurin.Yanzu ina za mu yi?"
Na yi jim,kafin na ce"kai ni Sharad'an kawai"
Ya ce"to bari na kaiki phase 1 don ya fi yawan kamfani"
"Na gode" Na fad'a ina duba wayata,da agogo ya nuna d'aya saura kwata.
A daidai wani babban kamfani ya saukeni,na ba shi kud'insa ina kallon wurin da aka rubuta ALBARKA FOOD'S LTD da manyan bak'i,har ya ja mashin d'insa zai tafi na yi saurin tambayar shi na ce"don Allah nan d'in me da me su ke yi?"
Ya ce"kema kamar ba y'ar Nigeria ba? Ai duk wani nau'in kayan abinci taliya,macaroni, couscous, shinkafa,da kika ga an saka ALBARKA to a nan ake had'a shi"
Na sake kallon wurin,ina jinjina kai alamar gamsuwa,sannan na ce"kuma baka san sunan me kamfanin ba?"
Ya ce"ai sananne ne,na san shi,sunan shi Muhammad, amma am fi ce masa Oga Js".
Na d'an tab'e baki na ce"gaskiya ba shi bane,na gode".
Gaba na k'ara,ina ta kalle-kalle kamar y'ar k'auyen da ta fara zuwa birni a ranar,duk kamfanin da na gani komai girman sa ko k'ankantar sa sai na tambayi me kamfanin,ni dai ban ji kamfanin Salim ba,ban yi aune ba na ji kiran sallar azhar,na yi saurin duba wayata na ga k'arfe d'aya da rabi
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Na furta,ina jin bak'inciki,yanzu ya na can ya na cewa na yi masa African time. Na yi ta zagaye a Sharad'a har biyu da rabi,ganin zan yi asarar lokacin sallah na hak'ura na tari adaidaita na koma gida,takaici kamar zan yi kuka
A gajiye lik'is na shiga gidan,ko sallama ban yi ma,don gani nake da na bud'e baki da nufin magana to kuka ne zai biyo baya,sai dai ina shiga na ga abin da ya k'arasa d'ugunzuma zuciyata
Hauwa ce y'ar Mama tsaye a k'ofar d'akina,sanye da doguwar rigata ta yi rolling da mayafina ta na ta d'aukar kanta a hoto,na daskare ina kallon yanda ta ke malkwad'e-malkwad'e kamar musaka,takaici ya rufeni,cikin k'araji na ce"bura'uban nan!"
"Hauwa! d'akina,kika shiga ki ka d'akko kayana,kika saka?"
Ta juyo da sauri,cikin rashin gaskiya ta kalleni,sai kuma ta had'e rai ta zo za ta shigeni,na funcukota na wanke ta da mari,ta d'aga hannu za ta rama na murd'e hannun,aikuwa ta cakumeni mu ka shiga bawa hammata iska,kamar y'an dambe,na yi mata matsiyacin duka don na fita k'arfi,kuma na girmeta,na yi mamakin rashin fitowar Mama,har muka gama,na shige d'aki,Hauwa ta na ta zagina,ni dai ban sake kulata ba,na yi wanka na yi alwala,na tada sallah
Ina sallamewa na ji shigowar Mama gidan,ashe duk budurin da muka yi ba ta nan "Hauwa! Kin gama shirin kuwa? Ko sai ta dawo kina shashanci?"
Ni dai ban fito ba,ban kuma san amsar da ta bata ba,sai can Mama ta shigo d'akina cikin kwantar da murya ta ce"haba Zinatu,Hauwa ai k'anwarki ce,meye kuma don ta rab'i arzik'inki? Wannan ma ai wani girman ne,saurayin ta ne ya ce zai zo su je gaida hajiyarsa,to sai naga tunda masu hali ne bai dace ta je a tsiyace ba,shiyasa na ce ta ari kayanki ta sa,idan ta dawo sai ta wanke miki"
"Na ji!" Na fad'a a tak'aice.
Ta tashi ta fita,ta na min godiya,sai kuma na ji ban kyauta ba,na ma rasa meyasa na harzuk'a haka,kodayake dama a k'ufule nake,kuma ta k'ara b'atan rai da ta shareni
Kwanciya na yi,ina jin yanda k'afafuna suke amsawa,saboda yawon da na sha,na yi zaton ma Salim zai kirani ya tambayi dalilin rashin zuwana,amma sai na ji shiru,ni kuma ban kira shi ba,don ban san abin da zan fad'a masa ba
Zuciya duk a jagule na yi wunin ranar.Na yi ta nazari kafin na samu mafita,wadda nake fatan ita ce kawai za ta sadani da Salim idan na samu dama.
Washegari goma na safe a laundry d'in su Salim ta min,ko gidan Ummi ban je ba,don kar yau ma ta zaunar da ni.Kai tsaye na shiga,na yi ta dube-dube kafin na ga wanda ya bani lambar Salim,sai na yafito shi da hannu,na ja gefe na tsaya,ya zo muka gaisa,na d'an yi jim kafin na ce,
"Magana nake son yi da kai me muhimmanci"
"Ina jinki" Ya fad'a ya na min kallon sama da k'asa.
Na ce"don Allah ina son duk wani bayani akan Salim da rayuwarsa".
Ya d'age gira alamar nazari sannan ya ce"ke d'in wacece? Kuma meyasa ki ke son sanin Oga Salim?"
Na furzar da iska na ce"ba ina shirin cutar da shi bane,kawai ya na burgeni ne,kuma ina son shiga rayuwar shi".
"Ko gwamnati ba ta aikin banza". Ya fad'a ya na yiwa jakata kallon gefen ido.
Duk da na fahimta amma na ce"ban gane ba"
Ya ce"a nawa zan baki bayanan?"
Na ce"dubu biyu ne a jakata"
Ya ce"tabb! Aikuwa y'anmata Salim ya fi 2k,k'ara ki sha bayani"
Na zuge jaka,na zaro dubu uku na ba shi.Ya je ya d'akko kujeru guda biyu ya zauna a d'aya,nima na ja d'ayar na zauna,sannan ya fara kwararo bayani...
"Sunan shi Muhammad Ibrahim Muhammad,an fi kiransa da Salim,wasu kuma su na ce masa Oga Js.Shi kad'ai ne namiji a gidansu,ya na da k'anwa sunan ta Baby,ban san sauran y'an gidansu ba,ita d'in ma na ga su na zuwa nan ne wataran,da alama dai akwai shak'uwa sosai a tsakaninsu"
Na jinjina kai, alamar gamsuwa,ina sake sauraron shi,ya d'ora"wannan wurin wankin nashi ne,J.S shop ma na shi ne,kuma ya na zama sosai a wurin,musamman da daddare,kuma wurin cin abinci na 7:30 ma na shi ne,don an ce yawanci ma da daddare a can yake zuwa ya ci abinci.Akwai kamfanin mahaifin shi a Sharad'a phase I,sunan shi ALBARKA LTD,kuma Salim d'in ma a can yake aiki,a haka za ki ganshi kamar d'an wulak'anci,amma kuma ba haka bane,yana kirki,shi dai kawai ba ya son rainin hankali,kuma ba kowa yake sakarwa fuska ba,a iya sanin da na yi masa,da kuma yanda nake jin labari ba shi da buduruwa ko d'aya,kuma ya na shaye-shaye"
"A yanda na ji duk gidansu babu me zaman banza,ance ita ma Babyn ta na da wani wurin gyaran jiki a nan Sharad'an,na dai manta sunan wurin".
Na jinjina kai,ina tunanin ashe jiya kamfanin na shi aka kaini,na wuce shi a rashin sani
Na ce"na gode sosai, na ji dad'in bayanan ka,ba wani abun kuma?"
Ya ce"e to,zan iya baki hotunan shi,ina da su kala uku,biyun a ranar birthday d'insa na ga ya d'ora a dp,ya na girmama birthday sosai,d'ayan kuma drivern sa ne ya tura min,da yake abokina ne"
Da sauri na bud'e xenda ya tura min,sannan na rok'e shi lambar abokin na shi,da ya ce drivern shi ne,ya saka min,na yi masa godiya,na bar wurin da mad'aukacin farinciki.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 5
Gaskiya na ji dad'in had'uwa da wannan ma'aikacin,ni sai bayan na tafi ma na tuna ko sunan shi ban tambaya ba,bare lambarsa.Tun a adaidaita sahu nake ta kallon hoton Salim kamar an min dole na haddace kamannin sa kafin cikar mintuna,ya yi kyau sosai fiye da yanda bakina zai iya fad'a, gaskiya shi kyakkyawa ne,sai na ji ya k'ara burgeni fiye da da,na d'aura hoton a fuskar wayata,yanda da na danna zan ganshi,ba sai na sha wuyar shiga wurin hituna ba.
Ranar fa na samu assignment,haka na wuni ina k'are masa kallo,ga wani abu da ya ke ta azazzalar zuciyata,wanda na rasa gane ko na mene,kuma gabana ya na d'an fad'uwa idan na tuna da shi.
Gidan Ummi na wuce don na fad'a mata zancen kawo lefe ranar Juma'a,ina shiga na ci karo da Kawu Ummaru k'anin Ummi,ya na shirin fita daga gidan,na d'an rusuna na gaishe shi,ya amsa har ya wuce ya juyo ya ce"ke Zinatu,kamar ke na gani jiya a cikin adaidaita sahu wajan Sharad'a?"
Na ji fad'uwar gaba,don shaf na manta a wajejen yake aiki,na yi saurin fad'in"a'a Kawu,sai dai ko kama".
Ya gyad'a kai ya wuce,na sauke ajiyar zuciya na shige.Bayan mun gaisa da Ummi na fad'a mata Habib ya ce ranar Juma'a za a kawo lefe,Ummi ta ce"too! Ikon Allah,to Allah ya kaimu"
Na amsa da"amin".
Na ce"Ummi ai dai nan za a kawo shi ko?"
Ta ce"a'a,gwara dai akai gidan babanki Zinatu,y'an'uwana duk za su je,daga baya sai a dawo da shi nan d'in ko?"
Na ce"to"
Sai ta ce"kira min Halima a wayarki,sai na sanar musu gobe su zo mu yi d'an soye-soyen tarar bak'i"
Na kira na mik'a mata,su na fara wayar Umma ta k'wala min kira,na fita ina had'e gira.Nasihar ce dai take ta min,ga shi dole na zauna na ji,tunda Ummi ta na nan,haka dai na yi ta kallon bakinta don ba komai ma nake fahimta ba, hankalina ya rabu biyu,ina ta tunanin da ya ke shirin aurena
"Zinatu!" Na ji muryar Ummi
"Na'am" Na amsa,ina saurin tashi,don dama Umma ta isheni
Sai dai ina shiga wurin Ummi, na yi saranda ganin yanda ta k'urawa fuskar wayata ido,na ji wata fad'uwar gaba,tuni na fara tunanin amsar tambayar da ba a kai ga jefo min ba
"Zinatu wannan kuma waye?". Ummi ta tambayeni
Na yi murmushi na ce"kai Ummi! Saif Ali Khan ne fa,wannan na fiml d'in indiyan,ba ki gane shi ba?"
Na fad'a ne ba don suna kama da Salim ba,sai dan shi d'in ne kawai sunan shi ya zo kaina
Ummi ta ce"to ni da kallo bai dameni ba? Yanzu kalle-kalle ki ka koma kenan,maimakon k'arfafa ibadarki,tunda ba islamiyya kike zuwa ba?"
Na ji dad'in yanda ta yarda da ni,ina kwanciya a katifa na ce"a'a fa Ummi,kawai burgeni ya ke yi wallahi".
Ummi ta rik'e hab'a ta ce"e lallai! Ke da za ki yi aure nan da wani lokaci,shi ne har wani ya