Showing 27001 words to 30000 words out of 44304 words
ransh b'ace..
Yanmacin ranar Sulthana tadau gyadanta kamar yanda ta saba, Bakin tasha ta nufa ko kamin ta k'arasa ta hango motar Masroor pake a inda suka saba zama, da sauri ta k'arasa tana murmushi. Ta mirrown motan ya hangota zuwa ya fito dasauri ya nufeta yana huci
"Dama labarinda kika fadamin duk k'arya neh Sulthana? Ke ashe shegiya ce bakida uba"
Trayn kanta neh ya fadi ta k'walallo ido tana kallanshi da Mamaki, cigaba yayi da Magana cikin kakkausan Murya
"Kin cuceni Sulthana, dama duk abinda kika fadamin k'arya neh? Duk sanda nake miki? Duk lokacinda na bata akanki"
Tsugunawa Sulthana tai ta fasa ihu tareda daura hannu aka
"Yaya Masroor waya fadama wannan maganan? Wallahi k'arya neh Baffa shine Babana"
Ranshi b'ace ya juya Mata baya
"Shi Baffan zai miki Karya neh? Haba Sulthana Kinsa Mahaifina dani munji kunya, why Sulthana why?? Nasan baki sani bah Mahaifina neh Gwamna mai ci yanzu Alhaji Aminu"
Dagowa tayi da Mamaki tana K'allanshi
"Danasan Abinda zai faru knan daban bari Aminan mahaifina sunzo bah. Yanzu da wani ido zan kalli Daddy nah?"
Kuka sosai Sulthana take Hankalinta tashe
"Dan Allaha yaya Masroor karka gujeni, kai kad'ai ke sona kake tausaya min. Idan ka tafi ya zanyi"
Tsugunawa Yayi kusada ita zuciya na cinshi
"Sulthana Bazan iya bah"
Bai jira mai zatace bah ya shiga mota ya bar wajan a guje. Kuka ta k'ara fashewa dashi kamar ranta xai fita, hakanan ta d'au trayn gyadan ta nufo gida tana cigaba da kuka.
Zaure ta zauna ta cigaba da kukanta, saida tai mai tsarta Sannan ta mik'e rai bace ta shiga cikin gidan. Zaune ta samu duka y'an gidan a k'atuwar tabarma da Alama iska suk'e sha. Karasawa tai ta aje trayn a gaban Baffa ta tsugunna akan tabarman k'anta a kasa ta fara magana
"Baffa mai nai maka ka tsaneni baka sona? Idan na maka laifi neh kai hakuri. Meyasa kace bakai ka haifeni bah"
Da mamaki Mama ta k'alli Mallan Gabanta na faduwa
"Mallan Abinda Sulthana ta fada Gaskiya neh"
Tsaki yayi tareda kauda kai
"Hakaneh mana, bazai yuwu bah ace d'an gwamna guda yazo neman aurenta batareda na fadamai abinda ke faruwa bah. Tho yau ku shaida zan amayar da Abinda yake cikina"
Hafsatu ta mik'e dasauri tareda dafe k'irji
"Dan gwamna"
Daga kai Mallan yayi yana k'allan Hafsatu
"Kwarai kuwa"
Hankalin Ameenatu neh ya tashi tace
"Baffa muna jinka me kace zaka fada"
Sulthana ya nuna da Hannu yana cewa
"Sulthana bah y'ata bace, Shegiya ce batada uba. Cikin Shege uwarta tai ta haifeta"
Ihu Sulthana ta saki ta mik'e Dasauri ta daura hannu a kai ta fashe da kuka, rasa inda zatasa kanta tai ta dawo gaban Mallan ta tsugunna tana kuka sosai
"Baffa kai hakuri karka ce haka, ni yarinyanka ce haka Umma tace"
Tsaki yayi
"Karya umman naki takeyi, niba ubanki baneh"
Mutuwar Zaune Mama tai itada Ameenatu, Hafsatu ko cewa take
"Ashe gado tai, shiyasa itama take bin maza. Lallai gwara Baffa daka fadamana"
Kamar mahaukaciya Sulthana ta zama a cikin gidan, ihu kawai take tana kuka kwi kwi. Mama tai k'arfin Halin cewa
"Tunda nake ko a tarihan da mahaifana suka bani ban tabajin inda Uba yakema Y'arshi hakaba sai kai. Kaicona da aurenka Mallan"
Mik'ewa Mallan yayi yana huci
"Ni kike jifa da irin Wadannan Kalaman?"
Kauda kai Mama tai Ranta bace. Baffa ya dakama Sulthana Tsawa yanacewa
"Tunda abin naki ya zama haka maza ki tattara inaki inaki ki tafi ki nemi ubanki. Kada ki kuskura na fito daki na ganki a cikin gidan nan"
K'ara rushewa da kuka Sulthana tai ta rungume Mama tan kuka kamar ranta zai fita
"Dan Allah mama kice Baffa yayi Haquri ni y'arshi neh. Kadaya koreni dan Allah, wayyo Allah na"
Ameenatu ta rarrafo inda sulthana take rungume da Mama itama tana hawaye
"Kiyi haquri Sulthana, Baffa shine Babanki. Kada..."
Muryan Baffa dataji a kanta neh ya hanata k'arasa Maganan datai niya
"Kul! Karna k'araji Sam bah y'ata bace. Maza ki tattara ki bar min gida"
Dorinan daya fito dashi ya d'aga Sulthana na gani ta mik'e dasauri ta fice Zuwa zaure da gudu tana cigaba da kuka..
Mama ta shiga Dak'inta tadauko Mayafinta tana cewa
"Allah wadaranka Mallan, bazan iya cigaba da zama dakai a gidan nan bah"
Takalmanta tasa ta fice daga gidan tana kuka...
Gudu sosai Masroor yake yana kuka kamar K'aramin Yaro. Gidan da suk'a baro ya nufa wanda yanzu shine gidanshi, yana shiga ko k'wakwaran Parking beyi bah yahau hada kayanshi a Trolley yana cigaba da kuka. Waya yama Yasir akan su Hadu a Airport, dama Tun kwana biyu da suka wuce visan shi ya fito. Yana gamawa ya fitoda Akwatin yasa a mota ya kulle gidan ya nufi Airport..
Yana zuwa Yasir na K'arasowa, fitowa yayi daga nashi motan ya dauko Akwatinshi ya k'araso inda Yasir ke tsaye yana k'allanshi da Mamaki
"Friend meye haka?"
Hawayen idonshi ya share yana kallan Yasir
"Sulthana betrayed me, bazan iya cigaba da zama a k'asan nan bah."
Hannunshi Yasir ya kamo Cikin sigan Lallashi
"No Friend, Ni inaji a Jikina Sulthana nata yaudareka bah. She's young and batada wani ilimin da zata fadama K'arya, think of dis"
Girgiza kai Masroor yayi hawaye na gangara a idonshi
"I love her so very much Yasir, meyasa zatamin haka? Ni nasan Mutumin nan bazai mata k'arya bah"
Hannunshi Yasir yaja
"Pls Friend be strong muje gida mu tattauna"
Kai Masroor ya girgiza, duk yanda Yasir yaso Masroor ya hak'ura fafur yak'i yarda dole hakanan ya hakura ya barshi yahau jirgi zuwa lagos shi kuma ya tuk'a motar masroor din ya nufi government house jiki a sanyaye
Bayan dogon bincike Aka bari ya shiga gidan, nan ma kamin ya samu ganin Mami sai da akayi bincike Sosai Falonta datake ganin bak'i aka kaishi. Jin Yasir neh yasa batad'au wani lokaci bah ta shigo falon tana fara'a
"Idonka knan Yasir, tun bayan election ban k'ara ganinka bah"
Duk'ar dakai yayi fuskanshi bah Annuri, ganin haka yasa Mami ta zauna a sanyaye
"Yasir meke faruwa?"
Labarta mata duk yanda sukai da Masroor yayi cikeda damuwa. Mami ta girgiza kai rai bace
"Lallai Masroor ka kyalleshi ai dai ba'achan zai xauna kwatakwata bah koh? Zai dawo ya sameni"
D'agowa Yasir yayi
"Mami Masroor nasan yarinyan nan sosai, ni ina tunanin tsabar k'iyaiya ce kawai da Mahaifinta yake mata yasa yace haka"
Jim Mami tai alamar tunani Sannan tace
"Nima ina tunanin haka saidai bah yanzu zamu tunkari Alhaji da maganan bah dan yanzu yayi fushi"
Yasir ya gyada kai ya mik'e tsaye tareda mik'a mata keyn motan Masroor. Amsa tai tamai godiya yabar gidan...
Kuka sosai Sulthana take tana gudu batareda tasan inda zata bah, gashi gari ya fara duhu dan anata kiraye kirayen Sallan Magriba. Bata farga bah Ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya sam bata lura da hadari bah. Cigaba tai da gudun lokaci lokaci tanasa bayan hannunta na hagu tana share hawayen Fuskanta. Hasken Fitilan motane ya haskata ko kamin tai wani yunkuri tuni motar tai ciki da ita ta fadi k'asa sumammiya...
Ummy Abduol✍🏻
💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_
*Page 156 to 160*
Dedicated dis page to *Hadiza Ya'u* best fan.. Allah ya bar zumunci
Hasken fitilan motane ya haskata ko kamin tai wani yunk'uro tuni tayi ciki da ita ta fadi K'asa sumammiya. Dasauri ya fito daga motan hankalinshi tashe, Ganin wanda ke wajan yayi baya da sauri da Alamar mamaki. Nunata ya soma y bakinshi na rawa yace
"Su..Sulthana"
A hankali ya k'arasa inda take kwance ya d'auketa yasata a mota ya figi motan xuwa babban Asibiti dake cikin garin Kano inda yake aiki. Shi da kanshi ya shiga bata taimakon gaggawa duk da yanayi jikinshi na rawa zuciyarshi na bugawa, saida numfashinta ya daidaita sannan ya fita zuwa gidanshi kamin ta farka lokacin wuraren k'arfe goma na dare..
Sallah yayi Sannan yayi wanka duk hankalinshi na wajan Sulthana, wayanshi ya jawo ya soma neman layin Sa'ood yakoyi Sa'a yana fara ringing ya d'aga
"Aboki ya Akaine?" cewar Sa'ood
Murmushi Dr Fareed yayi suka gaisa sannan ya zaiyanamai abinda ke faruwa. Shiru Sa'ood yayi nad'an wani lokaci Sannan yace
"Yanzu abinda za'ayi gobe mu hadu a asibitin da safe lokacin ta farka sai mu tattauna"
Tho Fareed yace tareda mai godiya ya kashe kiran. Keyn motanshi ya d'auka ya rufe gidan ya koma asibiti, har yanzu bacci take. kujera yaja ya zauna kusada gadon datake kwance. K'allanta yake yana murmushi, hannunta na dama ya saka cikin mashi yana murzawa a hankali, a haka barci ya d'aukeshi ya d'aura kanshi gefen gadon..
Masroor na Sauka Lagos Airport, taxi ya shiga ya kaishi hotel dinda zai kwana. Yini yayi bah walwala koh abinci ya k'asa ci. Zuciyarshi Sunan Sulthana kawai take kira, Wayanshi ya janyo ya kunna sannan yasata a Fight mode dan baisan a nemeshi. Pictures d'in wayanshi ya shiga, hoton Sulthana ya dubo wanda ita batamasan an d'auka bah tana xaune tana murmushi da alama Gyada akazo siya
Shafa hotan ya soma yi hawaye cike a idonshi
"I love uh my beauty, meyasa kikamin k'arya"
Hawayen dake mak'alle a idonshi suka gangaro ya share tareda mik'ewa ya shiga toilet don watsa ruwa..
Sulthana bata farka bah sao wuraren k'arfe bakwai da rabi na safe. Firgigita ta mik'e zaune, bin dakin da Kallo ta soma yi cikeda mamaki. Ganin kan mutum kusa da ita yasata kwace hannunta tareda sakin ihu, tana k'okarin sauka daga kan gadon..
Farkawa Fareed yayi ya mik'e yana k'allanta da Murmushi
"Meya faru? Y are you shouting"
Drip din hannunta take kici kicin Cirewa tana k'allanshi a tsorace, rik'e hannunta yayi dasauri ganin tana kokarin jima kanta ciwo
"Me kike kokarin yi, ki kwanta bakida lapia neh"
Girgiza mai kai tayo hawaye na fita a idonta dak'yar da budi baki tace
"Ni ka ciremin wannan abin na tafi, ina neh nan? Waya kawoni"
Jin tashin Magana yasa Wata nurse ta shigo dak'in ganin dr Fareed yasa ta koma dasauri tana cewa
"Sorry sir"
Baice komai bah ya maida dubanshi ga Sulthana dake kuka a hankali
"Jiya da Daddare na bigeki a mota shine na kawoki asibiti, ina zaki da daddaren nan Sulthana"
Sai a Sannan ta tuna koran da Baffa ya mata, wani sabon kukane yazo mata, ta kauda kai gefe tana kuka kamar ranta zai fita. Runtse idonshi yayi ya naushi Iska ya fice daga Dak'in, Nurse dinda ta leko yama magana akan karta bari ta fita Sannan ya fita zuwa haraban asibitin. Motarshi ya hau ya figeta yabar Asibitin
Gidanshi ya nufa saida yayi wanka sannan ya k'arya duk abinda yakeyi jikinshi a mace yake. Wayan Sa'ood ya kira yace su hadu k'arfe tara a asibiti. Yana gama wayan yad'au keyn motarshi ya fice. Gidansu ya nufa batareda dogon bincikeba saboda securitys din sun sanshi aka barshi ya shiga gidan..
Mottoci ya gani kusan guda biyar a haraban gidan cikin shiri, da wasu mata dake gefe da Alama Umma suk'e jira. Side din Umman ya nufa kai tsaye dan yasan yanzu Abba ya fita zuwa Office, Bai sameta ta falo bah sai ma'aikata daketa gyara Falon. Benen dake falon ya hau a nan suk'ai kicibus da ita cikin shiri da Alama fita zatayi
"Good Morning Umma" yace kanshi a k'asa
Tsayawa tai chak sannan tace
"Morning"
Jin tayi shiru yasa yad'an dago suka hada ido
"Fareed Meke damunka?"
Wayancewa yayi
"Babu komai me kika gani"
Hannunshi ta kama suka sauko k'asa. Ma'aikatan na ganin haka sukabar falon dasauri, zaunar dashi tai kan 1seater itama ta zauna ana kusa dashi
"Fadamin meke damunka? Bah haka ka saba zuwa bah"
D'an murmushi yayi
"Bbu komai Ummah i'm fine bah abinda ke damuna."
Bayaso ta cigaba da tambayatan shi dan haka yace
"Ummah inace ke ake jira a waje"
Mik'ewa tai dasauri
"Eh wallahi, zamuje mu hadu da Matar governor zamuje wani meeting neh"
Kai ya gyada yana y'ar murmushi
"Allah ya tsare, kice ina nan zuwa na gaidata"
Hararanshi tai cikin sigan wasa
"Ni y'ar aikenka ce?"
Dariya yayi k'asa kasa yana shafa sumar kanshi
Sallama tamai ta fita. Shima mik'ewa yayi shima yabar gidan.
Saida ya tsaya yasai mata abinci mai rai da lafiya sannan ya koma asibitin. Patient ya gani burjik sunata jiranshi, saida ya tsaya suka gaggaisa sannan ya nufi dakin da Sulthana take kai tsaye.
Zaune ya sameta kan gado ta hada kai da guiwa tayi shiru. A hankali ya k'arasa kusada gadon yaja kujera ya zauna, zabura tai ta d'ago idanunta da suka runne tana k'allanshi. Harta bud'e baki zatai magana kuka yazo mata ta k'auda kai gefe tana kukan a hankali..
Runtse ido yayi ya bud'e tareda aje mata abincin a kusada ita
"Kici abinci sai kisha magani barin duba patients"
Bai jira mai zatace bah ya bar office din. Kamar yanda suk'ai da Sa'ood k'arfe tara ya k'araso Asibitin lokacin ya gama duba patients dinshi. Fareed ne yama Sa'ood jagora zuwa dak'in, yanda ya barta haka ya dawo ya sameta bata taba abincin bah. Nunama Sa'ood kujera yayi ya zauna shi kuma ya tsaya a tsaye.
Sa'ood ya nisa yace
"Sulthana!"
Kai ta d'ago ta kalleshi shi kuma ya cigaba da cewa
"Ki kwantar da hankalinki bazamu cutar dake bah"
Fareed ya nuna da hannu yana cewa
"Nasan kinsan wannan, ki fadamin meya fito dake jiya da daddare har ya bigeki da mota"
Hawaye ya cika mata ido ta k'auda kai gefe murya chan k'asa tace
"Bah komai"
Murmushin takaici Fareed yayi tana girgiza kai. Sa'ood ya cigaba da cewa
"Karki boyemana komai Sulthana, munsan halin da kike ciki keda Baffanki so ki fada mana meke faruwa? dukanki yayi ko meh?"
D'agowa tai ta kalleshi da mamaki. Murmushi Sa'ood yayi dan ya gane k'allan datake mai
"Kina mamakin y'anda akai muka sani koh?"
Kuka ta saki tana cewa
"Baffa ne ya koreni daga gida yace bashine babana bah wai banida..."
Kukane yaci k'arfinta. Sakin baki su Fareed sukai da mamaki
"Bashi ya haifeki bah?" cewar Fareed
Kai ta gyada kanta a k'asa tana cigaba da kuka. Lallashinta Sa'ood ya soma yi dakyar tai shiru, ya mik'e ya kama hannun Fareed suka bar dakin. Wata nurse Sa'ood ya samu budurwa wacce bazata wuce shekara ashirin bah da gani y'ar practical ce yasa hannu a aljihu ya ciro kudi masu tsoka ya mik'a mata
"Inaso ki kulamin da patient din dake dakin chan"
Ya nuna dakin da Sulthana ke ciki sannan ya cigaba da cewa
"Tak'i cin abinci neh inaso kisata taci abinci pls and banaso tana kuka"
Kudin ta amsa tana washe baki
"Bbu damuwa sir za'ayi kamar yanda kace"
Office din Fareed ya shiga ya sameshi zaune yayi tagumi. Sun dad'e suna tattaunawa Sannan Sa'ood ya mik'e tareda mai Sallama yabar Office din.
Saida Sulthana tai kwana hudu a Asibiti kullum tana tareda Nurse dinda Sa'ood ya barma amanarta, Sun saba sosai dan Sulthana batada wuyan sabo har tad'an saki ranta.
Kayan sawa kala kala Fareed ya saima Sulthana, sister Aisha ita ta koya mata yanda ake saka kaya da sauransu. Randa ta cik'a kwana shidda aka sallamesu a nan neh hankalin Fareed ya tashi dan baisan inda zai nufa da Itabah..
*wai ina labarin Masroor neh?*
Ummy Abduol✍🏻
💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_
*Page 161 to 165*
Randa ta cika kwana shidda aka sallamesu a nan neh hankalin Fareed ya tashi dan baisan inda zai nufa da itabah. Yanke shawara kawai yayi ya kaita gidanshi dan haka ya juya akalan motarshi zuwa gidanshi...
A bangaren Masroor kuwa kwanashi Biyu a Lagos sannan jirginsu ta d'aga zuwa k'asar turkey. Karatunshi ya cigaba dukda har yanzu san Sulthana na nan mak'ale a zuciyarshi. Mami da Daddy sun kirashi sun mai fada sosai akan rashin Sallamasu da baiyi bah, kullum yakan zauna yayita tunanin Sulthana gani yake kamar bai mata adalci bah daya taho ya barta batareda ya mata Sallama bah.
Yau ya kama sunday yana zaune a gidanshi bayan ya dawo daga supermarket. Waya ya d'auka ya soma neman layin Yasir, bugu d'aya ya dauka suka gaisa. Shiru Masroor yayi nad'an seconds sannan yace
"Alfarma nake nema Yasir"
Batareda bata lokaci bah Yasir yace
"Ok babu damuwa"
Ajiyan zuciya Masroor yayi sannan yace
"Dan Allah Yasir inaso neh kaje min wajan Sulthana, she's always on my mind. Kullum zuciyana bugawa yake gani nake kamar wani abu ya faru da ita"
Saurin katseshi Yasir yayi da cewa
"No stop saying that, babu komai insha Allah"
Runtse ido Masroor yayi sannan ya bud'e, Yasir ya wuce aboki a wajanshi ya wuce Amini ya zama hamimi. Bah abinda zai iya boye mai, zaiyana mai duk yanda Sukai da Fareed yayi hankalinshi tashe..
Yasir yayi murmushi yana cewa
"Oh friend wani tabbaci kake dashi akan cewa Sulthana ce"
"Naji a jikina itace Yasir, idan har Fareed santa yakeyi bansan yanda zanyi bah I cn't live witout Beauty"
"Ka kauda wannan tunanin a ranka pls"
Kai Masroor ya gyada kamar yana ganinshi
"Shiknan sai na jika"
Sallama sukai tareda kashe kiran..
A kauye kuwa Mama na fita Ameenatu ta bita a guje tana kuka bako hijabi, hannun Mama ta rik'e
"Dan Allah Mama karki tafi, idan kika tafi dawa zamu zauna"
Kuka itama Maman keyi
"Ameenatu bazan zauna bah, duba fah abinda Mallan yayi yanzu kina kallo, wannan wanne irin k'iyaiya neh?"
Ameenatu ta share hawayen idonta da bayan hannu
"Kiyi haquri Mama karki tafi dan Allah, nasan Sulthana batai nisa bah zan dubota nidai ki koma gida"
Hannunta ta kama suka koma cikin gidan, dakinsu ta shiga ta samu hafsatu zaune kan gado tana nunke kaya
"Hafsatu komenene ya faru Sulthana K'anwarmu ce, kada ki daka ta baffa dan abinda ya fada bah gaskiya bneh. Ki natsu kiyi tunani kada rud'in duniya ta kwasheki, ranar danasani nake gudan miki Hafsatu, ranar da batada wani anfani"
Dagowa Hafsatu tai tana K'allan Ameenatu fuskanta bah walwala da Alama magananta ya fara tasiri. Ameenatu ta zauna kusada ita ta rik'o hannun hafsatu tana hawaye
"Hafsatu ke k'anwata ce kamar yanda Sulthana take kanwata. Haka kema Sulthana kanwarki ce, bai kamata muk'i yar uwarmu bah jinnin mu ce ki tuna"
Hawayen idonta ta share tana jan magina
"Kinyi karatun Addini daidai gwargwado akwai hadisi da manzo Allah tsira da Aminincin Allah su tabbata a gareshi yake cewa imanin d'ayanku baya cika har sai kasowa d'an uwanka abinda kakd soma kanka. Kiyi tunani cikinmu bah wanda yakeso ya kasance cikin rayuwar da Sulthana take ciki