Showing 42001 words to 44304 words out of 44304 words

Chapter 15 - SULTHANA complete Hausa Novel

25 Jul 2025

1435

BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 199*

Lefe na gani na Fada aka kawo kowaccen su akwati dozin biyu akai mata. Mutanen Kauyen sai shiga suke suna kallan kaya kowa na tofa Albarkacin bakinshi..

Ranar Alhamis Ameenatu da kawayenta Sukayi k'auye day, su kuma su Sulthana dukayi Fulani day itama itada nata k'awayen. Ranar Juma'a aka sasu Lalle da daddare. A Daren Masroor da Fareed sai d'an rakiyansu Yasir dukazo gidan, a tare amaren suka fito kowacce ta k'araso wajan angon nata. Masroor sai Kallan Sulthana yake da Murmushi

"Beauty kin k'ara kyau meye sirrin?"

Rufe fuskanta tayi da Hannayenda da sukasha had'adden kunshi. Ya rik'o hannunta yana kallo yace

"Waya miki wannan design din yayi kyau sosai"

D'an murmushi tayi ta turo baki

"Ya Masroor ka daina wannan maganan kanasa inajin kunya"

Dariya yayi yana shafa sumar kanshi

"Ki daina jin kunyana beauty, nidake yanzu mun zama d'aya karki manta gobe za'a daura mana aure ki zama tawa na xama taki"

Hannu tasa ta rufe fuskanta tana dariya K'asa kasa, daidai nan Yasir ya karaso wajan yace

"Ni kun barni chan gefe"

Ya kalli Sulthana

"Madam kinsan meye?"

Ta girgiza kai tana kallanshi, ya gyara tsayuwa ya sassauta Murya

"Nifah Sistern nan naki nakeso"

Tace "wah kenan?"

Yace "Hafasat"

Da zumud'i tace

"Dagaske?"

Kai ya gyada Mata, Masroor yayi saurin cewa

"Dallah kyalle wannan, mayaudari neh karki yarda
kadama ki fadamata"

Duka Yasir yakaimai

"Kai bansan fah iskanci i'm serious"

Sulthana tace

"Karka damu Ya Yasir zansan Yanda zanyi"

Godiya ya mata yabar wajan. Sun d'an taba hira sannan suka musu Sallama Suka tafi..

Washe Gari ya kasance ranar Sati, a ranar duban mutane suka shaida d'aurin auren Fareed da Ameenatu, sai Masroor da Sulthana. D'aurin auren daya samu hallartar Manyan Mutane tun daga kan shi kanshi shugaban k'asa, Gwamnoni, sarakuna da saurayan Manyan mutane masu fada aji a nigeria..

Har hawaye saida Baffa yayi dan bai taba tunanin zaiga irin wadannan Mutanen bah a rayuwarshi. Masroor baki yak'i rufuwa, Ana gama d'aurin aure yad'au wayanshi ya soma nemqn layin beauty. Ya dad'e yana ringing kamin a kawo mata ta d'auka tana y'ar Murnushi, cikeda Farinciki yace

"Beauty am now urs uh are mine. An d'aura"

Dariya tayi ta kashe kiran tad'au buta tayi alwala tazo ta tada nafila. Addua tayi sosai har tana hawaye musamman data tuna ana aurenta Ummanta bata raye, tayimata Addu'a sosai. Sannan ta tashi ta koma cikin k'awayenta..

Anyi d'aurin aure lapia kowa ya koma gudanshi. Wuraren k'arfe hudu na yanma aka d'au Amare dan kaisu Gidajensu, Ameenatu da Sulthana sai kuka suke bama Kamar Ameenatu, Nasiha mai ratsa jiki tayi Baffa da Mama sukai musu sai Maman Sadiya. Sannan aka d'aukesu zuwa government house..

Su kuma achan ake shagalin bikinsu Fareed da Masroor dan sun hada taron ne shi yasa gidan ya cika mak'il bah masaka tsinke. Yan kauye nan suka saki baki suna kallan Aljannar duniya, Wani had'aden Part dake gidan aka kai Sulthana, ita kuma Ameenatu sai daga baya za'a kaita. Mai make up aka kira ta d'andasa musu kwaliya sukasa had'aden golden gown dan zuwa dinner. Yau k'auye duk an basu anko sunsha sunata washe baki cikeda Murna. Kowacce Amarya tareda angonta suka tafi wajan dinnern, suma angon nan cikin Babban riga Fari tas dah aikin Golden. Sunyi kyau ainun gwanin ban sha'awa

A gurin dinner anci ansha anyi nak, su deejatou harda zuba abinci a leda lol. Bayan an gama an dawo sannan Aka kai Ameenatu gidanta. Washe Gari da safe akayi bud'an kai, shima wani buki akai na musamman Bayan an gama akasa yan kauye a mota aka maidasu bayan an cikasu da alheri sunata godiya. Aka bar Sulthana daga ita sai Mahnoor, Aisha batasamu zuwa bikin bah dan ta koma makaranta...

Mahnoor batabar Side dinbah saida sukai sallan isha. Wuraren k'arfe tara ango ya shigo sanye da fara k'ar din yadi sai zuba kamshi yake Hannunshi rike da leda, k'ara rufe fuskanta tayi cikin gyale tana wasa da zoben zinarin dake hannunta. Kan gadon ya zauna gefenta a hankali yasa hannu ya yaye gyalen ya d'ago fuskanta, runtse ido tayi tana murmushi shima murmushin yayi yace

"Open ur eyes beauty, Masroor dinki neh."

Tad'an bude ido kadan tareda janye fuskanta ta dan kauda kai. Hulan dake kanshi ya aje gefen bedside ya mik'e tsaye tareda riko Hannunta

"Tashi muyi Alwala muyi nafila dan mugodema Allah"

Bah musu ta mik'e shi ya fara shiga yayi alwalan ya fito Sannan itama ta shiga. Ko kamin ta fito ya shinfida musu Sallaya, tana fitowa ta yafa gyalenta suka tada sallah.

Bayan sun idar ya d'auko ledan daya ajiye yace

"Dauko mana plate Beauty"

Bah musu ta mik'e ta aje gyalanta akan gado ta fito daga dakin, shige shige ta soma yi dakyar ta gano kicin din. Tsayawa tayi tana k'arema wurin kallo dan kaya neh mak'il a ciki masu tsada da daukar ido, murmushi tayi dan tasan wannan aikin Mami ce. Kwalin dinner set ta d'auko dakyar ta bud'e ta ciro plate ta wanke sannan ta d'auko cups shima ta wanke ta koma dakin. A gabanshi ta ajiye tana kokarin mik'ewa, dasauri ya rike hannunta ya jata ta fado jikinshi

"Ina zaki? Ai tare zaki zauna muci"

Turo baki tayi tana kokarin fizge jikinta daga nashi

"Nifah na koshi dazu muka gama cin abinci da Mahnoor"

Yanda tayi maganan bah k'aramin burgeshi yayi bah har saida ya kwaikwayi yanda tayi. Dariya tad'anyi ta k'ara shagwabe Fuska

"Nidai ka daina"

Kazan ya saka a plate din ya bud'e fresh youghut ya zuba a cup dinda ta ajiye Sannan ya soma bata a baki. Kauda kai tayi tana yatsine fuska

"Nifah ya Masroor na koshi"

Matso da fuskanshi yayi daidai nata har numfashinsu na had'uwa

"Wai yaushe za'a chanza min suna neh daga Ya Masroor"

Batace komai bah sai murmushi datayi. Tura mata kazan ya somayi tana ci tana bata fuska kamar xatai kuka, shi kuma yana mata d'ariya. Tadanci bah lefi sannan ta mik'e ta xauna kan gado tana cigaba da yatsine fuska

"Kagani koh kasa cikina ya cika dayawa"

Mik'ewa yayi ya kamo hannunta

"Tho zo na miki doki nasan cikin zai sassauta"

Tsugunawa yayi a kasa sannan yace tahau. bako kunya ta d'ane bayanshi ya soma tafiya ita kuma sai dariya takeyi, sun dad'e suna haka sannan ta sauka tana hanma a hankali

"Bacci nakeji"

Kai ya gyada yace yana zuwa ya fita daga d'akin. Kamin ya dawo ta shiga toilet tayi wanka ta fito ta sauya kayan jikinta zuwa na barci tahau gado nan da nan barci ya d'auketa

Wanka ya shiga yayi a d'akinshi, koda ya dawo nata ta dad'e dayin bacci. Hannun jalabiyar jikinshi ya nad'e ya d'auketa chak ta bud'e ido dasauri tana kallanshi Murnushi ya mata ganin yana kokarin fita da ita daga dakin yasa ta soma zulezule, bai direta ko inaba sai lumtsatsiyar gadonshi.

Mikewa tayi ta zauna a tsorace

"Ya Masroor Bacci fah b
Nakeji"

Bako kunya yace

"Kazana da kikaci zan amsa abuna"

Bata gane me yake nufi bah tace

"Tho bah kai kace naci bah ni yanzu ina zan samu kaza na biyaka"

Tana magana cikeda shagwaba. Fitilan d'akin ya kashe ya rage na side lamp sunada haske sosai dan su kadai mah sun wadata d'akin. Kan gadon ya hau ya matso kusada ita tad'an mata, ya kara Matsowa ta k'ara Matsawa

"Beauty ni dodone? Meyasa kike matsawa"

Shagwabe fuska tayi

"Ni tho ka kwanta a gefe nima na kwanta a gefe"

Maganar tazo mai a bazata anma ya share yace

"Anma ai keh matata ce xan iya kwantawa a kusa dake ai"

Batace komai bah sai chuno baki datayi, matsowa yayi kusada ita ya rikota tareda matseta a jikinshi. Bud'e baki tayi zatai magana ya had'a bakinshi da nata. Ina ganin haka na tattara inawa inawa nabar musu gidan gaba d'aya na koma k'auyenmu..

*Bayan Wata hud'u*

Masroor ne zaune a falo yana daddana system dinshi, hankalinshi duk ya tattara ga abinda yakeyi. Sulthana ta fito cikin wani riga pink iya cibi da wani matsatsen short, kayan sun mata kyau sosai. Jikin Masroor ta fada tana maida numfashi. Dasauri ya aje system din ya k'ara matseta a jikinshi

"Beauty naji jikinki ya k'ara zafi, nifa zafin jikin nan na. Cutana gashi kinki yarda muje asibiti"

Batace komai bah saima janye jikinta datayi daga nashi ta koma chan gefe ta zauna. Kara matsowa yayi yana kokarin tabata, bai ankara bah ta soma kwararo mai Amai, Aman take sosai jikinta na rawa. Riketa yayi har saida ta gama sannan ya mik'e ya dauko ruwa ya bata ta kuskure baki ya dauketa ya kaita daki ya kwantae da ita. Masu aiki ya kira suka gyara wajan ya koma dakin

Kwance ya sameta tana juye juye jikinta bah dad'i, daukanta yayi chak ya kaita bayi ya mata wanka ya fito da ita. Da kanshi yasa mata kaya ya d'auketa yasata a mota sukad'au hanya. Tana ganin sun nufi asibiti ta soma bata fuska, baice mata komai bah. Da kanshi ya d'auketa suka gida, bah tareda wani b'ata lokaci bah aka dubata tareda mata gwaje gwaje, a nan neh aka gano cikin datake d'auke dashi na wata biyu.

murna sosai Masroor yayi, d'aukanta yayi suka nufi gidan Mami bayan an rurubuta mata magunguna tareda bata shawarwar..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 200*

🔚

Da Farinciki suka k'arasa gidan Mami bah ko kunya ya mik'a mata takardan test din itadai Sulthana na zaune k'anta a kasa. Mami na gama karantawa ta girgiza kai tana mai cikeda farinciki

"Allah ya raba lapia"

Ga Mamakin Mami da Sulthana saijin Masroor sukai yace

"Ameen Mami"

Kunya sosai Sulthana taji har ta k'ara duk'ar dakai, shiko gogan ko a jikinshi. Tun daga ranar Sulthana ta k'ara samun kula daga wajan Mami da Masroor da duk sauran yan gidan mah. Tattalinta sukeyi sosai kamar kwai hakan bah k'aramin sata farinciki yayi bah..

A bangaren Fareed da Ameenatu basuda Matsala zama suke na soyaiya da mutunta juna. Ita tana d'auke da nata cikin na wata uku, Mama da Baffa bah k'aramin farinciki sukayi bah da samun labarin cikin da y'ayansu suke d'auke dashi. Yasir da Hafsatu sun hada kansu har anma Ranar biki. Haka Sadiya k'awar Sulthana da S'aood wanda ya ganta lokacin biki ya lik'e mata.

Bayan wata shidda Ameenatu ta haifi santalelen d'anta namiji inda akasa mai suna Farhan. Bayan wata d'aya Sulthana ta xankado santaleliyar Y'arta mai kamada Masroor sak. Murna wajan su Mami ba'a magana. Inda yarinya taci sunan Mahaifiyar Sulthana wato Rabiatu anma ana kiranta da Mimi. Kula Sulthana take samu itada jaririyarta sosai daga bangarorin biyu hakan yasa ta saki jikinta tana shayar da y'arta hankali kwance..

Ban k'ara komawa government house bah sai bayan Shekara biyu. Anan nakejin Labarin Ansha bikin Hafsatu da Yasir haka na Sadiya da Sa'ood dukanninsu suna d'auke da tsohon ciki haihuwa yau ko gobe. Sai Mahnoor dake karatunta na likita a k'asar Masar

Had'adiyar Mace mai jida kanta na gani ta fito a wata lumtsatsiyar Mercedes benz, saida na k'ara matsawa dakyau naga Ashe Sulthana ce. A gajiye ta shiga gida ta fada kan kujera tareda fadin wash. Y'ar yarinya ce fara sol kana ganinta kaga Masroor saidai tafi Masroor din haske ta taho dasauri da tafiyanta dabai gama k'wari bah ta fada jikin Sulthana. Rungumeta ta k'arayi tana y'ar Murnushi

"Mimi ina kikanar nannyn naki"

Dai dai nan nannyn ta karaso wajan a guje tana kwalla ma yarinyan kira. Ganin Sulthana yasa tayi turus ta tsugunna tana gaidata. Amsawa tayi ita kuma yarinyan sai k'ara shiga jiki Mamanta take tanama Nannyn dariya. Sulthana ta kalli Nannyn tace

"Barta kawai tunda na dawo"

Tho tace ta tashi tabar wajan ita kuma ta k'ara shigewa jikin Mamanta. Dadaddare tana kwance akan cinyar Masroor suna k'allo yace

"Beauty ya jamb din yayi sauki koh"

Murnushi tayi

"Sosai mah"

Ya janyota ya k'ara matseta jikinshi yana shakar kamshinta

"Anya baza'a bar karatun nan bah sai shekara mai xuwa? Dan ni k'ani nakeso aima Mimina"

Mikewa Sulthana tayi dasauri tana turo baki

"Gaskiya my pearl bah yanzu bah, haihuwa fa da zafi."

Yayi dariya ya kama hannunta cikeda xolaya yace

"Tho shiknan yanzu ni sai kimin cikin ni na haihu kinga sai a rinka rabawa koh"

Kyalkyalewa da dariya tayi ta mik'e tabar wajan ta biyota tana ganin ya nufo dakinta ta tura kofan ta rufe tareda sa key tace

"Gaskiya My pearl yau ka barni na huta na gaji kullum abu d'aya"

Kwafa yayi yace

"Zan kamaki neh xaki sani"

Bai jira mai zatace bah ya shige Dakinshi yana cizon Yatsa..


A nan zance Allah ya baku Zaman lapia mai d'orewa ya k'ara muku k'aunar juna Ameen..


ALHAMDULILLAH

A nan na kawo k'arshen littafina mai suna Sulthana.. Allah ya bamu ikon Anfani da darusan dake ciki. Kurakuren danayi Allah ya yafeni Ameen


Ina godiya ga Masoyana na nesa dana kusa. Ina alfahari daku dan da bazarku nake rawa Masoyana

*Bazan Manta daku bah*

Ayoush yusuf
Ummyn yusrah(my ruhi)
Jannart lameed'o (my zuciya)
Sumaiya d'an fulotiee (Allah yasa na fadi sunan daidai)
Members na pure moment of life writerd
Hajiya Fateema
Aisha zagi
Fati azland
Deejatou
Meela adeel
Nafeesah hasheer
Zeenaseer
Hafsatbm
Ummiey
Fatima adamu
Nana khadeejah
Maman zakiya
Wai kumin Afuwa kunada yawa. Kuma wadanda ban anbata bah kunsan kanku ina Alfahari daku ina mik'a gaisuwata gareku

*Sadaukarwa*

Na sadaukar da wannan littafi ga late Rabiatu s suleiman (mrs usman kademi) Admin House of novels Allah ya gafarta miki yasa Aljannatul firdaussi ya zama makoma a gareki yasa kina a kyayyawan Makoma Ameen..

*Kyautarwa ga*

Mahaifiyata Allah yaja kwana Mama..

*Jinjina*

Ga Members na dabazarmu Writers Association. Kunyi neh Allah ya barmu tare..

*Godiya ta musamman*

Sulthana novel fans
Dabazarmu writers association
Musan kanmu Marubuta
Musan juna o.h.w
Deejatou novels
House of novels
Itace kaddarata fans grp
Preety queen novels
B u hamzert novels grp
Feedoh online novels
Marubuta
Marzah hausa novels
Sweerys novels fans
Duniyar novel
Mukaru da juna
Mata rahamane
Jannart lameed'os novels grp
Jinin Sarauta fans
Tamamancy novels
Facebook surbajo fans
M.kaoje novels
Fareedat novels grp
Hausa novels by surbajo
Ummyn yusrah novels
Ko ajikinmu
Maryam salisu maidala
Da duk sauran grps daban anbata bah. Ina jinjina a gareku na gode sosai.. Ummy Abduol na sanku.

Sai kunjini a sabon littafina nan bada dad'ewa bah

Taku har kullum

Ummy Abduol✍🏻

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login