Showing 39001 words to 42000 words out of 44304 words

Chapter 14 - SULTHANA complete Hausa Novel

25 Jul 2025

1436

Mamakin yanda ya amsa mata gaisuwan. Kujera Mahnoor taja mata ta zauna Sannan ta soma serving dinta.. Ganin tak'i sakin jiki taci abincin yasa Abba ya tashi yamusu sallama yabar Wajan..

Itama Mami ta mik'e tana cewa

"Ina zuwa"

Ganin haka yasa Masroor d'aukan plate dinda ke Gabanshi yabar wajan. Sai a sannan ta kalli Mahnoor idanunta taf da hawaye tace...


Ummy Abduol✍🏻Abduol✍🏻

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 197*


Gudu yake sosai yabi ta bayan gidan inda zai sadashi da filin basket ball. Ganin tuk'in nashi bana hankali baneh yasa Sulthana k'ara fashewa da kuka

"Dan Allah ya Masroor kayi hakuri ka daina gudu"

Wani wawan burku yaja ya juyo yana k'allanta idanunshi a rune

"Sulthana bakya sona ko? Fareed kikeso?"

Batace komai bah k'anta a kasa, fita yayi daga motan ya jingina yasa hannayenshi a aljihu ranshi a b'ace. Tana ganin haka tafito jikinta na rawa ta tsugnna gabanshi kanta a k'asa

"Kayi hakuri ya Masroor, ya fareed na d'aukeshi yayana saboda shiya taimakeni. Ban tab'a sanshi bah kuma bai tab'a cemin yana sona bah"

D'agota yayo daga tsugunnen datake ya tallafo fuskanta suna kallan juna

"Ina Sanki Beauty, ina sanki sosai. Pls ki soni kar sanki yasa na shiga wani hali"

Rungumeshi tayi ta fashe da kuka, a hankali tace

"I love uh to ya Masroor"

D'agota yayi daga jikinshi ya kura mata manyan idanunshi da Mamaki

"What do uh just say"

D'an Murmushi tayi tasa hannu tana share hawayen fuskanta. Da lebbunanta ta furta

"I lav uh"

Tsalld yayi yace

"Woaw!"

Ta kyalkyace da dariya tana kallanshi. Motar Fareed neh tazo wucewa ganinsu awajan yasa yayi parking dan yau ji yake saidai duk abinda zai faru ya faru..

Parking yayi ya fito ya karaso inda suk'e tsaye, Masroor na ganinshi ya had'e rai ya juya ya kalli Sulthana yana cewa

"Shiga mota ki jirani"

Bah musu ta bud'e kofan tana kokarin shiga Fareed yayi maza ya k'ama hannunta, a tsorace ta juyo ta kalleshi. Masroor ya fizge hannunta daga nashi yana huci

"Fareed ka kiyayi kanka, meyasa kake kokarin shiga hurumin daba naka bah"

A hasale Fareed yace

"Hurumin daba nawaba ko hurumin daba naka bah"

Ya kalli Sulthana suka hada ido yace

"Tun ranar da Yayarki ta kawoki chemist din kauyenku Allah ya d'auramin Sanki. Nayita k'okarin in sanar dake ban samu daman hakan bah. Naje neman aurenki wajan Mallan anma yacemin an miki miji. Bayan kin dawo gurina inata kokarin na sanar dake abin yacitira"

Ya d'ago yana kallanta

"Ina matuk'ar sanki Sulthana. Na dad'e ina dakon soyaiyarki a zuciyana"

Fashewa tayi da kuka ta fadi a wurin zaune tana kuka sosai, harga Allah bata tab'a zatan Ya Fareed zai Furta Mata Kalmar so bah.
K'arasowa wajan Masroor yayi yana huci

"Fareed kana b'ata lokacin ka neh a banza, karka taba tunanin Sulthana a matsayin matarka. Na fada zan kuma k'ara fada Sulthana Tawa ce!"

Bai ankara bah yaci Fareed ya kai mai wani mugun naushi a baki nan da nan bakin ya fara jini, Fadane Sosai ya kaure tsakaninsu, Sulthana ta mik'e dasauri tana kuka ta shiga tsakiyarsu

"Ku daina fada d'an Allah"

Ta juya ta kalli Fareed dashima gefen idonshi ke jini tace

"Ya fareed ku daina fada, indai saboda nine na hakura banayi"

Ai kamar k'ara zuga Fareed take ya wawuri Masroor ya soma kaimai nushi, Shiko Masroor kasa dukanshi yayi dan sam baiso hakan ta faru tsakaninsu bah. Ganin Fareed na neman halakashi yasa shima ya fara maida Martani, dukan juna suke bana wasa bah Sulthana na gefensu tana kuka da ihu dan neman agaji. Daidai nan mottocin su Mami suka k'araso wajan a guje dan tun dazu bayan fitansu Mahnoor ta sanar da Mami abinda ke faruwa. Yawo suketayi har Allah yasa suka biyo ta wajan..

Umman Fareed ce ta fara fitowa ta k'araso wajan a zuciye, lafiyayyen Mari ta wanke Fareed dashi tana huci

"Bantaba sanin bakada hankali bah sai yau Fareed, yanzu akan mace shine kuke kokarin Kashe junanku?"

Kasa ma magana Mami tayi anma kana gani kasan ranta bah k'aramin Baci yayi bah. Mahnoor ta k'araso wajan ta rik'e Sulthana daketa kuka kamar ranta zai fita tasata a mota. Motar y'an sandan dake bayan nasu Mami Umman Fareed tasa aka shigar dasu Masroor aka kaisu Asibitin dake Cikin gidan..

Daddy da Abban Fareed suma Ransu bah k'aramin baci yayi bah bama Kamar Abban fareed dan shi cewa yayi Fareed ne baida gaskiya dan koma menene bai kamata ya biyo Masroor har gidansu ya dakeshi bah. Dole hakan yasa aka hadu dan Sulhu wuraren K'arfe sha d'aya na dare a babban Falon Daddy..

Daddy da Abban Fareed a a gefe zaune sai Mami da Umman Fareed suma suna gefe. Su Masroor kuma suna k'an Carpet zaune kowa da kumburaren Fuska. Daddy neh ya soma magana fuskanshi bah walwala

"Banji dadin abinda ya faru bah, haba Masroor haba Fareed. Yanzu akan mace kuke kokarin kashe kanku"

Abban Fareed yayi saurin amshewa da cewa

"Yanzu idan abun nan yakai waje duniya zatai mana dariya akan cewa ga y'ayanmu suna fada tsakaninsu akan mace. Sam wannan abin bai dace bah"

Masroor ne ya soma d'agowa yace

"Daddy, Abba kuyi hakuri"

Abba ya nuna Fareed da yatsa

"Duk abinda ya faru ga babban mai lefi nan, haka kawai Masroor baya kamaka da dukaba dan kazo gidansu. kaida nakema Kallan mai hankali ashe bakada shi, karka manta kaifa babba neh ka girme ma Masroor anma ace haka na faruwa tsakaninku"

Daddy yace

"Ai bashi k'adai bah harda Masroor din, shima kana ganinshi bashida hakuri."

Abba ya nisa yace

"Sam baku kyauta mana bah. Banji dadi bah kun bamu kunya"

Daddy ya nunasu da yatsa

"Sannan ku sani yarinya bazata taba aurenku bah duka tuna abin haka neh"

Mami tai Saurin cewa

"Ur excellency inaga hakan kamar tauyewa neh. Yakamata ita yarinya ta fadi wanda takeso sai a bata, wanda kuma bataso saiya hakura"

Gyada kai Abba yayi

"Wannan Gaskiya neh"

Daddy yace

"Abinda za'ayi gobe in Allah ya kaimu da Sassafe dukanmu zamu dunguma muje kauyensu dan mu samu asalinta. D'an duk wannan abin da mukeyi kamar munyi tuyane mun manta da Albasa"

Umma tace

"Gaskiya neh"

Abba yace

"Hakan ma yayi, daga chan sai ayita ta k'are ta fadi wanda takeso mu nema masa aurenta kawai"

Kowa dake falon ya amince Abba yace su Fareed su tashi su tafi, duk suka mik'e suka bar falon kowa jiki a sanyaye..

A daren Mami ta samu Sulthana a dakinta kwance tana aikin kuka, karasawa tayi ta zauna kan gadon ta dagota tareda share mata hawaye.

"Wannan kukan duk na menene? Ya isa haka kinji"

Kai ta gyada kawai kanta a kasa dan yanzu kunyan yan gidan takeji. Mami tace

"Gobe dasassafe ki shirya zamuje kauyenku dan.."

Kuka Sulthana ta fashe dashi ta rik'e hannun Mami gam

"Dan Allah Mami karku maidani wajan Baffa kasheni zeyi"

Rufe mata Baki Mami tayi cikeda tausayawa

"Bah barinki zamuyi bah, zamuje neh dan yasan kina wajanmu"

Dakyar Mami ta shawo kanta ta amince, saida taga Barci ya dauketa Sannan tabar dakin..

Ranar Fareed da Masroor babu wanda ya runtsa kowa da abinda yake s'akawa a ranshi. Ganin bacin ya gagara yasa Masroor mik'ewa yayo Alwala ya soma kai kukanshi gurin Ubangiji..

Kamar yanda akayi da Sassafe Abban Fareed da Umma sai shi Fareed din suka iso gidan, Already su daddy sun shirya. Wasu motoci daban suka d'auka bana gwamnati bah suka dau hanyar kauyensu Sulthana..

Fareed ne yakema Drivern kwatance har suka kawo kofar gidan. Gaban Sulthana ne ya fadi sanda ta kalli gidan, duka suka fifito daga mota anma banda Sulthana, Mahnoor ta bud'e kofan

"Sulthana fito mana"

Dakyar ta sauko kafa ta fito tana bin kofar gidan da Kallo, bah abinda ya chanza har yanzu komai na nan yanda yake, saidai ta lura kamar yanzu bah almajirai a runfar su. Yaro su Abba suka samu yamusu Sallama da Baffa.

Ba'adau lokaciba ya fito daga gidan, Kallo d'aya zakaima Baffa kaga ramar da yayi. Duk ya fige kamar bashi bah, ganin Manyan Mutane Yasa jiki na rawa ya shiga cikin gida yasa aka shishimfida tabarma sannan ya fito yace

"Bismillah ku shigo"

Sam bai lura da Sulthana dake jikin Mami a makale bah. Tsakar gidan suka shiga Suka zazzauna, Ameenatu ta fito daga dakin Mama dauke da kwanun sha ta aje Sannan ta gaidasu, harta mik'e suka hada ido da Sulthana. Mik'ewa tayi dasauri tana nuna Sulthana bakinta na rawa

"Su..Sul...Sulthana"

Baffa ya mik'e yana kallan inda Ameenatu ke nunawa, jin kamar an kira sunan Sulthana yasa Mama fitowa daga dakinta hakama Hafsatu

K'ara shigewa jikin Mami tayi tana boye Fuska, Baffa ya soma Hawaye yana cewa

"Sulthana ki gafarceni, nasan nayi kuskure. Sharrin shedan neh da kuma rashin sani"

Jin abubuwan da Baffa yake cewa yasa ta d'ago tana kallanshi da Mamaki. Mama ta k'araso wajan itama tana hawaye

"Sulthana dama kina raye, bah inda bamuje nemanki bah. Baffanki kullum ke yake anbata"

Sai kallansu Sulthana take da Mamaki, Abban Fareed neh yace

"Mallan zauna muyi magana"

Bah musu Baffa ya zauna yana matsar kwalla. Tunkan Abba ya sake Magana Baffa ya soma zaiyane musu duk abinda ya faru yana hawaye. Kuka Sulthana take na farinciki da Allah yasa ita bah shegiya bace. Bayan ya gama Abban Fareed shima ya dora da basu labarin zaman datai tareda fareed da kuma wanda tayi a gidansu Mami..

Zabura Baffa yayi ya gyara zama yana rarraba ido

"Dama da Gwamna da Mataimakinshi nake zaune"

Ya juya ya Kalli Mama dasu Ameenatu tana mai cikeda Farinciki. Hafsatu da yanzu ta zama salaha tace

"Sulthana ki yafemin lefukan dana miki, nasan nayi kuskure"

Yau Sulthana na Cike da Farinciki yau ga yan uwanta na santa suna neman gafaranta.. batareda wani dogon tunani bah tace

"Baffa, Mama, yaya Ameenatu, yaya Hafsatu duk na yafemuku tuntuni, dama ban rikeku bah. Ina sanku sosai"

Mik'ewa tayi ta rungume Baffa, ya fashe da kuka yana cewa

"Allah ya jikan Mahaifiyarki Allah ya gafarta mata. Ke kuma Allah ya miki Albarka"

Ameen tace Sannan ta janye jikinta ta rungume Mama da sauran Y'an uwanta..

Su Daddy yan kallo suka koma kowa yana tayata Murnar sassantawa da Mahaifinta da y'an uwanta

Mama ta mik'e ta soma kici kicin d'aura girki na musamman Dan tarban manyan Bakinsu...

Saida aka natsa, Sulthana tana d'akinsu Yaya Ameenatu itada Mahnoor sunata basu labarin Birni sukuma su Daddy suna kam tabarma cikin ihuwa sunata hira da Baffa kamar sun saba. Su Masroor kuwa suna chan gefe zaune sunyi jugum jugum kowa da abinda yake sakawa a ranshi...

Ummy Abduol✍🏻

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 198*

Su Masroor kuwa suna chan gefe zaune sunyi jugum jugum kowa da abinda yake sakawa a ranshi sannan Abba ya gyara zama yaba Baffa labarin Soyaiyar dake tsakanin Sulthana da y'ayansu sanna ya d'aura da cewa

"Dole yanzu zamu kirata neh ta zaba wanda takeso a cikinsu"

Baffa ya b'ata rai

"Haba ranka ya dad'e ai duk wannan bai taso bah, kuma fah iyayenta neh ku da kanku kawai ku zaba mata wanda zata aura"

Daddy yayi murmushi yana k'allan Baffa

"Aa baza'ayi haka bah, idan mukai haka kamar mun tauyeta neh. Tho idan kuma muka zaba mata wanda ita bai kwanta mata bafa?"

Shiru Baffa yayi baice komai bah. Abba yad'au waya ya kira Umma yace su fito duka, duk suka fito daga dakin Mama itada Mami suka zauna k'an tabarman. Baffa Yacema Mama ta kira Sulthana tace tho

Dakin ta shiga ta kirata suka taho tare, koda sukazo sun samu Fareed da Masroor xaune a wajan. Kusada Mami ta zauna k'anta a kasa, Abba ya kalleta da fara'a

"Y'ata mun kiraki neh dan muji ra'ayinki. Munaso ki fada mana tsakanin Masroor da Fareed wa kikeso"

Gabanta neh ya fadi ta d'ago ta kalli Masroor taga kanshi a kasa ta maida dubanta ga Fareed shima kanshi a kasa. Kasa magana tayi gabanta na cigaba da bugawa. Mami ta tabota

"Sulthana kiyi Magana mana karkiji Tsoro ki Fada abinda ke ranki"

Shiru tayi nad'an mintina Sannan tad'an dago bakinta na rawa tace

"Ya Fa..."

Dasauri Fareed ya d'ago ya kalleta da Alamar Mamaki, Masroor ko runtse idonshi yayi zuciyarshi na bugawa da sauri. Umman Fareed tace

"Kiyi Magana mana Sulthana keh muke jira"

Ta maza tayi ta saukar dakanta kasa tace

"Yah Masroor"

Sauke kai Fareed yayi yana girgixa kai ahankali, dasauri ta tashi tabar wajan. Abba yace

"Tho Alhamdulillah tunda yarinya ta fadi wanda takeso yanzu sai ayi maganan sadaki koh"

Su Umma najin haka suka mik'e suka bar wajan, Su Fareed suma suka mik'e suka fita waje. Fareed ya share hawayen idonshi yace

"I'm very sorry friend"

Ya mik'ama Masroor hannu yace

"Congratulations am very happy for you, Allah ya sanya Alheri"

Jikin Masroor neh yayi sanyi shima ya mik'amai hannu

"Ni yakamata nabaka hakuri, bakai bah"

Fareed ya girgixa kai ya shiga mota ya zauna ya daura kanshi jikin stering motan ranshi jagule..

Sulthana na shiga d'akinsu ta fada kan gado ta fashe da kuka, Ameenatu ce ta dafata tana cewa

"Meke faruwa Sulthana?"

Mik'ewa zaune tayi hawaye chabe chabe a idonta, tace

"Bansan da wani ido ya Fareed zai kalleni bah. Gani nake kamar namai Butulci"

Hafsatu ta dafata tana Murmushi

"Mahnoor ta mana bayanin komai, kuma bakida laifi saboda bai sanar dake bah Sannan kuma na lura bah wai sanki yake bah tausayinki neh"

Sulthana ta k'ura mata ido da Mamaki, gyada mata kai Hafsatu tayi sannan ta juya ta Kalli Ameenatu wacce itama su take kallo ta juya ta maida dubanta ga Sulthana tace

"Ya Ameenatu ta dad'e tanasan Likitan nan, tun sanda ta soma ganinshi ta fara sanshi, kullum sai tayi min maganar shi."

Mik'ewa Ameenatu tayi rai b'ace

"Baki kyautamin bah Hafsatu Ashe bazaki iya rik'emin d'an sirrin nan dana baki bah"

Murmushi Sulthana tayi ta share hawayen Fuskanta ta mik'e ta fito tsakar gidan, ganin su Fareed basa wajan yasa tasa takalmanta ta fita kofar gida. Zaune ta sameshi cikin mota shida Masroor suna hira jefi jefi, nesa dasu ta tsaya Masroor na ganinta ya fito ya karaso inda take yana murmushi

"Har na cire rai Beauty, sai gashi nine gwaninki"

Hannu yasa ta rufe fuskanta tana dariya

"Dan Allah ya Masroor inaso nayi magana da Ya Fareed"

Murmushi ya mata

"Bbu komai ki sameshi a mota"

Dariyan jindadi tayi

"Thank uh Bro Masroor"

Da Sassarfa ta k'arasa bakin motan ta bud'e ta shiga tana Kallanshi

"Ya Fareed kayi hakuri dan Allah"

Sai a Sannan ya d'ago ya kalleta tareda k'irkiro Murmushi

"Bakimin komai bah Queen, Laifina neh da ban fadamiki tun tuni bah naiyi zurfin ciki, haka Allah yaso. Allah ya nufa ke bah Matata bace"

D'an dukar dakai tayi tana wasa da zoben dake hannunta tace

"Nagode ya Fareed, bazan t'aba mantawa dakaiba a rayuwata. Kayimin Abubuwa da dama wanda banida bakin godiya, ka taka muhimmiyar rawa a rayuwata thank uh v...."

Saurin katseta yayi ya d'aura yatsanshi a lebenshi

"Uh dn't have to thank me"

Jim tayi nad'an wani lokaci sannan tace

"Ya Fareed akwai wani abu danakeso kayimin dan Allah"

Batareda wani bata lokaci bah yace

"Menene shi Queen?"

Tacigaba da cewa

"Inaso dan Allah Ya Fareed ka auri ya Ameenatu"

Dasauri ya juyo yana kallanta da mamaki, gyada mai kai tayi tana y'ar murmushi. Kasumbar dake fuskanshi ya shafa

"Ita tace miki tana sona?"

Girgiza kai tayi alamar Aa. Ya numfasa yace

"But queen I have no feelings for ha, and zai iya yuwuwa bata sona. Kawai ki barshi nagode"

Ta turo baki ta soma gungunai

"Nidai Dan Allah Ya Fareed ka aureta, shes kind kuma batada matsala. Nasan zata soka and kuma kagani zaku saba"

Dariya yayi Mara sauti yana k'allanta kasa kasa, baisan ya musa mata kuma a ganinshi wannan karamci tamai and kuma bah lefi yarinyan tanada kyau Sam bata kamo k'afar Queen dinshi bah dukda ita b'akace.

Ya juyo da Fara'a kwamce kan Fuskanshi yace

"Shiknan Queen na Yarda"

Ihu ta saki tana dariya har saida Masroor ya K'ara sako wajan dasauri. Fitowa daga motan tayi ta shiga cikin gida da gudu. Dakyar suka shawo kan Ya Ameenatu ta fita wajan Fareed, a waya Sulthana ta fadama Masroor abinda ke faruwa, Yaji dadi sosai shima. Ameeantu da Fareed sun fahimci juna kuma har ya Amince zai aureta, su Daddy sunyi Mamaki sosai jin Maganan. Basu bar Kauyensu Sulthana bah saida aka tsaida Ranar Bikin Masroor da Sulthana sai Fareed da Ameenatu wata d'aya, Aka ba Baffa sadakinsu Dubu D'ari d'ari dan Baffa yace baison Asa Sadakin dayawa..

Mama ta rok'i Alfarman a bar mata Sulthana har zuwa ayi bikin. Baffa ya tambayi Sulthana ta amince batai Gardama bah, Masroor sam baiso haka bah bah yanda zaiyi hakanan ya hakura sukai musu Sallama suka tafi bayan Sun Cika Baffa da kudi. washe gari Mami ta turo Driver da Kayan Sawan Sulthana da Kayan Abinci dana sawa nasu Mama cike da Mota...

Kula Sosai Sulthana take samu a gidan Mahaifinta ta bangaren Mama da Baffa har takan rasa wayafi kula da ita. Kullum suna Makalle da Masroor a waya haka soyaiya Suke mai Tsafta da Shiga rai. Fareed na Xuwa wajan Ameenatu hakan yasa suka k'ara shakuwa da ita, ya sai mata waya itada Hafsatu. Shima Masroor na xuwa shida Yasir..

Mama ta zage tanata gyara Y'ayan nata daidai karfinta, Mami ma Tana aiko Mahnoor da Wasu kayan gyaran jikin anaba Mama dan tayi Musu. Yau Saura kwana biyar Biki, Yau Sulthana take expecting Mahnoor dan tace mata zatazo har a gama biki. Tana gidansu Sadiya K'awarta Wayan Sulthana yahau Ruri, ta d'auka da Fara'a tana cewa

"Kin iso neh"

Harta mik'e ta koma ta zauna tace

"Yah Hafsatu tana Nan kice ta kawoki"

Bata jira mai zatace bah ta kashe kiran. Sadiya dake gefenta tace

"Ta iso neh?"

Da Fara'a tace

"Eh wai da lefe suka zo"

Dariya Sadiya tayi ta mik'e dasauri

"Ah bari muje muga Lefe"

Tab'e baki Sulthana tayi sadiya tad'au mayafinta ta fita daga gidan dasauri. Tana fita Mahnoor ta shigo gidan itada ya Ameenatu, sulthana ta mik'e dasauri ta rungumeta tana Dariya

"Uh welcome"

Dagota Mahnoor tayi daga jikinta tana k'are mata kallo

"Friend kinga yanda kika koma? Kin K'ara kyau sosai"

Turo baki Sulthana tayi tana doka kafa a kasa. Nan suka zauna suka soma hiran yanda bikin zai kasance basu bar gidan bah sai Yanma lis lokacin sun tabbatar yan kawo lefe sun tafi..

Ummy Abduol✍🏻

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
*SULTHANA*
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

By *Ummy Abduol*


DA

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login