Showing 6001 words to 9000 words out of 36102 words
ke burgeki?"
"Uhm! Inji me ciwon baki" Na fad'a yanda ba za ta ji ba.
"Abba,ka d'an k'ara min lokaci zan zab'a nan ba da jimawa ba in sha Allah!" Salim ne ke yiwa mahaifin shi maganar cikin son kwantar masa da hankali.
Abba ya ce"yawwa yaron kirki! Ba wai ina son takura maka bane ba fa,amma ina son ka fahimci shi auren zai k'ara maka nutsuwa da hankali,kuma kamalarka za ta k'ara cika,babu mamaki ma ka daina wannan d'abi'ar taka..."
Salim ya sunkuyar da kai ya ce"Abba na daina fa..."
"Za dai ka daina,tashi ka tafi Allah ya yi maka albarka". Mahaifin nashi ya fad'a ya na murmushi.
Bai jima da shiga d'aki ba Baby ta shigo da sallamarta,bakin gadon da ya ke kwance ta zauna,ta rik'o hannunsa ta matse kafin ta ce" Bros tashi mu yi magana,na san ba bacci ka ke yi ba".
Ya bud'e ido,ba tare da ya kalleta ba don kar ta fahimci halin da ya shiga,ya ce"Baby! Ina lafiya,ki je ki huta,za ki rakani J.S anjima".
"Ba zan je ba!" Ta fad'a da k'arfi.
"Dama na sani,matsalarka kenan Bros,haba! Kai fa namiji ne cikakke,son kowa k'in wanda ya rasa,akan me za ka na wahalar da kanka akan wacce ba ta da imani? Ta na neman lalata rayuwarka,amma ka k'i fahimta,na tsaneta!"
Sai ta fashe da kuka,ta tashi ta bar d'akin a guje.Ya yi saurin durowa daga gadon ya bi bayanta.
Ranar Juma'a aka kawo kayan lefena,akwati shida da manyan jakankuna guda biyu,cike da kaya kowa ya yaba da k'ok'arin Habib,kuma aka tsayar da rana sati shida masu zuwa
Hmmm! Sati shidan da suka zame min kamar shekara shida,a cikin sati shidan nan komai ya faru,idan na ce komai ina nufin komai da komai,a cikin wa'innan satuttukan ne na aikata kurakurai da dama,wanda su ka jefani halin da nake ciki a yanzu,ko ma na ce k'addara.
To k'addara mana! Duk wanda ya ce so ba k'addara bane,to bai tsinci kanshi a irin halin da so ya sakani ba
Kallo d'aya tak! Ya jefani a manyan matsaloli.
A daren juma'ar su Anti Halima suka kwashi kayan,su ka maida shi wurin Ummi,ni kam ko kallon tsanaki ma ban tsaya na yi musu ba.Bayan sallar isha'i Baba ya kirani,ya ke tambaya ta wasu irin kayan d'aki nake so?
Sai na ji duk jikina ya yi sanyi,tunda na fara gane da gaske dai auren zan yi,kuma da Habib,na kwantar da murya na ce"Baba ba ni da wani zab'i,duk wanda aka samu na gode".
Baba ya ce"to ma sha Allah! Zinatu kin ga dai ni ba me k'arfi bane,sai dai rufin asiri,don haka zan yi miki iya k'arfina.Kuma don Allah ki k'ara nutsuwa,ba na son na sake jin wani ya kawo min k'ararki,ki nutsu mu samu mu rabu lafiya,kema auren shi ne kwanciyar hankalinki".
Na amsa da to, sannan na tashi na koma d'akina,kwanciya na yi rigingine haka kawai na ji saukar hawayen da ban san ko na meye ba.Na d'akko wayata cikin rashin sanin abun yi na kira layin Salim,har ta katse bai d'aga ba, sai na yi masa sak'on fatan alkhairi,nan ma dai bai dawo min da shi ba.
Washegari da misalin k'arfe goma na shirya tsaf,cikin dogon hijjabina har k'asa,na fita na tari adaidaita sahu,ban tsaya ko'ina ba sai ALBARKA
Ban samu matsalar shiga wurin ba,don na sanar musu Salim ya san da zuwa na,sai dai ina zuwa k'ofar office d'in na tarar da wata matashiya,kuma ta ce min sai ya bada izini ake shiga,don haka na dakata ta yi min iso
Na jinjina kai,ina fad'a mata sunana Zinatu,ba ta jima ba ta fito ta ce min na shiga
Gabana ya yi fad'uwar da ban tantace ko ta meye ba,na san dai ba ta rasa nasaba da rashin k'wakkwaran dalilina na zuwa wurin,da kuma yanda Salim zai yi idan na fad'a masa k'arya nake ba kaya zan siya ba,sai kuma uwa uba yanda zai karb'i maganar da zan yi masa yanzun
Da sallama na shiga a nutse, kai sai ka rantse ba ni bace,na tadda shi zaune a kujera ya na danna waya,da jarkar coca cola a kan teburin,sai d'an k'aramin kofi
Ya yi masifar kyau,yau sanye yake da manyan kaya,wani yadi ne dak bulu da bak'ar hula a kanshi,ga bak'in agogo sanye a hannunsa
Idona ya sauka a bayan wayarsa,me d'auki da hoton wata budurwa me kyau,ban san ko wace ba,amma na fi kyautata zaton ita ce Baby
"Wa alaikissalam" Ya amsa da muryarsa me dad'i,ya na min nuni da kujerar da take fuskantarsa alamar na zauna.
"Na gode" Na fad'a bayan na zauna d'in.
Shiru na d'an lokaci kafin na ce"Zinatu ce".
"Na gane" Ya fad'a ya na ajiye wayar.
Na d'an yi jim,na sauke ajiyar zuciya,ina jin wani sanyi da ya ke shiga kowace kafa ta jikina,kar fa ku ce ko sanyin Ac ne,a'a,wani irin sanyi ne da rasa yanda zan yi muku bayanin sa,ni dai na san k'alau na shigo wurin da sai na ce zazzab'i nake yi
Na d'an yi gyaran murya,wai ko za ta k'ara dad'in sauraro na fara magana"da farko dai zan fara baka hak'uri na rashin zuwa na jiya..."
Ya katseni"ai shiyasa nake son ki hanzarta,don yau ba ni da appointment dake"
"Hakane,na gode da bani dama" Na fad'a ina muskutawa,sai gyara zama nake kamar me nak'uda.
"To a gaskiya ba zan b'oye maka ba Salim...ba da gaske na ke ba, da na ce maka zan yi siyayya a kamfanin ku..."
Ya katseni"e na sani,kuma ba na neman dalilin k'aryarki,dalilin zuwan ki yanzu na ke buk'ata".
Na kalle shi,na ga ni ya ke kallo,irin kallon nan na ido cikin ido,nan da nan ya yi min kwarjini,sai na ji duk na muzanta,na ji dama ban zo ba ma,To wai ma me ya ke damuna ne? Meye hakan na ke ta yi? Me zai sa na zubar da ajina na zo har wurin shi? To ko dai son shi na ke yi? Kai ba haka ake so ba,so ba rana d'aya ake fara shi ba,kamar yanda Habib ya fad'a min,na dai fi yarda Salim burgeni kawai ya ke yi...
K'was! K'was! Ya buga teburin gaban shi,da wani had'addan zobe dake yatsan shi na tsakiya.Ban gama dawowa cikin nutsuwata ba na ji ya ce"kar ki min k'arya,don ita ce abin da na fi tsana,kuma idan ki ka min k'arya ba zan sake sauraron kalma d'aya daga bakinki ba.Meye dalilinki na bibiyata?"
Dum! Dum! In ji k'irjina,na sanyaya murya kamar marainiya na ce"wallahi Salim haka kawai na ji ka burgeni,idan ba damuwa ina son k'ulla alak'a da kai,ko da ta abota ce,ka zama abokina don Allah"
K'urr! Ya tsaya ya na kallona,sai kuma ya dafe kanshi da duka hannunsa biyu,ya lumshe ido,ina ta fargabar yanda zai d'auki zance na,har tsawon mintuna ya na haka sannan ya d'ago ya zube idonsa akina.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 6
"Ban amince ba". Ya fad'a a sanyaye
Na ji zuciyata ta motsa,na kalle shi,sai ya lumshe ido ya na nuna min k'ofar fita daga office d'in
"Don Allah Salim". Na fad'a a kasalance,idona su ka ciko da k'walla
"Tashi ki fita" Ya fad'a,ya na janyo lokar dake jikin teburin.Ban fita ba,sai ma kallon sa da na tsaya yi,ina son ganin abin da zai d'akko
Wata kwalba ya fito da ita,ta maganin tari ya janyo robar coca cola ya bud'e ya juye maganin a ciki duka,ya jijjiga ya kafa kai ya na kwankwad'a ya na kallona
Ko wani bai fahimtar da ni ba,na san hakan ya na nufin shaye-shaye kenan,cikin inda-inda na ce"Salim! Me hakan ya ke nufi? Me kake sha?"
Ya ajiye robar ya ce"yanayin ku d'aya! Kalaman ku ma iri d'aya ne,ko ita ta turoki ki gwadani?"
Gabana ya fad'i,to ba dai giya ya sha ba,bare na ce har ya fita daga hayyacinsa,ina cikin nazarin na ga ya d'auki waya ya yi kira"zo office d'ina". Abin da ya fad'a kenan
Ba a jima ba kuwa sai ga wani ma'aikaci ya shigo,tun kafin ya k'araso ya yi masa nuni da ni ya na fad'in"fita da ita,kuma ka fad'awa Godiya kar a sake bari ta shigo!"
Na bugawa ma'aikacin wata kafirar harara,ganin ya na shirin tab'ani,sannan na tashi a sanyaye na fita,ina waiwayen Salim idona taf k'walla.
Ina fitowa daga office d'in na ji na kasa rik'e hawayen,ina jinsu su na ta zuba amma ban damu da gogewa ba,ko kuma na tsaida su
Sai dai dab da zan fita daga wurin na gamu da Kawu Ummaru zai shigo,gabana ya yi mummunar fad'uwa,na yi wani wawan ribas na juya don komawa ciki,ashe na makara don kuwa ko taku uku ban yi ba na ji ya kira sunana da alamaun mamaki
Duk k'ok'arin da na yi na ganin na tsaida hawayena kafin na juyo abu ya ci tura,har sai da ya sake kiran sunana sannan na juyo ina share hawaye
"Zinatu me kika zo yi a nan?" Ya tambayeni har yanzu da mamaki a fuskarsa.
Dabara ta zo min na ce "Aiki na zo nema".
Sai ya bud'e baki da mamaki ya ce" aiki kuma? To an d'auke ki?"
Na girgiza kai alamar a'a
Ya ce"banda shirme ki taho neman aiki ba tare da shawara ba? Kuma ba jiya na ji ana zancen kayan lefenki ba? Ko kuma shi Habib d'in ne ya ce ki nemi aikin yi kafin auren?"
Na cigaba da hawayena,ba tare da na ba shi amsa ba. Sai ya wuce ya barni tsaye ina goge hawayen
To bayan na fita daga wurin a maimakon na yi gida,sai na yi 7:30 restaurant,ina ta rarraba ido bayan na shiga wurin,sai na je wurin wani da nake kyautata zaton ma'aikaci ne,tunda ga shi da uniform me d'auke da sunan wurin,na yi masa sallama ya amsa
Sannan na ce"don Allah zan iya ganin manager?"
Ya ce"e ba matsala,ga office d'in shi can".
Na shiga k'ofar da ya nuna min da sallama,aka amsa ana yi min izinin shigowa,wani matashi na gani kwance akan doguwar kujerar dake office d'in
"Hajiya barka da zuwa" Ya fad'a ya na tashi zaune
"Barka" Na ce,ina zama a wata kujerar
Na ce"alfarma na zo nema"
Ya ce"to,ta mene?"
Na d'an cije baki kafin na ce"don Allah aiki nake nema a wurin nan".
Ya ce"tabb! Aikuwa baiwar Allah, ba mu jima da k'ara ma'aikata ba,yanzu dai sun wadata gaskiya ba ma buk'atar k'ari".
Na yi saurin fad'in"don Allah ka taimakeni,ko da shara ce ko wanke-wanke"
Ya ce"zancen kike so"
Na tausasa murya na ce"don Allah ko kyauta ne ni zan dinga aiki,idan ya so duk wata ka dinga rik'e albashina,na bar maka...".
Ban k'arasa ba ya tareni"ok, ba sai ta kai nan ba,zan iya baki aiki,amma fa ba wanda kike zato bane idan za ki iya duk wata za ki samu kud'i fiye da zaton ki,amma nima za ki na bani wani abun k'arshen wata"
Na yi saurin fad'in"e na yarda, in dai a wurin nan ne".
Ya ce"a anan ne ba matsala.Wurin namu b'angare biyu ne,akwai wurin da masu kud'i suka fi zama idan sun zo cin abinci,to za mu saka ki a cikin wa'inda za ki na kai musu abinci,wasu kuma sukan buk'aci wata ta zauna ta tayasu fira,ke wani ma idan firar ta yi dad'i har ya buk'aci ki raka shi wani wurin,to ta nan ne ake samun kud'i daga hannunsu,ga kuma albashinki me tsoka,dad'in dad'awa ma ku da kayan gida za kuna zuwa,amma fa sai kin kula da kwalliya mai d'aukar hankali".
Na jinjina kai bayan na gama sauraron sa,na ce"babu matsala zan yi".
Ya ce"yawwa! Amma dutyn dare za ki na yi,saboda na ga kina da kyau sosai,Allah yasa dai za ki iya aikin".
Na yi murmushi na ce"kar ka damu zan iya.Yaushe zan fara zuwa?"
"Tun daga yau" Ya bani amsa,sannan ya tambayi cikakken sunana,na fad'a masa,ya tashi ya rubuta a wani littafi,mu ka yi musayar lambar waya sannan ya ce zan iya tafiya.
Na yi masa godiya,na fito daga wurin ina jin wani farinciki sosai.
Yanzun ma ba gida na yi ba,kasuwar sabongari na wuce na yi siyayyar kayan kwalliya kala-kala da turaruka masu k'amshi,domin inganta aikina.Gidan Ummi na wuce kai tsaye,bayan na gaisheta na tashi na yi alwala na yi sallar azhar,don lokacin k'arfe d'aya saura kwata, ta zubo min abinci na ci kad'an na tashi zan tafi,ta ce min"kin ga kayan naki kuwa?"
Na gyad'a mata kai,alamar e,ta na murmushi ta ce"Habib ya yi k'ok'ari sosai,Allah dai ya baku zaman lafiya".
Ban amsa ba na fice ina yi mata sai gobe.
To daga nan kuma gidansu Kamisu na wuce,wani a k'asan layinmu da mu ke mutunci da shi,na yi sa'a kuwa ya na nan,zaune akan benci na tadda shi a k'ofar gida,na zauna a bencin nesa da shi,ina tambayarsa ya garin
Ya ce"normal wallahi,kin yi wuyar gani, sai jiya nake jin ashe auren ya kusa?"
Na yi murmushi na ce"haka aka ce".
Ya ce"a,ban gane haka aka ce ba?"
Na yi y'ar dariya na ce"share kawai,kamar na ji ance k'anwarka ta na yin lalle ko?"
Ya tab'e baki ya ce"wai Nana? Ko yanzu ma shi na fito na barta ta na yi"
Na ce"yawwa! So nake don Allah, d'an kad'an za ta yi min"
Ya ce"ok,mu shiga to"
"A'a,ta fito dai ta min,sauri nake".
Na fad'a ina d'akko wayata da ta fara ringing. Habib ne me kiran,na d'aga,bayan mun gaisa ya ke ce min yau zai shigo da daddare,na ce masa a'a sai dai da yamma,don ina da abin yi da daddare,ya amince muka yi sallama
Na kalli Nana dake tsaye na ce" yawwa Nana,kinga ba me yawa bane,da na iya rik'e lallen ma da kaina zan yi, harafin (S) kawai za ki zana min babba a nan"
Na yi maganar ina nuna mata bayan hannuna.Nana ta zauna a benci nima na zauna,ta zana min kamar yanda na buk'ata,sannan ta cike tsakiya da jan rani,hannun ya yi kyau sosai kuwa,na mik'a mata d'ayan na ce shi kuma ta zana min J.S,nan ma ta zana min,sannan ta saka min a y'an yatsuna ,na yi mata godiya na ce ta zuge jakata ta d'auki d'ari biyar,ta ce a'a na bar shi,ta shige gida.
Kamisu ya kalli lallen ya ce"amma Zinatu na ga dai sunanki daga Z ya fara".
Na yi murmushi ina kallon hannun da na shanya shi s titi na ce"hmm! Share kawai Kamisu,wai ka ji y'an drugs sun k'wamushe Salisu ko?". Daga haka mu ka shiga wata firar.
Da yamma Habib ya zo kamar yanda na ba shi lokaci,ya kwashi surutun sa ya k'ara gaba,don ni kam duk rabin hankalina ya na ga yanda aikina zai kasance,ya ce dai da daddare amma ban san ko k'arfe nawa ake tashi ba,yanzu idan za a kai dare sosai wace k'aryar zan yi wa Baba akan fita ta kullum? Wannan tunanin ya d'an sanyaya jikina,amma fa bai canza min k'udirina ba.
Ana fara kiran sallar isha'i,ina kammala shirina,doguwar riga na saka dama duk ta fi burgeni cikin kayana,na zauna na rangwad'a kwalliya,na nad'e kaina da mayafi kalar takalmin da zan saka,na baza turare bayan humrar da na yi wankanta,lokaci-lokaci nake kallon k'unshin hannuna na yi murmushi, kamar dai an bani tabbacin yau zan had'u da shi,na saka takalmina me tudu,na rayata jaka y'ar k'arama na fito
Mama Saude da ke kwashe tuwo ta bud'e baki ta na kallona,na tsuke fuska ina shirin wuceta na ji ta ce"Allah me iko! Zinatu wannan kwalliyar fa? To ko dai dawo da bikin yau aka yi bani da labari?"
"Wurin dinner k'awata zan je" Na fad'a don kar ta had'ani da Baba,na fice daga gidan cikin sauri-sauri.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 7
Ina zuwa manager ya had'ani da wani,ya kaini b'angaren da aikina ya ke,ya na ta yaba kyauna,ni dai binsa kawai nake ina k'arewa wurin kallo,wani holl ya kaini,na ga y'an mata wasu na girmesu wasu sun girmeni,ga kuma sa'annina duk sun ci kwalliya su na zaune,wasu na fira,wasu na danna waya. Wata ya nunawa ni ya ce ta koya min yanda zan gudanar da aiki.Ta matso kusa da ni ta na murmushi ta fad'a min komai,sannan ta d'ora da fad'in"akwai Oga Salim,shi ne me wurin,shi ma ya na zuwa wataran,kuma be cika cin abinci ba idan ya zo,shi ya fi yin shaye-shayen shi,da yake d'an shaye-shaye ne".
Sai na ji kalmar shaye-shayen har cikin raina,na ji ban ji dad'i ba a ganina Salim ya wuce ana danganta shi da wannan kalmar mara dad'in ji,to amma ya zan yi? Tun da halinsa ne dole a fad'a
"Allah ya shirya shi dai" Na fad'a ina sauke numfashi
Ta ce"hmm! Ai ni idan ya zo har na tsani a turani kula da shi wallahi"
"Kula da shi,sai kace wani jinjiri?" Na fad'a a zuciyata
A fili kuma na ce"to ya ake kula da shi?"
Ta ce"ai idan mutum ya shiga ba ya barin d'akin har ya tafi,saboda kai za ka rik'e masa d'an farantin da zai dinga karkad'e tokar sigarin da zai sha,kuma kai za ka had'a masa lemo da maganin tarin nan,idan zai ci abinci sai ya fad'i wanda yake so,ka kawo masa,ga shi ba ya son kallo,sai dai ka duk'ar da kai,ga warin taba shiyasa duk muka tsani a tura mu idan ya zo"
Na jinjina kai,ina mamakin wannan mulki irin na Salim,sai dai sosai hakan ya min dad'i,ko banza zan jima ina ganin shi,kuma zan samu hanyar shigar da kaina cikin sauk'i,na yi farinciki da ba sa son zuwa,ni kam ba warin sigari ba ko na giya ne zan jure.
Muna nan zaune aka yi kiran mutum