Showing 21001 words to 24000 words out of 44304 words

Chapter 8 - SULTHANA complete Hausa Novel

25 Jul 2025

1427

key dinshi yace
"Nidai na tafi"
Har bakin mota ya rako shi sukai Sallama ya nufo gida cikeda fargaban tambayoyin Mami..

A bangaren Sulthana fah..

*Mu tara page na gaba dan jin yanda Sulthana zata kwashe da y'an gidan nasu*

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 121 to 125*

Har bakin mota ya rakoshi sukai Sallama ya nufi gida cikeda fargaban tambayoyin Mami..

A bangaren Sulthana kuwa tafiya take sauri sauri duk inda ta bi k'allanta ake wasu kuma nunata. abin bah Karamin daure maka kai yayi bah, kanta a k'asa ta karasa gida. Da Sallama ta shiga ciki bah kowa a tsakar gidan dan haka ta aje trayn Sannan ta leka dakin Mama, zaune ta sameta k'an sallaya. Mama najin Sallamanta ta mik'e dasauri
"Sulthana ina kikaje? Ance anga wasu sun turaki mota"
Gabanta ne ya fadi ta fashe da kuka
"Wasu neh suka saceni"
D'an zaro ido Mama tai ta shiga jujuya Sulthanan tana dubata
"Basu dai miki komai bah koh"
Kai ta gyada tana cigaba da kuka a hankali..

Jin kamar magana daga dakin Mama yasa Hafsatu da Ameenatu fitowa daga dakinsu, dai dai nan Sulthana ta fito zata koma zaure, Hafsatu ce ta kada baki tace
"An dawo yawon dandin yawon iskanci, ai dama nasan bah wani saceki da'akai"
Tsaki Ameenatu tai tareda rik'e kugu
"Kuma bai wuce Wannan likitan nifah na tsaneshi, dan na lura dan iska neh. Koda yake ai yar uwa ya samu"
Mama tafito dasauro ta daka musu tsawa
"Kul! Ameenatu karna k'ara jin wannan maganan a bakin ki, wai meke faruwa neh? meyasa Ameenatu duk kika chanza"
Juya kawai tai ta shiga daki, itako uwar marasa kunya Hafsatu cigaba tai da Aibanta Sulthana har saida Mama tayo k'anta Sannan tabar wajan a guje..

Kuka sosai Sulthana take a inda take tsaye, karasowa Mama tai ta dafata
"Ki daina kuka kinji, wata rana sai labari"
Kai Sulthana kawai ta gyada batace komai bah
"Maza dau buta kiyi sallah kizo kici abinci" cewar Mama
Bah musu tadau butan ta dibi ruwa ta shiga bayi..

Sai Bayan isha'i Baffa ya shigo gidan, tun yana waje yaga shigowan Sulthana, baice komai bah ya shiga dakin Mama, Sannu da zuwa tamai Sannan ta kawo mai Abinci. Yanaci tanamai Fifita tace
"Sulthana ta dawo, kaji saceta akasoyi"
Tsaki Baffa yayi
"Ina ruwana, dama an saceta na huta"
Kallanshi Mama tai baki bude
"Mallan kakosan abinda kake fada"
Baice komai bah saima Sulthana daya soma kwalama Kira, tana gefen rijiya tsugunne tanacin Abinci taji kiran. Amsawa tai ta nufi dakin dasauri, Saida tai sallama Sannan ta shiga...

Hannu Baffa ya mik'a mata, tasan me yake nufi dan haka ta ciro kudin a gefen zaninta ta mik'a mai. Amsa yayi yana duba kudin tareda k'allan Mama wacce itama kudin take K'allo
"Kindai gani da idonki koh? Sababbin kudi gar haka"
Girgiza kai Mama tai ta kauda kai gefe. Tab'e baki yayi ya k'alli Sulthana wacce kanta ke kasa tana jiran hukuncin da Baffa zai yanke a kanta, ga mamaki sai taji yace
"Tashi ki bani guri, abinda zan gaya miki shine kada ki sake ki kawomin Cikin Shege gida"
Hawaye ya ciko idonta ta fita daga dakin ta nufi zaure ta fashe da kuka mai sauti.
"Haba Mallan wannan wanne irin abu neh da kanka kaita aibanta y'arka kana mata baki"
Dogon tsaki Baffa yaja ya wanke hannu cikin roban dake kusa dashi ya mik'e yabar dakin..

Kuka mai isarta tai Sannan ta sulalle a wajan ta kwanta, tunanin abinda ya faru dazu tai, Yau data fadama wani halin datake ciki har tadan samu sauki azuciyarta. Lumshe ido tayi ta bude a hankali tareda sakin Murmushi
"Yau naje birni" ta fada a hankali tana cigaba da murmushi _Lol oh bakauyiya_
Da shirmen tunane tunanen tah barci ya dauketa..

Yauma kamar kullum Bakin Kasuwa taje kamar yanda ta saba, mutane sai mata jaje suke itadai saidai tai murmushi idan sukace Allah kyauta na gaba bata amsawa a ranta kuma fadi take bah Amin bah _kujimin Sulthanan nan fah haha_
Yau da wata benz yaso bakin Kasuwan, chan bayan wajan yayi parking ya tura yaro ya kiramai ita. Tana zaune yaron yazo yace
"Wai kije ana kiranki"
D'an zaro ido tai tana k'allan yaran
"Wah?"
Girgiza kai yayi yana cewa
"Bansan sunanshi bah, wani neh a k'atuwar mota"

Bata kawo komai bah ta mik'e ta tabo Murja dake kusada ita
"Dan Allah murja ga tsaron Gyadata ina zuwa"
Tho murjan tace ita kuma Sulthana tabi hanyar da yaran ya nuna mata. Motan ta hango tayi slow ta tsaya tana k'arema motar kallo dan bah karamin burgeta yayi bah. Ta mirrow ya hangota ya fito yana mata murmushi, wajan motan ta k'arasa ta manna k'anta jikin windown tana K'allan ciki. Dagowa tai tana turo baki
"Ina K'awata"
Sumar kanshi ya shafa Yana y'ar murmushi
"Yau kam k'awarki bata nan suna biki"
Hannu ta rungume tana cigaba da turo baki.
Kurri Masroor yayi yana k'allanta, ganin hawaye cike a idonga yasa ya k'araso gabanta ya riko hannunta suka zauna bakin bishiyan dake wajan
"Karkiyi kuka kinji, gobe na miki Alkawari tare zamu zo"
K'ara tunzure baki tai ta kauda kai, d'an dariya yayi
"Dama haka kikeda rigima? Lallai akwai aiki"
Juyowa tai ta k'alleshi murya K'asa k'asa tace
"Yaya"

Juyowa yayi ya k'alleta da mamaki, har ya bude baki zaiyi magana wayanshi ya fara ringing. Hannu yasa a aljihu ya ciro ganin sunan dake jiki tasa ya dauka yana murmushi
"Old Friend, yau ka tuna dani"
Shiru yayi yana sauraren mai kiran yana murnushi Sannan yace
"Oops! Wallhi bana gida naje wani guri bt nan da 1hr I wl b on my way"
Shiru ya k'arayi Sannan yayi dariya mara sauti Yace
"Kah bata haquri ai nima zanzo"
Sallama sukai ya kashe kiran yana k'allan Sulthana da itama shi take K'allo..

Murmushi yamata itama ta maidar mai, mikewa yayi ya bude motan ya ciro wani leda ya mik'a mata.
"Gashi tsaraba nane"
Mak'e kafada tai tana k'allanshi kasa kasa
"A'a idan aka gani a gida dukana za'ayi"
Tsugunawa yayi daidai Saitin Fuskanta Yace
"Ki ansa ai bah nace kije dashi gida bneh"
Amsa tai ta soma bude ledan, Takeway neh da drink sai Icecream da cake. Takeawayn taketa Kici kicin budewa, dariya ya mata ya amsa ya bude mata, K'allan Abincin tai Sannan ta kalleshi
"Duka nawa neh"
Kai ya gyada mata yana cigaba da k'allanta da narkakun idanunshi..

Abincin ta soma ci hannu baka hannu kwarya, Kallanta yake cikeda tausayi, saida taci tai nak sannan ta dago tana mai murmushi
"Nagode Yaya"
Murmushi shima ya mata yasa yatsa ya taba Dimple dinta. Mik'ewa tai dasauri tana zare ido.
"Yaya lokaci na tafiya kuma ban saida gyada tah bah"
Hannu yasa a aljihu yace
"Nawa neh kudin gyadan?"
Girgiza mai kai tai dasauri
"A'a kah barshi wanda nakai jiya saida Baffa yamin Fada"
Kai ya jinjina kawai
"Yaya ka tafi nima zan koma, kah gaida min K'awata"
Bata jira mai zaice bah ta fara tafiya tana waigenshi tareda daga mai hannu. Binta yayi da k'allo harta bace...


*Shin ya labarin Dr Fareed neh??*

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 126 to 130*

Bata jira mai zaice bah ta fara tafiya tana waigenshi tareda daga mai hannu. Binta yayi da k'allo harta bace ma ganinshi, Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya shiga motarsa yaja yabar wajan...

Saida ya shiga cikin gari sosai Sannan yadau waya ya soma kira, ana dauka yace
"Am on my way na kusa gida"
D'an murmushi yayi Sannan yace
"Ok sai kah karaso"
Ya kashe wayan ya tura a aljihun shi. Bai zame koh ina bah sai gida, a haraban gidan yaci k'aro da Mahnoor ita da wasu masu aiki tana tayasu shara, girgiza kai kawai yayi ya nufi side dinshi. Tana ganin ya wuce ta aje tsintsiyan ta bishi, wanka ya farayi sannan ya fito Cikin Threequaters dah T shirt fari kal, zaune ya samu Mahnoor a falonshi tana K'allo, jin Karan bude kofa ta shagwabe fuska ta dago tana kallanshi
"Bro Masroor shine ka tafi bakaje dani bah koh"

Zama yayi kusa da ita ya kamo hannunta
"Am sorry sis, kinga fah bakwa nan and I cnt wait har sai kun dawo, dnt uh worry wata rana nan zata dawo ku zauna tare"
Zaro ido tai ta saki murmushi
"Allah dagaske bro Masroor"
Kai ya gyada mata shima yana murmushin _kujimin wannan masroor din fah taya zata dawo gidansu_

Phone dinshi yadau ringing ya dauka Sannan yace
"Ok ganinan zuwa"
Ya kalli Mahnoor wacce itama shi take kallo
"Barinje nayi bako"
Tare suka fito ita ta nufi side dinsu shi kuma ya fita wajan gate, a kofar gidan ya ganshi zaune Cikin mota, karasawa yayi yana y'ar murmushi
"Uh welcome old friend"
Dariya yayi Sukai musabaha, Masroor yace
"Wai gidan bakonka neh dah bazaka shiga bah"
K'asumbarshi ya shafa yana y'ar murmushi
"Banasan Mami ta ganni neh dan nasan sai nasha surutu"
Dariya Masroor yayi mai sauti
"Surutu koh sai kasha shi indai mami ce, saidai kah rufe ido kah toshe kunnuwan kah"

Yasir neh yayi parking ya fito yana murmushi
"Kai wah nake gani haka?"
Hannu yabashi suka gaisa "Dama ana ganinka"
Dariya yayi
"Yasir knan dama kana nan?"
A tare suka shiga cikin gidan zuwa side din Masroor, maids din gidan suka shiga hidima dasu. Jin surutu na tashi daga side din Masroor yasa Mahnoor ta shiga side din tana rarraba ido, dagowa bakonsu yayi yadan zare ido
"Wah nake gani nan kamar Mahnoor, lallai kin zama big girl"
Murmushi tai ta k'arasa kusada shi ta zauna
"Bro Sannu da zuwa"
"Yauwa" yace yana shafa kanta yana murnushi. Zamewa tai daga jikinshi ta fita daga daga side din... batafi minti biyar da fita bah wayan Masroor ya soma ruri..

Dauka yayi yasa a kunni sannan yayi murnushi yace
"Ok gamu nan zuwa"
Dariya ya saki mai sauti yana shafa sumar kanshi, binshi da kallo sukai da mamaki, sai dayayi mai isarshi Sannan yace
"Numbernka ya fito Mami na kiranka, kuma nasan Mahnoor ce ta fada mata"

Dariya Yasir shima yayi
"Kace mai lefi neh?"
Kai masroor ya gyada yana cigaba da dariya a hankali. Murmushi yayi ya mik'e
"Tho ku tashi muje"
Bah musu suka tashi suka nufi side din Mami, A falonta suka sameta zaune da bakuwa, kan carpet suka ya zauna su kuma Masroor da Yasir sukai d'are d'are akan kujera, sunkuyar dakai yayi sannan yace
"Ina yini Mami"

Kallanshi Mami ta tsaya yo jin shiru yasa ya dago suka hada ido ya maida kai dasauri
Murmushi tai
"Likita bokan turai Kama daga kai kawai, wato kasan bakada gaskiya shine harda zama a kasa"
Dagowa yayi yana y'ar dariya
"Mami knan kiyi hakuri, bana zama neh shiyasa"

Masroor da Yasir sai dariya suke mai yanata susunne kai, Mahnoor ce ta shigo falon ta zauna kusadashi a Kasa
"Bro fareed zakaje dani wajan Umma"
_niko Ummy Abduol zaro ido nai jin sunan da mahnoor ta fada_ wah knan take nufi?

*manage dis banida chargi*

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 136 to 140*

*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

Wannan Shafin Sadaukarwa ce gareku All *Da Bazarmu Writers Association* Members.. Allah ya bar K'auna.

Shekewa da dariya Hafsatu tayi harda tafawa
"Gaskiya neh Baffa haka yayi"

K'ara rushewa da kuka Sulthana tai jin Abinda Baffa yace, Saida tai mai isarta Sannan ta shigo cikin Gidan idanunta a kukumbure. Gyadan daya saba aje mata a kofar dakinshi ta dauka ta daura a wuta ta koma gefe tana cigaba da hawaye...

Yana dahuwa ta sauke ta zuba a tray, batayi mah Mama sallama bah ta tafi, inda suka saba zama ta hango Motar Masroor, ta k'arasa jiki asanyaye ta samu guri ta zauna batareda tamai magana bah. Sam bai lura da tazo wajan bah saida ya leko tah glass din motarshi sannan ya hangota zaune tayi tagumi, fitowa yayi dasauri ya k'araso inda take ya zauna
"Sulthana meke damunki"
Shiru tai k'anta a kasa

Ya marairaice Fuska yana cigaba da K'allanta
"Banasan ina ganinki cikin damuwa kinsan fah ina..."
Kasa k'arasa Maganan yayi ta dago jajayen idanunta tana kallanshi. Ajiyan zuciya ya sauke
"Meyasa yau kike so boyemin damuwarki? Nifah Abokinki neh kuma yayanki"
Hawaye ne ya gangaro mata, ta dago tana k'okarin Fashewa da kuka
"Baffa neh zaimin Aure"
"What?"
Fashewa da kukan tai ta duk'ar dakai K'asa

Rudu Masroor ya shiga ya mik'e ya dawo gabanta ya tsugunna
"Sulthana kin Tabbatar da abinda kike gayamin"
Batace komai bah sai kukan data cigaba
Suman kanshi yaja ranshi b'ace
"Pls Banasan kukan nan, ina jinshi har cikin raina. Just answer my question"

Ganin tak'iyin shirun yasa ya mike tsaye, k'ugunshi ya rik'e da hannu daya, dayan kuma yana cigaba da jan suman kanshi. Nan da nan idanunshi suka kad'a sukai ja
Tsugunawa yayi guiwa biyu a k'asa
"Pls stop crying, fadamin meya faru"

Cikin sheshekan kuka ta bashi labarin duk abinda ya faru
"No!!!" ya fada da k'arfi hakan jaya hankalin mutanen dake wajan suna k'allansu, bai damu da yanda ake kallansu bah saima cigaba da magana dayayi cikin D'aga murya
"No 1 can snach uh from me, u're mine."
Duk abinda yake fada bah wanda Sulthana tasan ma'anarshi idan bah no din bah, duk'ar dakai kawai tai saboda yanda mutane ke K'allansu

Gani tai ya mik'e ya shiga motarshi yaja yabar wajan da gudu. Bin motan tai da k'allo ta k'ara fashewa da matsanancin kuka, cikin muryan kuka take magana a hankali
"Shiknan yaya yayi fushi ya barni na shiga uku, meyasa Baffa baka sona? Menai maka??"
Hannu ta daura akai tana kuka wiwi
"Mama meyasa kika tafi kika barni? Kowa baya sona ki dawo dan Allah"
Mutanen dake wajan sun tausaya mata matuk'a jin kalaman datake fada..

Wasu ko basa sha'awar gyadan suna siya dan su rage mata radaddin datake ciki, haka taita bah mutane tana cigaba da kuka harta siyar. Hanyan da Masroor yasaba bi taketa k'allo tana hawaye, ganin bai dawo bah yasa ta mik'e jiki a sanyaye ta kama hanyar gida...

Gudu Masroor ke shararawa kamar zai tashi sama, Ikon Allah ne kawai ya kaishi gida, baiyi wani k'wakwaran parking bah ya fito ya nufi side din Mami idanunshi jawur. Bell ya danna aka bude mai ya shiga, masu aiki sai gaidashi suke anma baiko kallesu bah ya nufi falon Mami. Ganin bata falon sai bak'inta dake zaune suna jiranta yasa ya k'arasa dakinta, knocking yayi a kofar dakin ta amsa tareda tambayan waye
"Masroor" yace atakaice
Bashi umarni tai daya shigo

Yana shiga suka hada ido ta mik'e dasauri ganin yanda idanushi suka rune
"Son whats wrong"
K'asan dakin ya zauna yana cigaba da ajiyan zuciya
Mami ta k'araso kusadashi tareda dafashi
"Son tell me whats wrong pls, meke damunka? Why are you like dis"
Kama hannunta yayi ya ya dago ya k'alleta idaunshi Cikeda kwalla
"Mami som1 wnts 2 snach her from me, I love her, I so much love her. Shes my happiness, I cnt do without ha"

Fashe mata da kuka yayi ya duk'ar da kanshi kasa
Rungumoshi jikinta tai itama hankalinta tashe
"Its ok son, stop crying. Cool down and tel me meya faru"

Kasa magana yayi sai kukan daya cigaba dayi, dak'yar ta ja hannunshi suka mik'e tsaye, hannunshi ta rik'e ta kaishi side dinshi. Bedroom dinshi ta shiga dashi tareda zaunar dashi kan gado, tsugunawa tai ta ciremai cover'n dake kafanshi sannan ta mik'e tana shafa suman kanshi
"Its ok son have some rest, idan kah huta sai muyi maganan kaji"
Kai kawai ya gyada mata, ta fita daga dakin cikeda damuwa...

Masu aiki tasa suka kaimai abinci, anma koh kallan abincin beyi bah..waya Mami ta d'auka ta kira Yasir bai d'au lokaci bah ya k'araso gidan a rud'e. Falon Mami ya fara zuwa saboda tace ya sameta.
Da sallama ya shiga ya sameta zaune tana y'an rubuce rubuce. Zama yayi ya gaidata, ta amsa fuska bah walwala..

Duk abinda ya faru ta zaiyanama Yasir sannan tace
"Yasir nasan kai zakafi kowa sanin wanda Masroor yakeso, baya cikin hayyacinshi dats why ban tambayeshi bah"
Yasir yayi murmushi ya gyara zama yaba Mami labarin tun sanda suka soma ganin Sulthana har zuwa daukota da Masroor yayi da labarin data basu nata. Mami ta share k'walla tace
"Yasir meyasa tuntuni baku fadamin bah? Yarinyan nan bah kalar Masroor bace anma kodan yanda yak'e santa zan hakura kuma nasan Alhaji zai yarda"

Shiru yayi baice komai bah kanshi a k'asa, Mami ta cigaba da cewa
"Ya zamuyi yanzu Yasir? Masroor na dak'i yana kuka"
Jin haka yasa Yasir mik'ewa dasauri ya nufi side din Masroor hankalinshi tashe..

Zaune ya sameshi yanda Mami ta barshi, saidai yanzu bah kukan yake bah. Ya k'arasa ya zauna kusa dashi
"Friend why all this?, uh have to be strong. Komae zai zama normal"
Masroor baice komai bah sai girgiza kanshi dayayi. Dak'yar yasir yasamu yaci abincin ya hada mai ruwan wanka yayi sannan yajashi suka tafi yawo ko hakan zaisa ya rage tunanin dayake...

Washe gari kamar yanda Fareed da Sa'ood sukayi hakan neh ya faru, karfe hudu a kauyensu Sulthana tai musu, bayan layinsu Sulthana sukai parking motarsu, yaro suka samu suka hadashi da sabuwar dari biyar ya musu k'iran Babban Almajirin mallan.

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 131 to 135*


"Bro Fareed zakaje dani wajan Umma"
Rik'e baki Mami tayi tana kallan Mahnoor
"Mahnoor da yawo, sae kace taci kafan kare. Tho schl din fah"
Zumbure zaki tayi ta juya baya,
"Mami kinga fah sai bro fareed ya rink'a kaini"
Kanta fareed ya shafa yana y'ar murmushi
"Sis ki bari idan akai hutu da kaina zanzo na daukeki kinji"
Kai ta gyada ta mik'e tabar wajan tana gungunai..

"Likita bokan turai aure fah?"
Sosa kai yayi kanshi a k'asa
"Mami na kusa, kiris ya rage"
Gyada kai Mami tai tana murmushi
"Gaskiya kah kyauta kaga wadannan"
Ta nuna Yasir da Masroor
"Sunk'i aure suna nan sai gantali"
Dariya mai sauti Yasir keyi ya dafa kafadan Masroor
"Mami ai shagwababen naki ya kusa, hmm zan baki labari anjima"
Dukan wasa Masroor yakai mai
"Mami k'arya fah yake"
Tabe baki tai ta kauda kai kudai kuka sani..

Fareed ya mike yana cewa
"Mami zan tafi, dama na shigo ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login