Showing 12001 words to 15000 words out of 44304 words
yakai dubanshi Ga Ahmad
K'allan Sanni Masroor yakemai Anma ya manta a inda ya sanshi. Jan Hannun Hafsatu Ahmad Yayi yana cewa
"Ki Kyale kawai mu tafi inace ai kince zaki gayama Baffan ku"
Janta ya dingayi tana cigaba da zage zage Har suka bar wajan...
Juyowa Masroor yayi anma yaga Wayam bah Sulthana, K'allan Yasir Yayi da Alamar Mamaki
"Ina Yarinyan nan Take"
Yasir ya K'alleshi
"Tah Tafi"
Naushin Iska Masroor yayi
"Oh Shit! Meyasa Zaka bari tah tafi, Ni ban lura bah"
Yasir ya Bata Fuska Tareda juyawa
"Tho ina Ruwanka dah ita, Pls Kazo mu tafi"
A Sanyaye Suka Shiga motan Suka nufi Cikin Garin Sosai
Sunsha Wahala kamin Su gane Gidan Malamin, duk abinda Yasir keh buk'ata ya samu Sun dade a K'auyen Sannan Suka Nufi Gida..
A kofar gida Sulthana taga Mallan Zaune Yana K'arantar da Almajiransa, Hawayen Idonta ta share Tareda Rusunawa ta gaidashi. Bai amsa bah ya kauda kai, Gidan ta shiga tana cigaba da matsar kwalla. Mama ta gani a tsakar gida tana shan Iska, ta K'arasa ta Tsuguna ta gaidata Sannan ta aje Trayn ta koma Zaure ta zauna. Baffa bai Shigo Gidan bah Sai da Akai Sallan Magriba, Kwala mata kira yayi ta fito daga bayi dasauri Gabanta na dukan Uku uku, Dole yau tasan sai tasha dukan tsiya. Tana xuwa ta tsuguna a gabanshi ta fashe da Kuka Hade rai Yayi
"Mai Akai miki da zaki Hau Kuka, Ina Kudin Gyadan"
K'ara Fashewa da kuka tai Daidai nan Hafsatu ta shigo gidan tana Washe Baki da Ledar Kaza a hannunta. Jin Abinda Baffa yake cewa Yasa Tai Saurin K'arasawa wajan
"Wallahi Baffa K'arya take duk abinda ta fadama, Yarinyan nan Ashe Juye ake Mata. Yaudai Allah ya toni Asirinta na gani da idona wani dan Birni na mik'a mata Bugun Abuja dayawa Wallahi"
Hannu Baffa Ya dagama Hafsatu Alamar tai Shiru Sannan ya Kwalama Mama kira, Duk abinda akeyi tanajinsu banza tai dashi ya gaji da kiranshi ya Kyalle. Rannan Dukan tsiya Sulthana Tasha Abin Tausayi duk Baffa Ya Farfasa mata jiki. Zaure ta koma tai Kukanta mai Isarta Sannan Barci ya dauketa ga yunwa dake damunta..
Bayan Isha'i Wani d'an Yaro Almajiran Baffa ya Shigo da Sallama, Tsugunawa Yayi ya Gaida Mama Yace
"Wani neh a Waje yake Sallama da Ameenatu"
Mama tace
"Kaje kace tana zuwa"
Kwalama Ameenatun Kira Tai ta Fito daga Dakinsu Fuskanta bah Annuri jin Abinda ya Faru da Sulthana bayan ta dawo daga Gidansu Habiba. Mama Da Murnushi a Fuskanta Tace
"Maza kije ana Sallama Dak'e"
Tsaki Ameenatu tai
"Mama fah bai wuce Musa mai Kifi, Nidai Gaskiya bana Sanshi"
Hade Rai Mama tai Rai Bace
"Maza ki dau mayafinki Ki Wuce Kafin Raina ya baci. So kike kita zama a gida Muna K'allanki"
Daki Ta shiga tana Gungunai tadau Hijabinta tasa Ta nufi Zaure tana Turo baki, Sulthana ta gani kwance Tana Barci. Hawaye Suka ciko idonta Ta rintse ido Ta fita dasauri..
Tsaye ta Sameshi jikin wata Hadadiyar Benz, Sanye Yake da T shirt Bak'i da Brown Trouser. Hannunshi d'aya Cikin Aljihu D'ayan Yana Latse Latse a Wayarshi K'irar Samsung Galaxy S7.
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*Page 76 to 80*
Hannunshi D'aya Cikin Aljihu D'ayan Yana Latse Latse a Wayarshi K'irar Samsung Galaxy S7. K'ara Mutsitsika ido tai Tabbas Dr Fareed ne, K'arasawa tai a sanyaye fuskanta dauke da murmushi, Sallama Tamai Ya dago kai Yana K'allanta Sanna Ya amsa.
Wayan ya saka cikin aljihu tadan sauke kai ta gaidashi ya amsa fuska a sake. Shiru ne ya biyo baya nadan wasu seconds, Yadan K'alleta yana Murmushi
"Ya jikin Kanwarki"
Kanta a K'asa tace Dasauk'i. Jim yayi sannan Yace
"Wel Ameena koh?"
Kai da daga mai Alamar eh. Sannan ya cigaba da cewa
"Dalilin Xuwana Shine Gaskiya ni Naga Sisternki Inaso, and so na Gaskiya nake mata, Bansani bah ko Zaki Taimaka min"
Gaban Ameenatu ne keta faduwa jin Maganganun dake Fitowa daga bakinshi, nan da nan gumi ya feso Mata. Jin Shirun yayi yawa yasa yace
"Kina jina?"
Kai ta gyada mai batareda tace komai bah, Hawaye ne Suk'a gangaro mata tai Saurin Kauda kai Sannan Tace
"Bah Komai ai anma bah mamanmu d'aya bah ita mamanta ta rasu"
Cikeda damuwa yace
"Allah ya Jikanta"
Ameen Tace Zuciyarta na Mata zafi, Ji take Kaman ta Fashe da Kuka a Wajan.
Ganin Shirun Yayi yawa yasa Tace
"Zan Shiga Gida, Saidai kai Hakuri dan Ta riga tayi barci"
Murmushi yayi tareda Sah Hannu a Aljihun Shi
"Babu damuwa Zan dawo gobe"
Kudi ya Ciro dayawa ya mik'ama Ameenatu anma tak'i Karba, Saida Ya hadata da Allah Sannan Ta K'arba Tamai Sallama ta Shiga Gida. Kamar Yanda Tabar Sulthana haka ta dawo ta sameta Kudundune tana Barci, Batace komai bah ta Shiga Cikin gida, Dakinsu ta nufa ta fada Kan Gadonsu ta Fashe da Kuka Mai Ban Tausayi.
Damuwa Masroor ya Shiga Tunanin Sulthana ya Hanashi Sukuni, Tunanin Halinda Take Ciki yake tabbas Yasan yarinyan tana cikin Mawuyacin Hali, Duk dah baisan meke faruwa da ita bah. Koda suka isa gida yana gaida Mami ya wuce dakinshi kai tsaye, wanka yayi tareda sallan la'asar ya fada kan gado, hugging pillow yayi yana tuna abinda ya faru dazu. Mikewa yayi dasauri tareda girgixa kai yana cewa
"No bah santa nake bah, Tausayinta neh Kawai"
Wayanshi ne Yayi K'ara Ganin Sunan dake wayo yasa Ya dauka a Sanyaye
"Hello" yace Sannan Yayi Shiru. Chan Yace
"Gani nan zuwa Mami"
Mikewa yayi ya Fita zuwa Falon Ya Fita A Stirs dinda zai Kaishi xuwa part dinsu Mami yaga Mahnoor tana K'okarin Zuwa side dinshi. Murmushi tai Tana Turo baki
"Bro Masroor tunda ka dawo kah daina tayani Assignment, Kuma kah daina Wasa dani"
Hararanta Yayi da Wasa
"Ai na lura neh yanzu bakida Kunya"
Kara Turo baki Tai Sannan Tace
"Mami toh na K'iranka"
Hannunta Ya Rik'e yana cigaba da Tsokanata Har suka K'arasa Side din Mami, Falon K'asa Suka sauko inda Mami ke Zaune tana Rubuce Rubuce a Wasu Takardu. Zama Yayi Sannan Yace
"Mami gani"
Dago Kai tai ta K'alleshi
"Son Yaya dai is anything Wrong"
Yadan Girgiza kai Yana cewa
"Bbu Komai I'm Fine"
Girgiza kai tai na Rashin Fahimta tace
"Shiknan, Pls akwai Mutane a Waje da Suke bukatar temako"
Kudi ta Dauko Bandir Guda Uku Yan Dubu D'aya ta Mik'amai
"Kah Rabamusu"
Girgiza kai Masroor Yayi Yana Y'ar murnushi
"No Mami zan Basu ki Aje Wannan"
Mik'ewa Yayi ya K'alli Mahnoor data Makaleshi Yana cewa
"Tho Sakeni Naje inda aka aikeni koh"
Turo baki tai tana buga k'afa a kasa
"Nidai muje tare"
Baice mata komai bah Ya Haura sama zuwa dakinshi, Bedside drawer'n dakinshi ya bude yadauko kudi Ya fito. Tsaye ya Samu Masroor Tana jiranshi, Hannunshi ta kama suka Fito farfajiyan Gidan. Ma'aikata neh burjik kowa nata aikinshi, Daga K'ai yayi inda Wasu Maza Masu aikin Gidan Ke Wanke Motocin Daddy. Tsayawa yayi chak yana K'allansu, Su sam mah basu lura dashi bah
Hannun Mahnoor Ya saki ya K'arasa Wajan motocin Y'ana K'allan daya daga cikinsu dak'e wanke Taya Yanata Surutu. Duka Sauran Suk'a zube suna Gaidashi, wanda ke Tsugunen Ya Dago Dasauri Suka Hada Ido Nan da Nan Jikinshi Ya soma Rawa Ya duk'ar dakai yana Raba idanu
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*Page 81 to 85*
Duka sauran suka zube Suna Gaidashi, Wanda ke tsugunen ya dago dasauri suka hada ido nan da nan jikinshi ya soma rawa ya Duk'ar dakai yana raba idanu. Bude Baki Masroor Yayi da niyar magana ya fasa, Juyawa yayi yabar wajan dasauri Cikeda Mamakin Ganin Saurayin nan da suk'e tareda marakunyar Yarinyan datamai Fitsara dazu. Kamar yanda Mami ta Umarta haka yayi, duk dunbin Mutanen dake Wajan saida ya raba nusu dubu d'ayi D'ayi Shida Mahnoor Sannan suk'a Shigo Gida, Saurayin nan ya Y'ara bi da K'allo Sannan Ya nufi Side dinshi ta K'ofar Waje...
K'iran Sallan Asubah ne ya tada Sulthana ta Mik'e dakyar saboda yana jikinta ke mata ciwo, cikin gidan ta shiga tai alwala da sauri sauri ta dawo zaure ta shimfida buhu tai Sallah dan tasan dah Baffa ya fito bah lallai baneh ya barta tai sallah, tana idarwa taji k'aran bude kofan Baffa, Saida yayi alwala sannan ya nufo zauren..
Haskata yayi da torch light Ganinta zaune yasa ya bata fuska yace
"Kindai san bah ruwa a rijiya koh, Maza ki tashi duk inda xaki samo ruwa kije ki samo"
Mik'ewa tai da Sauri har Saida tadan saki Y'ar K'ara, nan da nan idonta ya ciko da K'walla, Jikinta duk Ciwo yak'e mata kuma a haka Baffa yace ta dibo Ruwa. Yana Fita ta koma ta zauna ta fashe da kuka a Hankali, Jikinta take Tabawa tana Kuka Sosai, K'ayanta dake Cikin Poly bag ta fara bincikawa, Wani Zani ta Ciro ta rungume ta k'ara Fashewa da kuka tana Turo Baki
"Umma meyasa Zaki tafi ki Barni, Baffa Baya sona. Nima inaso na mutu nazo inda kike"
Kuka take Sosai, sai bataji Zuwan Mama bah sai hasketa da Torchlight datai
"Sulthana Kukan meh Kike"
Mik'ewa tai dasauri ta share Hawayen Fuskanta,
"Babu komai"
Zanin ta mayar inda yake Ta nufi Cikin Gidan, Bokitin K'arfe ta dauka ta Fita. Abinda Ya daure mata kai bai Wuce K'in Amsa gaisuwanta da Ameenatu tayi bah. Haka ta Cigaba da Tafiya tana Mamaki, Duk Gidan Tasan Masu Santa daga Ameenatu sai Mama, Har ta Nufi Rijiyan Burtsasai sai ta tuna Rijiyansu Sadiya bai K'afewa. Murmushi ne Ya subuce mata ta nufi gidan dasauri..
A tsakar gida taga Maman Sadiya da ita sadiyar suna alwala, dagowa sukai tareda amsa sallaman datai cikeda mamakin ganinta a wannan lokacin. Mama na gamawa ta mik'e tace
"Yaki nan Sulthana"
Bokitin ta aje ta k'arasa inda Maman take, Hannunta ta rik'e duka biyu tana haske Jikinta da torchlight, sanin shedan duka yasa ta girgiza kai ta dago ta k'alleta
"Waya dukeki Sulthana"
Shehekan kuka ta soma tana turo baki a hankali
"Baffa neh ya dukeni jiya"
Sadiya ta k'araso wajan itama fuskanta bah walwala
"Sulthana me kika fito yi da asubah"
Bokitin data aje ta k'alla
"Koba Baffa baneh yace naje na dibo ruwa"
Girgiza kai Mama tai cikeda takaicin Hali irin nah Mallan Jamilu, Bokitin ta dauka da k'anta ta diban mata tareda daurata akai ta tafi gida. Sahu tai Yakai Goma daga Gidansu zuwa gidansu Sadiya, Duk sanda taje Mama je diban mata ta kuma Daurata ta nufo Gida. Ana K'arshen Mama ta zaunar da ita taci abinci ta Koshi sannan ta nufi gida Cik'eda murna..
Yauma gyadar ta dafa K'amar kullum, A tray ta juye Tana kici kicin dauka, Ameenatu ce ta shigo cikin gidan da sallama hannunta dauke da leda da alama daga aike take, K'allanta tai tana d'an murmushi
"Yaya Ameenatu dazu na Gaisheki baki amsa bah, Koh baki ji baneh"
Harara Ameenatu ta wurga mata tareda kauda kai, Mamaki sosai Sulthana har ta k'asa boyewa
"Yaya Ameenatu menai miki, dan Allah kiyi hakuri"
Tsaki Ameenatu tai tana nunata da D'an Yatsa
"Keh karna k'arajin kin kira. Sunanan a gidan nan idan bah haka bah wallahi zaki sani"
Bata jira mai Sulthana zatace bah ta bar wajan tana tsaki, hawaye ne masu zafi suka gangaro mata
"Shiknan Ameenatu ta daina santa, yanzu ina zata waiga taji sanyi"
Durkushewa tai ta fashe da kuka mara sauti, Jin k'amar sheshekan kuka yasa Mama ta fito dan ko ba'a fada mata bah tasan Sulthana neh. Durkushe ta sameta gaban Gyadan,
"Sulthana kedai kuka bai miki wuya, mai makon kizo ki gayamin ai dana dauraki"
Mik'ewa Sulthanan tai Mama ta daura mata gyadan tareda mata Kashedin K'arta kula maza, Sannan idan har tasan maza na mata juye tho ta daina. Tho kawai tace ta fita zuwa Bakin kasuwa inda ta daba Zama. Tana Cikin Tafiya taji ta bayanta ana Cewa
"Sulthana bako gaisuwa"
Juyawa tai dasauri, K'allanshi ta tsaya yi nadan Wasu Seconds. Ganin bata ganeshi bah yasa yayi murnushi ya k'araso inda take Tsaye
"Baki ganeni bah koh"
Kai ta gyada mai batareda tace komai bah...
Murmushi ya K'arayi yana k'allanta
"Nine likitan dana dubaki ranan a Chemist"
Sai a sannan ta tuna, idanunta ta sauk'e k'asa tace
"Ina Wuni"
Amsawa yayi yana Mata murmushi, Ganin Tana kokarin tafiya yasa yasha gabanta dasauri
"Ina zaki bamu gama magana bah"
Turo baki tai idonta ya ciko da Kwalla
"Dan Allah kaban hanya na wuce"
Ganin yanda Hawaye ke gangarowa a idonta yasa ya matsa jiki a sanyaye ta wuce, Binta da K'allo yayi harta bace ma ganinshi. Ajiyan zuciya ya sauke, Zuciyarshi ta shiga raya mishi
"Yarinyan nan tana cikin Damuwa"
Kamar zai bita ya Fasa ya shiga mota ya nufi Cikin Garin Kano...
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*Page 91 to 95*
Turo baki Masroor yayi ya mik'e yabar Dinning din
Girgiza kai Mami tai
"Ai kai bakasan Maganan aure"
Mik'ewa Daddy yayi
"Zan Tafi Office daga nan zanje Meeting da Party chairman"
Fatan Alheri Mami tai mai ya fito bodyguards dinshi suk'a budemai Kofan mota ya shiga, Driver yaja Sukabar Gidan Tareda Suran Bodygyards din da Suke a wata motar daban..
Kamar Jiya yauma Bakin K'asuwar Masroor yazo anma baiga Sulthana bah, yaranda ke wajan ya tambayan sukace mai bata zo bah. Hankalinshi ne ya tashi, motarshi ya shiga ya shiga cikin kauyen, duk inda ya kutsa da mota K'allanshi ake bama kaman mata. Tsaki yayi ya kauda kai ya cigaba da driving, ya dad'e yana kewaye Garin kafin ya koma gidah ranshi babu dadi..
Sulthana kuwa tana dauk'ar tallanta tasha ta nufa dan ma k'artaga Wannan dan Birnin, Batako dad'e bah ta saida Gyadarta ta dawo gida cikeda Farinciki. Abu guda keci mata tuwo a kwarya rashin Sake fuska da Ameenatu batamata yanzu, Hakan yasa ta yanke hukuncin ta sameta taji koh wani laifin tai mata. Tana zaune Zaure Baffa ya fita wajan Almajiranshi, tana ganin ya fita ta mik'e ta shiga cikin Gidan, Dakinsu Ameenatun tai Sallama ta Shiga, Kwance ta samu Ameenatun akan Sallaya. Jin muryan Sulthana yasa ta mik'e zaune
"Keh Wacce irin Dabba ce idan anyi Sallama bah bari ake sai mutum yace a shigo bah"
Dagowa Sulthana tai dasauri tana K'allan Ameenatu da mamaki, tunda take da Ameenatu bata taba mata Fada bah sai yau. Idonta neh ya ciko da K'walla ta zauna dabar a Kasa tana k'allan Ameenan daketa cika tana batsewa
"Yaya Ameenatu mai nai miki kike fushi dani, idan namiki magana bakya amsa min"
Mik'ewa Ameenatu tai tana nuna mata k'ofa
"Fita daga dakin nan ko yanzu nai miki dukan tsiya, dah ina ganin laifin Baffa dayake azaptar dake ashe ko da Gaskiyar sa"
Kuka Sulthana ta fashe dashi
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi haquri idan na miki laifi bazan sake bah"
Mari mai rai da Lapia Ameenatu ta dauke Sulthana dashi
"Zaki fita koh saina babbala ki"
Dagudu ta fita ta nufi zaure tana cigaba da kuka, kukanta neh ya fitoda Mama daga daki
"Lapia meke Faruwa Sulthana"
Lekowa cikin gidan tai ta zube gaban Mama tana cigaba da Kuka, Dagota tai tsaye
"Yi Shitu fadamin menene"
Tsagaita kukan tai
"Yaya Ameenatu ne ta mareni bansan menai mata bah"
Da mamaki Mama tace
"Mari?"
Kai Sulthana ta gyada tana cigaba da kuka, Lallashinta Mama tai dakyar tai shiru ta koma zaure ta zauna tareda hade kai da Guyiwa...
Mama ta kwalama Ameenatu kira ta fito tana gungunai,
"Haba Ameenatu mai Sulthana tai miki da zaki mareta, ki tuna fah keh kadai take rab'a tanajin dadi"
Tsaki Ameenatu tai tareda kauda kai
"Mama ni yanzu kawai naji na tsani Sulthana"
Da mamaki Mama ta K'alleta baki bude
"Kinko san Abinda kike fada Ameenatu"
Gyada kai Tai tareda barin Wajan, Abin ya dad'e yanaba Mama mamaki, Tabbas akwai wani abu da Ameenatu ke boyewa..
Bayan isha'i Sulthana na Kwance Yaro ya shigo zauren harda zai shiga cikin Gidan Ya dawo inda tak'e Kwance
"Sulthana ana sallama dake a Waje"
Mik'ewa zaune tai dasauri tareda zaro ido
"Wanene?"
Girgiza kai yaron yayi
"Bansan waye bah, Wani ne dai a mota"
Zazzaro ido take cikeda tsoro, Kaje kace bana nan. D'an jim Yaran yayi sannan yace
"Jiya yazo wajan yaya Ameenatu kila sako zai baki ki kai mata"
Jin haka yasa ta mik'e tadau dankwalinta ta daura ta fito kofar gidan. Zaune yake cikin mota yana latse latse a wayanshi, k'arasawa tayi bakin Motan cikin muryanta mai Sanyi tace
"Ina Yini"
Dagowa yayi ya k'alleta da Murnushi kwance kan Fuskanshi
"Lapia lau Sulthana, Ya gida"
Lapia tace a takaice..
Fitowa yayi daga cikin motan ya tsaya, shiru ne ya biyo baya nadan mintina Sannan ya dago ya K'alleta kanta a k'asa yace
"Sulthana"
Dagowa tai tadan K'alleshi sannan ta maida kai tace
"Na'am"
Ajiyan zuciya ya sauke yace
"Shekaranki nawa?"
Dan Jim tai kamar karta fadamai sai kuma ta dan dago batareda ta kalleshi bah tace
"Sha hudu"
Jinjina kai yayi yace
"Ajinki nawa a makaranta"
K'ara dago kai tai ta K'alleshi tareda girgixa kai
"Bana zuwa makaranta"
Kallanta yayi da Mamaki
"Meyasa?"
Kauda kai tai tareda turo Baki
"Baffa ya cireni"
Kallanta ya tsaya yi, Abinda ya fahimta da Yarinyan shine tana fuskantan kiyaiya a gidan zai iya cewa wajan kishiyar mahaifiyarta kuma abinda ya burgeshi da ita sam batasan wani bare yasan halinda take ciki.
Hakan ya burgeshi sosai, Muryanta yaji tana cewa zan shiga gida kada Baffa ya fito ya ganni. Bata jira mai zaice bah tabar wajan ta shiga cikin gida. Kurri yana kofar gidan, tausayin Sulthana ke ratsa shi. Runtse ido yayi ya bude a hankali yace
"Ina sanki Sulthana, zan iyayin komai a kanki. Insha Allahu zaki fita daga k'angin da kike ciki kwanan nan"
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*Page 86 to 90*
"Yarinyan nan tana cikin damuwa"
Kamar zai bita ya fasa ya shiga mota ya nufi Cikin garin kano. Zama tai Bakin Bishiyan Data saba Zama, Gyadan ta soma saidawa kamar yanda ta Saba. Atika dake kusa da ita tana saida Rogo ta yafici Ladi tana nuna mata wata hadaddiyar mota