Showing 18001 words to 21000 words out of 98220 words

Chapter 7 - YAR SARKI CE HAISA NOVEL

14 Oct 2025

79

zai mulki masarauta cikin amana da zaman lafiya kaman yacce Papa na yake yi. Amma in abinda nayi ya ɓata maka rai Allah ya huci xuciyan ka Papa, Allah baka haquri insha Allahu bazan sake wannan kuskure ba."
Ajiyan zuciya mai martaba ya sauqe! "Naji dalilan ki amma duk da haka baki kyauta ba kuma bakiyi dai dai ba, sai dai ba komai Ebnateeyh Allah maki albarka ya zaɓa maki miji nagari."
Ta amsa da Ameen, cikin ranta tana hamdala, dan tasan halin mahaifin nata sarai......




ƳAR SARKI CE


Daga alqalamin✍️


𝙐𝙬𝙖𝙧 𝘽𝙖𝙩𝙤𝙤𝙧𝙡 🔥




*******
* kai daga fara chan charas chas chas sai kace hasti duka matan dake wajan sun taso abun su chasssss..........
Muje zuwa my people
Ku nishaɗantu, ku faɗakantu, ku wa'azantu, sannan ku dara. daga alqalamin uwar batoorl takuuuuuuu ako da yaushe
Fatan alheri agare ku masoya alqalamin uwar batoorl a ko ina kuke a faɗin duniyar nan....






𝘿𝙤𝙢𝙞𝙣 𝙩𝙖𝙡𝙡𝙖𝙩𝙖 𝙝𝙖𝙟𝙖𝙧𝙠𝙪, 𝙠𝙪 𝙩𝙪𝙣𝙩𝙪𝙗𝙚𝙣𝙞 𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙡𝙖𝙮𝙪𝙠𝙖:-
08146292652
𝘾𝙝𝙖𝙩 𝙤𝙣𝙡𝙮.
09161720046
𝙔𝙤𝙪 𝙘𝙖𝙣 𝙘𝙖𝙡𝙡 𝙙𝙞𝙨 𝙤𝙣𝙚, 𝙭𝙖𝙢𝙪 𝙢𝙖𝙠𝙪 𝙩𝙖𝙡𝙡𝙖𝙣𝙠𝙪 𝙖 𝙧𝙖𝙝𝙪𝙨𝙖 𝙢𝙖𝙞 𝙨𝙖𝙪𝙦𝙞,


# 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩
# 𝙇𝙞𝙠𝙚 &
# 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚






𝙐𝙬𝙖𝙧 𝙗𝙖𝙩𝙤𝙤𝙧𝙡 🔥


💦💦💦💦💦💦💦💦
𝙔𝘼𝙍 𝙎𝘼𝙍𝙆𝙄 𝘾𝙀𝙀
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

𝙎𝙩𝙤𝙧𝙮 𝘼𝙣𝙙 𝙒𝙧𝙞𝙩𝙩𝙚𝙣

𝘽𝙮


𝙃𝙖𝙧𝙞𝙧𝙖 𝙨𝙖𝙡𝙞𝙝𝙪 𝙞𝙨𝙖


(𝙐𝙬𝙖𝙧 batoorl✍🔥)

اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله saw🖤🤍



𝙒𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙡𝙖𝙗𝙖𝙧𝙞 𝙦𝙞𝙧𝙦𝙞𝙧𝙖𝙧𝙧𝙚 𝙣𝙚, 𝙬𝙖𝙣𝙙𝙖 𝙖𝙬𝙖𝙣𝙞 𝙗𝙖𝙣𝙜𝙖𝙧𝙚 𝙣𝙖𝙨𝙖 𝙖𝙠𝙬𝙖𝙞 𝙖𝙗𝙪𝙣 𝙙𝙖𝙧𝙞𝙮𝙖 𝙨𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙞 𝙛𝙪𝙨𝙠𝙖𝙣 𝙖𝙠𝙬𝙖𝙞 𝙖𝙗𝙪𝙣 𝙩𝙖𝙪𝙨𝙖𝙮𝙞, 𝙨𝙖𝙞 𝙙𝙖𝙞 𝙗𝙖𝙗𝙗𝙖𝙣 𝙖𝙗𝙪 𝙢𝙖𝙛𝙞 𝙧𝙞𝙣𝙟𝙖𝙮𝙚 𝙨𝙝𝙞𝙣𝙚 𝙛𝙖𝙙𝙖𝙠𝙖𝙧𝙬𝙖𝙣 𝙙𝙖𝙠𝙚 𝙦𝙪𝙣𝙨𝙝𝙚 𝙖 𝙘𝙞𝙠𝙞 𝙙𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 𝙙𝙖𝙧𝙖𝙨𝙞 𝙣𝙖 𝙧𝙖𝙮𝙪𝙬𝙖.
𝙄𝙣𝙖 𝙛𝙖𝙩𝙖𝙣 𝙯𝙖𝙢𝙪 𝙦𝙖𝙧𝙪 𝙙𝙖 𝙙𝙖𝙧𝙪𝙨𝙖𝙣 𝙙𝙖𝙠𝙚 𝙦𝙪𝙣𝙨𝙝𝙚 𝙘𝙞𝙠𝙞𝙣𝙨𝙖. 𝙎𝙖nn𝙖𝙣 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖 𝙗𝙖𝙢𝙪 𝙙𝙖𝙢𝙖𝙣 𝙖𝙢𝙛𝙖𝙣𝙪𝙬𝙖 𝙙𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 𝙖𝙞𝙠𝙞 𝙙𝙖 𝙖𝙗𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙯𝙖𝙢𝙪 𝙠𝙤𝙮𝙖 𝙖𝙘𝙞𝙠𝙞.
𝘼𝙗𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙮𝙖𝙠𝙚 𝙗𝙖 𝙙𝙖𝙞 𝙙𝙖𝙞 𝙗𝙖 𝘼𝙡𝙡𝙖𝙝 𝙮𝙖𝙛𝙚𝙢𝙪 𝙖 𝙠𝙖𝙣𝙨𝙖.

𝙎𝙖𝙙𝙖𝙪𝙠𝙖𝙧 𝙬𝙖 𝙜𝙖𝙧𝙚𝙠𝙪 𝙢𝙖𝙨𝙤𝙮𝙖 𝙩𝙖𝙧𝙚 𝙙𝙖 𝙙𝙖𝙪𝙠𝙖𝙘𝙞𝙣 𝙢𝙚𝙢𝙗𝙚𝙧𝙨 𝙣𝙖 𝙇𝘼𝙁𝘼𝙕𝙄 𝙜𝙞𝙙𝙖𝙣 𝙠𝙖𝙧𝙖𝙢𝙘𝙞.


***
yau take rana ta qarshe ga masu gasa a masarauta!
Yau take sojan umma zai dawo!
Yau take Ameera uwar little zata taho Kaduna garin gwamna itama tabar kakus da sinkin sikitin tijaranta!


Muje zuwa cikin littafin namu mesuna 𝙔𝘼𝙍 𝙎𝘼𝙍𝙆𝙄 𝘾𝙀𝙀
Dan jin ya abubuwan zasu kasance, wa zai lashe gasa?
Waye soja?
Sannan Ameera na komawa?
Muje labari kai tsaye masu karatu!!
***
_____________________________________________________________




🅿️ 25&26




💋💋 امى بتولة💋














^^Zaune suke suna karyawa. Ummace tace "Abban jarumin Umma wai yau ba zuwa kasuwa ne kam?" Wanne zuwa kasuwa kuma Maryama ai sai an qarqare wannan gasa a ido na Insha Allahu. Murmusawa Umma tayi! Tace "Ni ko naji haushi da Jarumin Umma bayanan, dan naso ayi gasan nan a idon sa". Ai ko bayanan dole ma na basa labari Maryama, dan nasan ɗan ki ko yana nan ba lallai ya yarda yaje wajan taron can ba, mutum sai kace ɗan aljanu bakason shiga jama'a bakason magana da mutane. Umma ce ta haɗa fuska tace "nifa Abban jarumin Umma ba nason cin fuska ɗan nawa ne ɗan aljanu? Tom ashe ni da kai aljanu ne. Dariya Abba yasa! Allah baki haquri Sarauniya Maryama ta Abban jarumi daga ke ba qari! Ɗan ki ɗan mutane ne ba aljanu ba kyakkyawan yaro mai kama da Umman sa. Ba shiri Umma ta murmusa!! "Yauwa ko kai fa mijin Maryama daso". Yanzu dai tunda ɗan ki baya nan tashi na tayaki ayyuka mu samu muje wajan taron nan da wuri dan so nake in ga qaqa zata kaya, ya zasu qare. Umma ce ta miqe tana cewa "Tom Abban ɗana, Nima dai inaso naga mace mai kamar mazan nan ya zata qare gasan, dan da ace yarinyar nan namiji ne ba mace ba, wannan Masarauta ba zata kuka ba dan anyi rashin mai martaba sarki. Amma ita ɗin ma muna mata addu'an samun miji na gari alfarman Annabi SAW!!




🄼🄰🅂🄰🅁🄰🅄🅃🄰🄽 🅀🅄🄱🄰🄸🅂🄷


** inji malam ba haushe yace "𝙙𝙪𝙠 𝙖𝙗𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙖𝙠𝙖 𝙨𝙖𝙬𝙖 𝙧𝙖𝙣𝙖 𝙩𝙤 𝙩𝙖𝙗𝙗𝙖𝙨 𝙯𝙖𝙞𝙯𝙤, 𝙨𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙙𝙪𝙠 𝙖𝙗𝙪𝙣𝙙𝙖 𝙮𝙖𝙮𝙞 𝙛𝙖𝙧𝙠𝙤 𝙩𝙖𝙗𝙗𝙖𝙨 𝙯𝙖𝙞 𝙮𝙞 𝙦𝙖𝙧𝙨𝙝𝙚". Kuma 𝙌𝙖𝙧𝙨𝙝𝙚𝙣 𝘼𝙡𝙚𝙬𝙖 𝙌𝙖𝙨𝙖!!

Yau take Ranan fafatawan nasu na qarshe a gasan. Ranar da tayi dai-dai da ranar Asabar(Saturday), Rana ta uku kuma ranar qarshe a gasan.
As usual(kaman ko wacce rana) wajan da yake ake yin gasan, ya cika sosai-sosai fun tunani! Kasancewan yau ne rana ta qarshe kowa nason ganin ya abun zai qare, wa zai yi nasara? Za'a samu mai faɗar da Gimbiyar kuwa? Daga waɗan da aka fara dasu har waɗan da ba suga farkon ba yau sun hallara taro yayi taro jama'a ba masa stinke, kaman ba kowa a cikin Masarautan bayan jama'ar wannan fili dan cikan wajan.(mai karatu kawai ka kwatanta hakan iya ganinka dan taro yayi taro)..
Umma da Abba ma har sun hallara suna maqale a wajan( shi kuwa gogannaku baima san mai ke tafiya a garin ba dan tsabar miskilancinsa da rashin shiga hayaniya ko jama'a gashi kuma yana daji).
Sarki na munbari wajan zaman sa da fadawan sa kaman koda yaushe. ƴaƴan Sarakuna dukkan su kowa na wajan da yake na zaman sa shi da muqarraban sa, da waɗanda sukayi da waɗanda ba suyi ba, dukansu sha biyu 12
Yarima Ahmad
Yarima Abham
Yarima Khalil
Yarima Suhail
Yarima Fu'ad
Yarima Ammar
Yarima Jawad
Yarima Waheed
Yarima Jaay(jabir)
Yarima Khaleed
Yarima Mu'azz
Yarima Abdoul. Duk ko wannen su na mazaunin sa.
Gefe guda kuwa wanda yake an qawata shi da ado gwanin burgewa da sha'awa! Gimbiya ce a zaune a wani haɗaɗɗen kujera da yaci ado, ado irin na sarauta, sanye take da kaya irin na mayaqa da ɗamaran ta hallau da rolling nata da ya rufe mata fuska, kayan nata daga sama har qasa Black ne,wanda ya amshi fatar ta kasancewar ta fara. Jakadiya na gefen ta a durqushe da kuma sauran kuyangu wanɗanda daga cikin su na hango, Laure da Hinde, sannan dogarai da suke staye gefe suna mata kirari.......
Mutumin da ke riqe da Miche(abun magana) ne ya tashi yai magana, kaman ko da yaushe, sannan ya gaida manyan-manyan baqi da kuma sauran jama'a. Magana yaci gaba da yi kamar haka:- "Kaman yacce muka sani duka, yau shine rana ta qarshe a wannan gasa namu wanda aka ɗauki stawon kwanaki uku anayi, kuma duk wanda ya cinye bi ma'ana ya samu nasarar buɗe fuskan Gimbiya tom shine ya lashe gasa. Sannan insha Allahu shine mijin Gimbiyar mu kuma Sarkin mu na gobe, kaman yacce kuma muka sani duka ƴaƴan Sarakuna sha biyu 12 ne suke gasan, sannan a yanzu uku ne kawai suka rage waɗanda ba'a fafata da su ba, a yanzu kuma za'a soma gudanar da gasan wanda muke sa ran yau za'a gama da yardan Allah, ga wanda ke da abun cewa tom fili domin sa, in Kuma babu tom zamu iya cewa, Allah bawa mai rabo Sa'a. Bissalam". Wasiqa aka miqawa wanda ke magana da Miche ɗin, kawar da Miche en yayi a bakin sa yace "wasiqan Menene?" Dogarin da ya kawo yace "saqo ne daga sauran yaran sarakunan da suka rage" to shikkenan ba mu isar da saqon wasiqan nasu. Buɗewa yayi ya karanta, sai da wasiqan ya isa wajan mai martaba yace ba komi sannan aka dawowa da mutumin wasiqan. Magana ya fara yi kamar haka:-
Assalamualaiki ya ke Gimbiyar wannan Masarauta tamu mai albarka, ƴaƴan Sarakunan da suka rage suna neman wata alfarma, acewan su tunda gasan da mutum ɗaɗɗaya akeyi, tom alfarman da suke nema shine a yanzu su ukun da suka rage, Yarima Khaleed، Yarima Mu'azz, da Yarima abdoul. Suna son su gudanar da gasan lokaci ɗaya ma'ana su ukun duka za'a fafata dasu a take, sannan suna fatan mai martaba Sarki da kuma Gimbiya zasuyi na'am da wannan alfarman da suke nema.
Jama'a ne suka fara surutu ko ta ina suna cece kuce kowa da abinda yake faɗa, "wasu na faɗin hakan baiyi ba, wasu na faɗin hakan ba dai-dai ba, wasu na faɗin haka ne ya kamata," kowa dai da abinda yake faɗa a nasa ra'ayin. Magana mai shelan yayi(wanda yake magana dama) "kowa yayi shiru jama'a, mai martaba Sarki ya amince da wannan buqata naku Yarima Mu'azz, Yarima abdoul, Yarima khaleed. Haka zalika a ɓangaren Gimbiya tayi na'am da buqatan ku, fatan nasara" ya faɗa yana neman waje ya zauna.
Sarki da yaji abunda mai shelan yace, lumshe ido kawai yayi! yana addu'an Allah ya sa wani a cikinsu su ukun yayi nasara, shiyasa ma yayi na'am da wannan buqatan nasu.
Ita kuwa uwar gayyar, ko a jikinta sai ma daɗi da taji komi zai qare yau Insha Allahu, dan tafisu jin daɗin amincewan Sarki kuma tafisu jin daɗin shawaran da suka yake, ko ba komai itama zata huta da shirmen nan. Idanuwan ta ta lumshe faɗi take a ranta "Ni MEHWISH ba dai mutum ya same ni dan wai shi jarumi ba sai dai dan ya cancanta ko in yamun, amma duk da haka ina burin auren jarumin jarumai, Allah ka tabbatar mun da alkhaeryh,amma a cikin waɗan nan bana jin akwai mijin aure na ni Ƴar Sarki Qaseem."
Haka aka shiga filin dagan domin fafata gasan, su ukun ne kaman yacce suka buqata ita kuma ita ɗaya, mai busan da ke nufi zasu iya farawa ne ya busa.
Sun fara faɗan abun gwanin burgewa ga daɗin kallo, dan kuwa faɗa suke bil haqqi, su uku sun dage ɗayan su sai yaci nasara. Ranta wasai take yin wannan faɗa ba ko alaman ta damu da kasancewan su har su uku ita ɗaya. Wani ne acikin su ukun ya nufi abun fuskan nata da biyan ya janye ganin kaman hankalinta yafi karkata kan Yarima Khaleed da yake jarumine na gaske kuma mayaqi yasan salo-salon faɗa da dama. Ai kuwa karaf ta kaiwa takobin nasa sara dan tana ankare da su dukan su ji kakeeee qasss qaqassssssssssssss har sai da takobin nasa ya ɗan lanqwashe, Jin saran da tai wa takobin nasa yayi kaman a hanunsa ta kai saran, dan sanda yaji kaman qashin hanun sa ya goce saboda qarfin saran. A haka suka ci gaba da fafata wa, ko wannen su na qoqarin samu ya kai hanun sa fuskan ta, koda da takobi ne. Yarima abdoul wanda aka kaiwa takobin sa Sara shine ta fara kaiwa qasa! Yarage Yarima Mu'azz da Yarima khaleed, ci gaba da fafatawan suka yi ba ji ba gani. A haka takuma kai yarima Mu'azz qasa! Ya rage filin su biyu Gimbiya MEHWISH da Yarima KHALEED. Fili domin su.......




🄳🄰🄹🄸
Tafiya yake akan dokin sa shi kaɗai, ba tare da jin storon girman jejin ko wani abu ba, tafiya dokin nasa ma yake a hankali, kalle-kalle yake yi, wanda da alama wani bishiyan yake nema, karatun Qur'ani yake yi qasa qasa yana tafiya akan dokin nasa, dai-dai wani babban bishiya da rasa gane na menene ya tsaya da dokin nasa, sauqa yayi ya shafa kan dokin yana masa magana "besty ka jirani ko ba na sari bishiyan nan nazo mu koma gida yau muga Umma" karkaɗa bindi dokin yayi yana miqar da kan sa, murmushi Amjad yayi yace "that's my besty dama nasan ka da jin magana, mintuna kaɗan ina dawowa." Qara sawa wajan bishiyan yayi ya sari jijiyan ya kuma sassaka bayan sannan ya ɗiba ganyen. Juyawa yayi ya koma inda yabar dokin nasa, a inda ya barsa nan ya same sa da murmushi ya shafa kansa ya haye saman sa yace "besty mu tafi ko" kaɗa bindi dokin yayi ya juya dan su koma gida. Juyawan da sukayi ido biyu yayi da......




Kan fafatawa suke tsakanin Yarima khaleed da Gimbiya Mehwish, sosai yarima Khaleed ya nuna Jarumta dan kuwa tunda aka fara gasan ba wanda ya nuna Jarumtan da ya nuna, ba tare da sun gaji ba dukansu. Ɗaga tokobin sa yayi da niyan kai mata sara kaucewan da tayi dan kare kanta, yayi amfani da daman ya kai hanunsa kan abinda tai rolling fuskan ta da niyan ya janye. Duk abinda yake Gimbiyar a ankare take, tana tare saran ta kuma yin qasa dan kaucewa hanun nasa domin hakan ne kawai kariyan da zata iya yi. Kaucewan da tayi ya sanya shi yin qasa ya faɗi domin da dukkan qarfinsa ya kai wannan harin, faɗuwan da ya janyo masa rashin nasaraa!!
haka duka ukun ta kaisu qasa. har Yarima khaleed!
Ba abinda kake ji yake tashi a wajan se ihun da jama'a suke yi suna qiran sunan Gimbiyar "𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼𝘼" "𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼" "𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼𝘼" 𝙎𝘼𝙄 𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼𝘼𝘼 𝙈𝙀𝙃𝙒𝙄𝙎𝙃".
Iya sunanta kawai ke tashi bakin ɗauka cin jama'ar wannan wajan.
Fuskan ta ba abinda yake fidda wa sai walwalin murmushin ta!! Wanda inka tsaya kallon qwayan idanuwan ta ko ta kalle ka dasu tabbas zaka kusa sumewa! Ba tare da ta tsaya sauraron kowa ba ta wuce, dan mutumi mai magana ya tashi zai yi magana. Wucewa tayi dan nufan wajan da dokin ta yake tayi dan tafiya gida kuyangun ta suka rufa mata baya suna mata kirari! Sannan mutumin da ke riqe da Miche ma kirari yake Mata!
𝙈𝘼𝙇𝘼𝙈 𝙆𝘼𝙂𝘼 𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼! 𝙆𝘼𝙇𝘼𝙉 𝙏𝘼 𝙆𝘼𝙇𝘼𝙉 𝘼𝙇𝙆𝙃𝘼𝙄𝙍𝙄! 𝙂𝘼𝘽𝘼 𝙎𝘼𝙇𝘼𝙈𝙐𝙉 𝘽𝘼𝙔𝘼 𝙎𝘼𝙇𝘼𝙈𝙐𝙉 𝙅𝘼𝙍𝙐𝙈𝘼𝙍 𝘿𝙐𝙉𝙄𝙔𝘼! 𝙒𝘼𝙇𝙇𝘼𝙃𝙄 𝙆𝙄𝙉𝙁𝙄 𝙌𝘼𝙍𝙁𝙄𝙉 𝘼𝙇𝙅𝘼𝙉𝙄 𝘽𝘼𝙍𝙀 𝙈𝙐𝙏𝙐𝙈! 𝘼𝙇𝙇𝘼𝙃 𝙅𝘼 𝙆𝙒𝘼𝙉𝘼 𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼, 𝙏𝘼𝙆𝘼𝙒𝘼𝙍 𝙆𝙄 𝙇𝘼𝙁𝙄𝙔𝘼 𝙁𝘼𝙍𝘼 𝙈𝘼𝙄 𝙁𝘼𝙍𝘼𝙍 𝘼𝙉𝙄𝙔𝘼.......
Kirari kuyangun nata ma ke mata! Daga qafa tayi da niyan hawa dokin nata amma sai dai me? Muryan mai martaba Sarki ne ya ziyarce ta, abinda taji ya faɗa ne yasanya ta fasa hawa dokin domin ji tayi kaman sauqan aradu a kunnuwan ta!!
Bayahn Sarki yasa an miqa masa abun magana cewa yayi. "𝙄𝙉𝘼 𝙈𝘼𝙄 𝙈𝙐𝙍𝙉𝘼𝙉 𝙎𝘼𝙉𝘼𝙍 𝘿𝘼 𝙆𝙊𝙒𝘼 𝘿𝘼 𝙆𝙊𝙒𝘼 𝘼𝙐𝙍𝙀𝙉 𝙂𝙄𝙈𝘽𝙄𝙔𝘼 𝙈𝙀𝙃𝙒𝙄𝙎𝙃 𝙉𝘼𝙉 𝘿𝘼 𝙒𝘼𝙏𝘼𝙉𝙉𝙄 𝘽𝙄𝙔𝘼𝙍 5 𝙈𝘼𝙎𝙐 𝙕𝙐𝙒𝘼 𝙄𝙉 𝘼𝙇𝙇𝘼𝙃 𝙔𝘼 𝙔𝘼𝙍𝘿𝘼". Sarki na gama magana ta ji kaman an daskarar da ita a wajan gaba ɗaya ta rasa gane mema yake faruwa, ba tare da tabi ta kan dokin da tayi niyan hawa ba ta kama hanyan komawa gida da qafa. Abun yayi mugun razanar da ita amma bata ce komi ba dan ba abinda zata iya faɗa. Ta dai wuce jikinta na rawa idonta har yanayin sa ya sauya!!
Su ma hadiman nata ba yanda suka iya da ita tunda ran uwar ɗakin nasu a ɓace yake ba mai bakin magana. Haka su ke bin ta a qafan su ma suna mata kirari. Yayin da ita kuma take ji a ranta kaman ta rufesu da duka amma bata da ko bakin magana dan abinda ke damun ta!! Haka suka miqa hanya da qafa.....


(Mastowa nayi na ce, afuwan uwar ɗaki na! hararan da tamun ne ya storita ni har ban san sanda na ganni a 𝙉𝙄𝙂𝙀𝙍𝙄𝘼 𝘽𝘼).




🄱🄰🅄🄲🄷🄸
^^ Kakus ce ke magana "Harara wai ba zaki qira driver ya zo ya fitar masu da kayan nasu bane kam?" Hayra ce tafito kitchen tana tura baki! Tana qunquni akan sunanta da kakar tasu ke ɓatawa. Ficewa tayi tai waje, Ameera tace "Amarya ba kin gaji da mu ba dole kiyi-kiyi ki koramu ai". Salati Amaryan ta sanya yanxu dan kawai sharri da balagaggen rashin kirki da ke damunki yaushe mukayi haka dake takwara? Yanxu duk kukan da nake a zuciyata baki gani ba so kike nata birgima ko? Tom dan ubanki Haruna bazan yi ba. Wuce ma ki fice ku barmun gida dama na gaji da kallonki, dariya Ameera da mijin ta suka sanya!! Driver ya shigo ya ɗau kayan suka bi shi suka fice a part en. Mama hansatu da mama Saratu suka samu wajan da hayra, ban kwana suka masu su na Ameera ta gaida masu Umman yara. "Insha Allahu zataji mama" faɗin Ameera suna shigewa motor da Daddyn Little en. Sallama suka wa Kakus en tasu, driver ya tada motor se Amarya ta fara hawaye!! Ayya takwara ku yafe Ni in na ɓata maku har dakai Angon Amarya, Allah stare maku hanya ya kaiku lafiya Alfarman Annabi SAW, dukan su wajan amsawa sukayi da "Sallallahu Alaihi Wasallam" driver ya ja motor suka yi hanyan airport dan wuce wa KD saboda yau soja zedawo.
Haka suka rabu kakus harda sharan kwallanta tana "takwarata yar albarka yar aljannah se an kuma leqo mu ko kuma wataqilan sai na mutu a kuma zuwa. murmushi su Hayra da su mama hansatu suka yi a haba dai Amarya zasu kuma dawowa Insha Allahu. Tom Allah ya sa ta faɗa ta juya tayi hanyan sashin ta, suma sukayi nasu. Harara qawar Amarya zo ki ɗau ko man goro a ɗaki Qur'ani har na fara kewan takwara ta Allah Sarki, fece hanci tayi ta share qwalla!!



Qarfe 2 na rana ta masu a cikin kaduna garin gomna. Sun sami Umma da Abba yau kam a gida duka kasancewan yau shalelen Abba zai dawo ko aiki bai je ba. Sosai Abba Yaji daɗin ganin ɗiyar tasa da kuma mijin ta suna lafiya lau. Sannu da hanya su Abba suka masu bayan mai aiki ta kawo masu ruwa suka sha. Sallah ko wannen su ya tashi ya je yayi kamun suka dawo su ka zauna, hira suke yi kai kace Daddyn Little da Abba ba surukai ba. Shi kuwa Little yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login