Showing 15001 words to 18000 words out of 44304 words

Chapter 6 - SULTHANA complete Hausa Novel

25 Jul 2025

1433

datazo wucewa
"Kai Ladi ji Wachan motan, Tafdi! Ni tunda nake ban taba ganin mota mai sama a bude bah"
Kyalkyacewa da dariya ladi tai tana tafawa
"Kai Wallah Motan nan Akwai Kyau, Allah ka bamu irin wanna motan"
Jin Yanda suke zuzuta motan yasa Sulthana ta dago ta K'alli motan, Lallai kuwa motan yanada Kyau, Murmushi ta soma tanabin Motar da K'allo. Duk mutanen dake K'asuwan kowa bin motar yake da K'allo cikeda Sha'awa, Wanda ta gani Cikin motan neh yasa Fara'ar dake Fuskanta yakau, Hijabin Fuskanta ta Turo Gaba ta Rufe Fuskanta dashi..

Zagaye yake yana yatsine Fuska, Waje ya samu yayi Parking Sannan ta fito. Mata sa binshi da K'allo suke harda Mazan, Dan D'an gayu neh na K'arshe. duk gungun Yara masu talla daya gani sai ya tambaya tareda Fadin sunanta anma duk suce basu santa bah, Ganin Yana Kokarin nufosu yasa Sulthana ta mik'e tana K'okarin daukan trayn Gyadan tah k'araf suka hada ido, Dauke kai tai Ta dauki Trayn Gyadan ta Fara tafiya. Binta Yayi tateda Kiran sunanta, Juyowa tai ta Murguda mai Baki
"Kah daina kiran sunana kuma ka daina bina"
Murmushi Yayi yanda ta murguda bakin Saita k'ara mai kyau
"Meyasa zakice na daina binki"
Batareda ta juyoba tace
"Nidai Dan Allah ka daina bina kada Yaya hafsatu ta ganmu taje ta fadama Baffa, Idan ta fadama Baffa dukana zeyi, Jiyama saida ya dakeni"

Tausayi ta bashi Ya sha gabanta yana K'allanta
"Kiyi Hakuri nasan mu muka ja miki dukah koh"
Batace mai komai bah tana k'okarin tafiya, hannu ya daga mata Yana cewa
"Tsaya mana, kudinki na jiya nakeso na Baki"
Kauda kai tai gefe
"Kah barshi, nidai dan Allah ka bani Hanya na Wuce"
Matsa mata Yayi ta soma Tafiya Yana K'allanta, meya tuna ya bita da Sauri tareda shan gabanta
"Tsaya tho kiji"
Tsayawa tai hannunta d'aya a kugu
"Inaso gobe mu hadu a Inda kike saida Gyada kamar wannan lokacin kinji"
Batacemai Komai bah ta cigaba da tafiya abinta. Binta yayi da K'allan tausayi, A Ranshi Yana raya
"She's Cute n Young, She need help. No matter how Zaki Kasance Cikin Farinciki nan daba"

Motarshi ya nufa dan komawa gida, Yara ya gani Yayyabe da Motan Sunata Shafawa, K'arasawa yayi dasauri ya koresu. Ganin Sunki Tafiya yasa ya Dauko bandir din yan Hamshin ya soma Raba Musu, ai a nan yaga wawaso harda manya. Tausayama Halinda yan K'auyen suke ciki yayi. Motan ya shiga ya tada Yabar kauyen Cikeda Tausayin Sulthana...

Gida Ya nufa Kai Tsaye, Horn yayi masu Gadi Suk'a budemai kofa, Saida yayi Parking Sannan ya Fito. Bodyguards din dadd ya gani a tsakar gidan, Murmushi Yayi
"Wel daddy is back"
Main palour ya nufa tareda Danna Bell, wata mai Aiki ce ta bude Tareda Zubewata gaidashi, Bai amsa bah ya Shiga falon Yana Fara'a Baiga kowa A falon bah. Wani Corridor ya nufa wanda zai sadashi dah Dinning area, a nan ya gansu zazzaune suna Lunch. Sallama yayi ya k'arasa ya rungume Daddy Yana dariya,
"I Missed uh Daddy"
Murmushi Daddy yayi Yana Shafa Kanshi cikeda Zolaya Yace
"Sai Kace nayi shekara kwana biyu fah nai"

Turo baki Mahnoor tai tareda Rungume Hannayenta
"Daddy kacema Bro Masroor ya daina Rungumeka shi babba neh"
Zama Masroor yayi akan Kujera suka fashe da Dariya duka, Hararanta yayi
"Lallai baki isah bah, Ai daddy nane"
Idonta ne ya ciko da K'walla ta kara hade rai tace
"Daddy na dai"
K'ara Fashewa da dariya sukai duka. Ganin Sunata mata dariya yasa ta fashe da kuka ta mik'e Tabar wajan tana kuka..

Hararan Masroor Daddy yayi
"Kaga kah koranmin Baby koh, Tho Maza ka tashi ka Lallasheta ta dawo taci abinci"
Turo baki Masroor Yayi yana Kai Loman Abinci
"Daddy kah kyaleta cikin wah Bah nata bah, Karta Cin"
Lekowa Mahnoor tai Tana Share kwalla
"Baza'a kyaleni din bah."
Guntse Dariya Mami da Daddy sukai dan Yanzu sunayi zasu takalo Rigima..

Rungume Mami tai ta Baya ta shagwabe Fuska
"Mami yanzu bro Masroor baya sona, Bro Yasir ne kawai ke Sona"
Cup din Juice Masroor ya dauka ya kora Sannan ya aje Yana cewa
"Kedai kika sani"
"Ahan ina Kaje dazo baka fadama Yasir bah, yazo nemanka neh kuma nasan din inda zaka tare kuke zuwa"
D'an jim yayi sannan yace
"Eh wannan fitan ni kadai neh, Banda Shi"
Murmushi Daddy yayi cikeda Nishadi
"Koh anje Wajan Sirikan nawa neh"
Suman Kanshi Ya Shafa Yana Y'ar Dariya.
"Aa Daddy"

Mami Itama Dariyan tai
"Ai dama bazaka fada bah, tho bari kaji gwara fa kama fada tun yanzu coz ana gama Hayaniyar siyasan nan Zamuje neman aure"
Turo Baki Masroor Yayi ya mik'e yabar Dinning din...

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 96 to 100*

"Ina sanki Sulthana, zan iyayin komai a kanki. Insha Allahu zaki fita daga k'angin fa kike ciki kwanan nan"
Motanshi ya shiga yabar wajan cikeda tausayin halinda Sulthana take ciki.

Da zazzabi Sulthana ta tashi da asubah, dakyar ta iya mik'ewa ta fito tsakar gidan. Alwala tai ta koma zaure tai Sallah, Tana zaune Baffa ya fito ya tafi masallaci. Kasa shiga tai aikin data saba tayi a cikin gidan har wuraren k'arfe bakwai da rabi, Ameenatu ce ta fara fitowa daga daki ganin ko'ina batsa batsa yasa ta nufi zaure a fusace. Kwance ta sameta tanata rawar sanyi, tsaki Ameenatu tai tana magana cikin daga murya
"Wato dan kin raina mutane yau bazaki je kiyi aikinki bah. Uban wa kikeso ya miki shara da wanke wanke"
d'an dagowa Sulthana tai hawaye na gangarowa a idonta
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi hakuri banida lapia neh"
Duka takai mata dai dai nan Hafsatu ta k'araso wajan tana Murmushin Mugunta
"A'a yaya Ameenatu yau kuma Y'ar son ake duka"

Tsaki Ameenatu ta k'arayi tana nuna Sulthana da yatsa
"Wallahi idan baki tashi kinyi aikin daya kamata bah sai na miki dukan tsiya"
Kallanta hafsatu tai da mamaki, Yau kuma Ameenatu kecewa zata duki Sulthana, Lallai abin babba neh.
Kasa tashi Sulthana tai sai kuka datake Mara sauti, dakyar ta mik'e ta zauna tana k'allan Ameenatu data hada girar sama data k'asa
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi Hakuri"
Ai kamar zugata take nan da nan ta rufeta da duka, Hafsatu taga bati itama ta tayata. Bah abinda Sulthana take in banda ihu. Ihunta ya fito da Mama ta K'araso wajan dasauri..

Dakyar ta kwace Sulthana a hannunsu a fusace tace
"Wannan wanne irin iskanci meh Ameenatu, wai meke daunki me? Metai muku kuke dukanta haka kamar Allah ya aiko ku"
Ameenatu ta hade rai tana huci
"Dan wulakanci tun dazu yarinyan nan batai aikin gida bah, jibi gidan nan sannan ina mata magana tana cemin wani batada lapia"
K'allan Ameenatu Mama ta tsaya yi
"Lallai Ameenatu baiwarki ce ita da zakice dole sai tamiki aiki, ai rashin lapia ya wuce komai sai kuyi mata uzuri"
Hafsatu ta chuno baki
"Haba Mama ke kullum sai ki rinka hana ana hukunta yarinyan nan, Gaskiya..
Saukan Mari Hafsatu taji a fuskanta, a fusace Mama tace
"Wallahi ki kiyayeni Hafsatu, na lura abubuwanki nema suke su wuce wuri"
Nunasu da dan Yatsa tayi tana cewa
"Tho bari kuje, daga yau Sulthana bazata k'ara aikin gidan nan bah ku zakuyi. Meye ku anfanin ku"
Baffa ne ya bankado kyauren gidan ya shigo jin hayaniya, cirko cirko ya samesu a tsaye sai Sulthana dake Zaune a kasa tana kuka duk jini a hancinta da baki..

"Lapia??" Baffa ya tambayi Mama, Hafsatu ce ta koromai bayanin duk abinda ya faru. Nan ko Baffa yahau sababi ta inda yake shiga batanan yake fita bah, Ameenatu ta kalla yana cewa
"Ku cigaba da dukanta ai wannan ma iskanci neh"
Hafsatu ce ta cigaba da dukanta Mama na tsaye tana k'allan Baffa cikeda takaici, batace komai bah ta koma dakinta ranta bace. Itama Ameenatu daki ta koma a fusace, ligi ligi Hafsatu taima Sulthana Baffa na Tsaye. Saida ta duketa san rai Sannan ta kyalleta, Sannan Baffa yasata tai duk aikin Gidan yana Tsaye. Tanayi tana kuka dakyar tai aikin ta gama ta koma zaure ta zauna ta cigaba da kukanta..

Nan da nan wani sabon Zazzabin ya rufeta. Ana Sallan Azahar Baffa ya kwalla mata kira, ta nufi Cikin gidan dasauri, gyada ya mik'a mata. Ta amsa dasauri ta hau wankewa, tana gamawa ta daura a wuta ta zauna bakin murhun ko sanyin datake ji zai ragu. Bata gama bah sai bayan La'asar sannan tadau Gyadan ta nufi bakin kasuwa. Inda ta saba zama ta aje gyadan, zama tai ta hada kanta da guiwa ta fashe da wani sabon kukan, murya taji a kusada ita mai sanyi yana cewa
"Meke damunki Sulthana whats wrong"
Dago runanun idanunta tai duk a tunaninta likitan nan neh, Ganin Masroor yasa ta maida fuskanta ta cigaba da kuka. Runtse ido Masroor yayi ya dunkule Hannayenshi, jin kukanta yake har cikin Ranshi nan da nan shima idanunshi suka chanza launi..

"Sulthana, meke damunki? Tel me pls"
Dago kai tai tana turo baki, ganin yanda take karkarwa yasa ya mik'e dasauri
"Sulthana are you sick?"
Dauke kai tai tana cigaba da turo baki, dakyar ta iya mai magana shima tanayi hakoranta na karo da juna
"Nidai ka daina zuwa inda make, idan Yaya hafsatu taganni zata fadama Baffa kuma dukana zaiyi"
Tsugunawa yayi gabanta cikeda damuwa
"Sulthana fadamin meke damunki, nasan kina cikin damuwa. Me hafsat take miki itada Baffa"
Mik'ewa tai dasauri tana k'akabe Riganta, trayn gyadan ta sunkuya zata dauka yayi saurin rik'ewa
"Please Sulthana ki tsaya ki saurareni, Am here to help uh. Taimakonki zanyi, ki fadamin ko menene nikuma na miki alkawarin zan kawo karshen koma menene"
Tsayawa tai ta tana K'allanshi da Alamar mamaki...

Tho fah ga *Doctor Fareed* Ga *Masroor*
Shin Fans wah kuka zabarma Sulthana ya taimaka mata?? Nidai nace......

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 101 to 105*

Tsaya tai tana K'allanshi da Alamar mamaki. kai ya gyada mata
"I mean what I said"
Sai a Sannan ya K'alleta da kyau, a rudeyace
"Sulthana maiya sameki a fuska? Wayaji miki ciwo?"
Shafa wajan tai, batace komai bah
Trayn Gyadanta ta fuzge ta daura akai ta soma tafiya. Binta yayi yana mata magana anma ko sauraranshi batai bah tayi tafiyarta. Ranar Sulthana batai ciniki nah hakanan ta koma gida, Duka kuwa saida tasha shi Wajan Baffa. Haka tai kukanta ta gaji ta kwanta, yauma k'amar jiya Yaro ya shigo yace Ana Sallama da ita, turo baki tai tacema yaron yace bazata zo bah haka koh akai, Yaron ya koma yagayama Fareeed Sakon da Sulthana ta bashi..

Baice komai bah ya bude mota ya dauko wani k'aton leda, yaron ya mik'ama wah
"Dan Allah gashi ka kai mata kaji"
Hannu Yasa a Aljihu ya ciro dubu daya ya mik'a ma Yaran
"kai kuma ga naka"
Washe baki Almajirin yayi tareda godiya, ledan ya shiga dashi cikin zauren ya bah Sulthana, zaro ido tai tana k'allan almajirin
"Dan Allah ka maidan mai kada Baffa ya gani kace nace banaso"
Niki niki yaron yadau leda ya koma dashi, yana fita yaga wayam bah motan Dr Fareed. Dawowa yayi ya shaida mata ya aje ledan ya fita, jikinta neh ya soma rawa yanzu idan Baffa yaga ledan nan tasan duka zataci. Sadiya ce ta fado mata a rai ta dau ledan dakyar ta nufi gidansu sadiya cikeda Fargaba..

Da sallama ta shiga Allah ya taimaketa Baban Sadiya baya nan, saida ta gaida Maman Sadiya sannan ta zaiyana mata duk abinda ke Faruwa, ga mamakinta sai gani tai Maman Sadiya ta washe Baki.
"A'a Sulthana wannan ai abin farinciki neh"
Hannu ta daga ta godema Allah sannan ta k'alli Sulthanan data sake baki tana k'allan Mama
"Ina tayaki murna Sultana, insha Allahu komai ya kusa zuwa karshe. Ni nasan wannan likitan sanki yake"
Gwalalo ido Sultana tai idanunta suk'a ciko da kwalla, Mama ta cigaba da cewa
"Kinga idan kikai aure komai zai zamo tarihi, zaki fita daga cikin wannan wahalan da kike ciki"
Rufe fuska Sulthana tai tana murmushi. Rungumeta Sadiya tai tana cewa
"Iyeh! Amarya"
Dukan wasa Sulthana takai ma Sadiya, kyalkyalewa da dariya Sadiya tai cikeda farinciki.

Mik'ama Mama ledan tai tareda mik'ewa
"Mama idan Baffa yaga wannan kayan dukana zeyi"
Amsan kayan Mama tayi ta hau dubawa, Hadaddun kayane kala kala. Dogayen riguna, Atamfofi da lesuka ready maid. Sai takalma da turaruka. Sakin baki sadiya tai
"Tab ni ban taba ganin irin wannan kayan bah"
Tabe baki Sulthana tai
"Mama kiyi anfani dasu keda Sadiya"
Dago kai Mama tai tana k'allanta, girgiza mata kai tai
"A'a bazamuyi anfani dashi bah Sulthana, na miki alkawarin zan aje miki su har lokacin da kika bukata"
Girgiza kai Sulthana tai tana cewa
"A'a kiyi anfani dasu"
Tsofafin Silifas dinta wari daban daban tasa tace
"Mama na tafi kada Baffa ya fito bai ganni bah"
Sallama Mama tai mata Suka fito tareda Sadiya, kara kyalkyalewa da dariya Sadiya tai
"Amarya knan"
Duka Sulthana ta d'aka mata tana hararanta
"Banaso fah"
Murmushi Sadiya ta rik'e haba tace
"Niko inasan naga wannan saurayin d'an birni"
Turo baki Sulthana tayi tana yatsine Fuska
"Nidai bana sansa"
Sakin baki Sadiya tai batace komai bah, a haka sukai sallama Sulthana ta nufo gida dasauri...

A kofar gidansu taga Ahmad saurayin Hafsatu, K'allanshi tayi da nufin gaidashi ganin ya balla mata harara yasa sum sum ta shiga Gida, kan buhunta ta zauna tai shiru. Haskota akai da torchlight ta mik'e dasauri muryan Hafsatu taji tana cewa
"Gatanan ta dawo"
Gabanta ne ya fadi Dam! Shiknan yau tasan nata ya K'are..

Baffa ne ya kwalla mata kira ta amsa ta shiga cikin gidan jikinta na rawa, Cirko cirko ta samesu a tsakar gidan, Ameenatu sai Balla mata harara take. Tsugunawa tai Sannan tace gani.
Baffa rai bace yace
"Waye Saurayin nan da hafsatu taganku dashi Ranan"
Gaban Sulthana ne ya fadi
Daka mata tsawa Baffa yayi
"Badake nake magana bah"
Muryanta na rawa tace
"Baffa wallahi ban sanshi bah, ranan kudin gyada na zai bani"
Mari Baffa ya dauketa dashi yana huci
"Bazaki fadamin Gaskiya bah"
Kuka Sulthana ta fashe dashi ta soma Rantse rantse
"Wallahi Baffa bansanshi bah"
Ameenatu ce ta amshe da cewa
"Karya kikeyi, wato Sulthana kin Fara kula kulan maza koh? Ai dama tunda naga wannan likitan nasan dan iska neh"
Sai a sannan Sulthana ta gane inda maganansu ta dosa
Daki Baffa ya shiga ya dauko Bulala, Sulthana na ganin haka ta kwala ihu tana kuka sosai

"Dan Allah Baffa kai hakuri Wallahi bansanshi bah"
Hafsatu tace
"Rannan Ahmad yake gayamin ya ganshi, kyaleta nai kawai ban fadaba sai yau kuma ni da idona naganshi Yazo yaba wani yaro katon leda ya kawo mata, shiyasa dana tambayi Mama sulthana ta kawo mata leda tace wani leda"
Tsula mata bulala Baffa yayi ta saki ihu ta fashe da kuka. Tana kururuwa
"Dan Allah Baffa kai hakuri bazan Sake bah"
K'asa magana Mama tai ta koma daki abinda cikeda bakin ciki
Saida Baffa yaga bata numfashi Sannan ya kyalleta Sukai shigewansu daki suka barta nan warwas a tsakar gidan...

Mamace ta fito jin sun shige daki, kuka ta fashe dashi mara sauti ganin Sulthana kwance. Daki ta koma ta debo ruwa ta yayafa mata, ajiyan zuciya tai ta K'ara fashewa da kuka tana ihu
"Baffa kai hakuri, Wayyo baffa zai kasheni. Yaya Ameenatu ki taimakeni"
Saurin rufe mata baki Mama tai itama tana kukan, Dakinta ta kaita ta dawo ta hada wuta ta daura mata ruwan wanka, ruwan na zafi ta surka ta kai mata ban daki. Da taimakon Mama tai wanka, nan da nan Zazzabi ya rufeta, magani Mama ta bata tasha Barci mai nauyi ya dauketa. Sai gaf da Asubah Mama ta tasheta ta koma zaure gudun kar Baffa yazo fita massalaci bai ganta bah...

A Bangaren Masroor kuwa koda ya koma gida kasa sukuni yayi, Falon k'asa ya zauna yayi shiru, Mami ce ta sauke zuwa falon ganin Masroor zaune ya k'urama tv ido anma daga gani hankalinshi ba'a tv take bah. Zama tai kusa dashi tadan Tabashi, Razana yayi ya juya ganin Mami yasa ya saki ajiyan zuciya.
"Lapia Meke damunka son" cewar Mami
D'an Murmushi yayi yana girgiza kai
"Nothing Mom"
Kauda kai Mami tai gefe fuskanta bah Walwala
"Masroor bakada kamana, ni yakamata ka fadama damuwanka."
Sumar kanshi daketa kyalli ya shafa yana y'ar Murmushi
"Mami bah komai karki damu"
Bell aka danna, Cikin Maid din gidan ta shigo dasauri ta bude kofan, Mahnoor ce ta shigo dagudu ta wurgama Maid din jakan Makarantan tah tana Murmushi
"Mamina I'm back"
Ganin Mami yasa ta nufeta dagudu ta rungumeta tana dariya
"I Missed you Mami"
Masroor ta k'alla taga sai hararanta yake..

chuno baki tayi
"Mami wai meyasa ya Masroor sai ya rinka eyeing dina"
Sumar kanshi ya shafa
"Mami K'arya take"
Hararanshi Mami tayi
"Banasan Haka fah, ka daina hararan min Y'a"
Baice komai bah yabar Falon..

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 106 to 110*

*Masoya Littafin Sulthana naga sakonin ku da dama wasu ban samu na karanta bah. Abinda nikeso ku gane a nan shine* _labarin Sulthana ya faru ne dagaske_ *So duk abinda kuka gani a ciki bah k'irkira nai bah abu ne daya faru dagske. Sannan Fans din Masroor da na Dr Fareed kowacce tasa ido taga Yadda labarin zai k'arke, yanda yazo a labari hakan zan baku a rubuce insha Allah. Ina fatan zaku fahimceni*..

Wannan Shafin Naku neh *Sulthana Fans* Allah yabar k'auna

Hararanshi Mami tayi
"Banasan haka fah, ka daina hararan min y'a"
Baice komai bah yabar falon. Bell aka k'ara dannawa Maid ta fito dasauri ta bude kofan, Yasir neh ya shigo da sallama ya karasa inda Mami ke zaune ya tsuguna har K'asa ya daidata. Da fara'a a fuskanta ta amsa tareda tambayanshi mutan gidan, ya amsa mata da lapia lau. Mutum nashi ya tambaya Mahnoor ta fadamai yana daki, mik'ewa yayi ya hau sama ya nufi side din Masroor..

Kwance ya sameshi kan Three seater cikin hadadden Falon shi yana k'allan celien, Zama yayi k'an 1seater kusa dashi tareda dafashi
"Friend its anything wrong"
K'akaro murmushi Masroor yayi yana k'allanshi
"No I'm fine"
Ajiyan zuciya Yasir ya sauke harya bude baki zaiyi magana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login