Showing 39001 words to 42000 words out of 214133 words
bacci take ji sosai da sosai ga gajiyar aiki, ga ta biki, ga tashin hankali ga kuma dukan da ta ci jiya da daddare a wurin Iya.
Babu tsammani ta ji rugugin hadari, da walƙiyya ko ta ko ina, fashewa tayi da kuka, tana son tashi ta fita da gudu ta koma gida, amma tsoro ya hanata.
Tana nan zaune ruwa ya kece ya din ga zuba kamar da bakin ƙwarya, ta tashi da nufin ta rufe ƙofar ɗakin, amma ƙarfin zubar ruwan, da kuma tsawar da ake yi, ya sanya ta koma ta zauna tana cigaba da kuka.
Ruwa ya din ga feshi cikin ɗakin, wani irin sanyi ya mamaye garin.
Ruwa ya shigo ɗakin sosai ya jiƙe, sai dai bai kai kan katifarta ba.
Kasancewar bacci ɓarawo ne, ya kwashe ummi a nan zaune ba tare da ta shirya hakan ba.
sai da gari ya waye ya fara haske, sannan ta tashi a razane.
Ruwan da aka yi duk ƙasa ta shanye, ta zama taɓo, wani kofi ta gani a tsakar gida, ya cika da ruwan da aka yi, tayi alwala da shi, ta koma ɗakin tayi sallar asuba.
Tana nan zaune cikin zullumi da fargaba, aka yi sallama, wasu daga cikin ƴan biki ne suka zo, hakan ya sanya ta ji daɗi.
Suka din ga rafsa guɗa, ummi dai da ido kawai take bin su.
Suka kawo mata abun karyawa, ake tambayarta ina angon? Tayi shiru ba ta ce komai ba, dan kuwa ba ta san me za ta ce ɗin ba.
Suka ƙara yi mata ƴan gyare-gyaren da zasu yi mata, suna ta hira suna yi mata nasiha, da azahar suka ce za su tafi.
Ummi ta ɗau hijjabinta ta ce za ta bi su.
"Ki bi mu ina? Ai ko ƙofar gida ki ka fita babu iznin mijinki, Allah zai ƙona ki a wuta, ki koma ki zauna, shima yana ango amma safiyar fari ya fice, har azahar bai dawo ba?" Cewar wata dattijuwa.
Ƙanwar Iya ta ce "Bar mara mutunci, ai da alama ba son auren nan yake yi ba, haɗin Iya ne kawai, kodayeke ai ma ya furta, tun da hama ta yi masa Allah ya sanya alkhairi, ya ce ba amin ba, ba ya so"
"Too ikon Allah, ai dama idiris ba mutunci ya cika ba, har ta bani tausayi, sannu kin ji ummi, Allah ya baku zaman lafiya ya baki juriya" suka gama salallaminsu suka tafi.
Ta dawo tsakar gida, ta haɗa takalmanta ta zauna, ta zubawa hanyar ƙofar gida ido, in da Allah ya taimaketa, baƙin da suka zo, sun saka yara su je gida, sun ɗaukko bokiti, an cika mata shi da ruwa, da haka ta samu na alwala.
Da la'asar aka turo ƙanin idris ya kawo wa ummi, abinci ta karɓa ta ce masa dan Allah ya tayata zama kar ya tafi, tsoro take ji.
Cikin ikon Allah bai tafin ba, ya tayata zama, har suka ci abinci tare, sai magariba ya tafi ya bar ta ita ɗaya ƙwal kamar mayya.
Hashim ya rasa in da zai sanya ransa, damuwa ta din ga sassaƙar zuciyarsa, gashi tun da aka ɗaura aure, bai saka idiris a idonsa ba, yana son zuwa gidan ummi, amma yana tsoron yaje ya tarar da abun da ba shikenan ba, da zai ɗaga masa hankali.
Baban su Idris ya samu Iya yake tambayarta, ya za ayi da dangin mahaifiyar Ummi, yakamata a sanar musu.
Iya ta ce "Rabu da su, gayyar tsiya ko an gaya musu uwar mai za su tsinana, talakawan banza, ba su ajiye komai ba sai buzu da tawwada sai allo, ai a haka aka tsaface mini ɗa, aka shanye shi ba ya moruwa sai abun da take so, yanzu idan suka sani tsaf za su yi wata ƙulla-ƙullar, a bari sai komai ya lafa, an kwana biyu sai a aika musu da goro da alewa ace na aurar da jikata, shikenan"
Saminu ya ce "Amma Iya za su ga kamar ba a kyauta musu ba fa"
"Ita abubuwan da tayi mini kyautawar ta yi? Can su ƙarata yarinya ce dai na aurar da ita"
Saminu ya jinjina kai, amma dai ya san abun da aka yi ba a kyauta ba, ko ba komai suna da hakki a kan ummi, tun da ƴar su ce ta haifeta.
Ummi haka ta sake kwana a gidan nan, ita kaɗai babu idris babu alamarsa, haka ta sake yin kwanan tsoro da tashin hankali.
Sai dai wayewar garin Allah, babu wanda ya tuna da ita balle ya aiko mata da abinci.
Babar idiris ta fara ƙorafin, tun da aka kai ummi, Idiris bai zo ya ko gaishe su ba, har maganar ta je kunnen iya, ita ma tayi maganar a ranta, amma kasancewar sai a ranar baƙi suka gama watsewa, abun ya dawo kanta.
Rai a ɓace ta aika Alhassan, ta ce ya je gidan ummi, ya ce Idris ya zo tana nemansa.
A hanyar ƙofar fita, ya tarar da ita a zaune, tana kallon masu wucewa.
"Ke ummi, kina amarya kina zama a hanyar ƙofar gida kina leƙe?"
Duk da ba shiri suke yi ba, ummi ta ce "Tsoro nake ji, nikaɗai ce a gidan"
Ya ce "Taɓ, ina yaya idiris, Iya ta ce yaje tana nemansa"
Ummi ta ce "To ai bai taɓa zuwa gidan nan ba, ni tun da aka kawo ni ban ganshi ba"
Ya waro ido ya ce "Ke da gaske!? Ke kaɗai ki ke kwana a gidan nan?"
Ta ɗaga masa kai alamar eh.
Ya ce "Sannu da ƙoƙari, kuma ki ka zauna? Kodayeke idan ma ki ka ƙi zama kin san sauran, bari na je na gaya wa Iyan"
Hankalin iya ba ƙaramin tashi yayi ba, da jin cewar wai tun da aka kai ummi bai taɓa kwana a gida ba.
Ta ɗau mayafi ta tafi gidan ummi, a nan tsakar gida suka tarar da ita a zaune.
"Ke ummi, ashe tun da aka kawo ki, Idiris bai kwana a gidan nan ba?"
Ummi ta ɗaga mata kai alamar eh.
"Kuma dan ubanki ki ka ja baki ki ka yi shiru baki faɗa ba? Har sai da na aiko, ke da na nemeki na rasa haka na yi miki, ba yawon nemanki na tafi ba? Wato baki damu da shi ba ko?" Ummi dai ta yi shiru ba ta ce komai ba.
Iya ta yi ta mata masifa, sannan ta fita, daga gidan, ta saka aka tafi kasuwa aka kirawo babansa, da sagir aka ce musu, ba a ga idiris ba.
Iya ba ta damu da tsawon kwanakin nan, ya ummi take ba, ta ci abinci ko ba ta ci ba, bata bi ta kan hakan ba.
Aka din ga yawon nemansa, wurin abokansa da sauransu, da ƙyar aka gano shi, can wurin wani abokinsa ya koma, a can yake kwana.
Iya ta same shi ta din ga zaginsa, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, mahaifinsu ma kamar zai kai masa duka, saboda takaici da ɓacin rai.
Hashim kallon su Iya yake yi, yana tausaya musu ranar da hakkin ummi zai kama su baki ɗayan su, babban abun da yake ƙara bashi mamaki, irin yadda ba wanda yake iya yi wa musu a kan duk wani son zuciyarta.
Ummi ba ta san me yake faruwa ba, sai ma tunanin Allah ya sa Idris yana lafiya, tun da an ce tun ranar ɗaurin aure ba a sake ganinsa ba.
Da ƙyar tayi sallar la'asar, saboda yunwar da take ji, cikinta sai ƙugi yake yi, har wani jiri take ji idan ta tashi, ban da ruwa ba abun da ta sha, tana son fita nemawa kanta mafita, amma an ce idan ta fita ba da izinin Idris ba, Allah zai ƙonata, gashi kuma tana son komawa makaranta, amma ba ta ganshi ba balle ta tambaye shi.
Sallamar yaro ta ji, tayi sauri ta fito daga ɗakin, wani yaro ta gani da kwano, ya ce mata "Gashi in ji mamanmu" saboda ƙuruciya da yarinta, ummi ba ta tambayi daga ina ba, ta karɓa ta ce ta gode.
Dafaffen rogo ne, da ƙuli-ƙuli, ko wanke hannu ba ta yi ba, ta hau rogon nan da ci, saboda yunwar da take ji.
Ta gode wa Allah bayan ta kammala, duk da ba ƙoshi tayi ba, saboda ɗan kaɗan ne aka zubo shi a kwano.
Ta fito da kwanon tsakar gida, ta saka ruwa tana girgijewa, dan ba ta da ko omo.
Kamar wanda aka cillo, ta ga idiris ya shigo, babu ko sallama, hannunsa riƙe da jakar kayansa, wata irin nannauyar ajiyar zuciya ta yi, saboda faɗuwar gaba da tsorata.
Babansa da yake bayan sa yayi sallama, ummi ta amsa ta tsuguna ƙasa ta ce "Baba ina wuni?"
"Lafiya ƙalau, ya gidan?"
Kai a ƙasa ta amsa masa da "Lafiya lau".
"Gashi nan, duk ranar da bai kwana a gidan nan ba, da safe ki je gida ki sanar da ni, zaka ga yadda zan yi da kai, mutumin banza wanda bai san abun da yake yi masa ciwo ba, an lallaɓa abun nan a rufawa juna asiri, ka daina ɗaukko mana magana, amma kana ƙoƙarin tona mana asiri" mahaifinsa yayi masa kaca-kaca, sannan ya tafi.
Ummi ji ta yi kamar tabi bayan sa, dan ta wani fannin zamanta ita kaɗai babu Idris shi ne rufin asirin ta.
Ta ajiye kwanon da take ɗaurayewa, ta nemi wuri can a tsakar gida ta zauna, tana ta addu'a a zuciyarta.
Idris kuwa ya cika yayi fam! Kamar ya fashe saboda tsabar baƙin ciki da takaici, fuskar ummi kawai idan ya kalla, ji yake kamar ya shaƙeta ta mutu, me zai yi da wata ummi, mummuna kamar ba bil'adama ba, aba kamar bayan garwa.
Tsaki yayi ya fito zai sake fita, aikuwa ta sake razana, kai tsaye inda take ya nufa, ta fara ƙoƙarin miƙewa tsaye, ya sanya ƙafarsa ya tankaɗata ta faɗi ƙasa.
"Shine ki ke je ki ka gaya musu bana kwana a gidan nan ko? Idan na kwana a gidan uwar me zan yi miki?"
Da sauri ta girgiza kai ta ce "A..aA'a iya ce ya aiko nemanka, wallahi ba faɗa na yi ba" tayi maganar cikin rawar murya.
"Rufe mini baki" yayi maganar yana dukanta a ka da hannunsa.
Ta saka hannu bibbiyu ta dafe kanta, saboda jin zafin dukan da tayi, dan ma Allah ya taimaketa, tudun gashinta bai bari ta ji zafin sosai ba.
"Idan ki ka kuskura ko da wasa, ki kai ƙarata, sai na yanka ki, kuma azabar da zan gana miki, sai kin gudu da ƙafarki, ke baki san yadda na tsaneki ba ko? Zaki gani yanzu ai, banza mai kama da dabbobi"
Kame jikinta take sake yi, saboda gudun kar ya kuma dukanta, aikuwa sai da ya sake takata da ƙafarsa, sannan ya fita.
Sai da ta tabattar ya fita, sannan ta iya ɗagowa a hankali, ta bi hanyar da ya fita da kallo.
Ta kalli jikinta, da ya ɓata mata da ƙasar takalminsa, tun da tazo gidan sau ɗaya tayi wanka, shi ma ba soso babu sabulu. Kayan jikinta tun wanda ta zo da su ranar da aka kawota, Iya ta ce za a aiko mata da kaya, amma shiru.
A hankali ta saka hannu ta karkaɗe ƙasar, tana takaicin yadda ya ƙasƙantar da ita ta hanyar takata da takalminsa mai datti da taɓo.
Tayi shiru tana ta saƙe-saƙe a zuciyarta, ta haɗe gwiwoyinta, ta kifa kanta, ta nemi hawayen ma ta rasa, sai zafi da ƙunar zuciya.
Yaya Hashim bai zo ya ganta ba, maman na'ima ba ta zo ba, tayi ta lissafin mutanen da take sanya ran su zo su ganta, amma basu zo ba.
***
A ɓangaren mariya kuwa, tuburan depression ya zame mata hauka, ga ta dai a nutse, sai dai babu cikekken hankali, wasu lokutan sai hankalin ya dawo, ta yi ta harkokinta, amma da abun ya juyo, sai daina cin abinci, ta daina magana. Duk wanda ya shigo da ƙaramin ɗa gidan, sai ta ce sai an bata umminta, ko ta ɗauki fulo tana yi masa wasa, ta ce ummi ce.
Idan ƴan yara mata suka shigo gidan, suma sai tayi ta kiransu da sunan ummi. Ta ce "Yaya ɗanlami, kalli yadda ummina tayi wayo ta girma".
Ya amsa mata da "Tubarkallah, ki yi ta yi mata addu'a, Allah ya ƙara rayata"
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Ba ummi ba ce, ummina baƙa ce mai kyau, bari in tashi in zuba ruwa in yi mata wanka, na goyata garin nan da sanyi"
Yayi saurin tashi, ganin da gaske tana ƙoƙarin kama ƴar mutane ta yi mata wanka, ya ce "Ki yi haƙuri in anjima sai ki yi mata wankan".
"To ai bana son babanta ya dawo ya tarar da mu, ba mu yi wanka mun yi kwalliya ba, kaga yana son turare da lallen da nake yi masa, baban ummina har kayan kasuwa yake sayo mana" haka tayi ta gwamutsa masa zantuka.
Yayi shiru yana kallonta, ba zai manta zuwan ƙarshe da yayi gidan Iya ba, da yaje da maganar neman alfarmar ɗaukar ummi, ko na ƴan kwanaki ne, dan hankalin mariya ya kwanta, ta fara samun matsala a ƙwaƙwalwa, amma ta kada baki ta ce Allah ya ƙara, hauka yanzu ta fara da yardar Allah sai ta din ga bi bola-bola hakkin ran ɗan ta ne.
Tun daga nan yayi alwashin ummi ko ƴar gwal ce ba zai kuma zuwa da niyyar a bashi ba.
Mama ta fito ta taya shi lallaɓa mariya, suka mayar da ita ɗaki, sai surutai take, tana basu labarin baban ummi da kuma ummi, sai dai ko da wasa ba ta zancen Iya, ko sauran mutanen gidan sai ummi da babanta.
Ummi ta sakankance idiris ba zai kwana a gidan ba, dan haka har ta hau kan tsurar katifar ta kwanta, sai dai ta kasa rufe idonta tayi bacci, saboda tana jin tsoro, ga gari hadari na ta haɗuwa, sai addu'a take Allah ya sa kar ayi ruwan sama.
Sai da hadarin ya haɗo gaba ɗaya tare da iska, kawai ta ga hasken tochlight a tsakar gida, inuwar Idris ta hango, ya tunkaro ɗakin. Ta runtse idanunta, tana fatan Allah yasa ba shi bane ba, sai dai ta ji ya mayar da ƙofa ya rufe, hakan ya tsananta bugun zuciyarta.
Ba ta san me yake yi ba, saboda ta rufe idonta, ƙafafuwanta ya taka ya ce "Ke dalla tashi" yayi maganar a matuƙar kausashe cikin rawar jiki ta motsa, ta tashi zaune, me zata gani Idris a tsaye a kanta tsirara kamar mahaukaci.
Ihu ta saki, ta runtse idanunta ta dafe kanta da hannayen ta.
"Dalla malama rufe mini baki, ki tashi na ce, uban meye baki sani ba? Munafukar banza da ta wofi, maƙaryaciya an cuceni an haɗani da saura, har da zuwa ki gaya musu bana kwana a gida, ai na san kin san komai kin saba".
Kyarma ta fara yi, taƙi motsawa, aka kece da wani irin ruwan sama mai ƙarfin gaske, ba ka jin komai, sai sautin zubarsa da ƙarfin gaske a kan kwano.
Ganin za ta ɓata masa lokaci, ya sanya ya jefar da fitilar hannunsa yayi kanta, kamar zararre.
Ayshercool
08081012143
*CUTARWA!*
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
BRIGHT PENS
(FREE BATCH)
P12
Kamar mai shirin tarayya da dabba, haka yayi kan ummi, ya fara yage suturar jikinta, yana ja tana ja, tana ihu tana bashi haƙuri.
"Ba zaki rufe mini baki ba?" Yayi maganar cikin fusata.
Warin bakinsa ya daki hancin ummi, kai ka ce an buɗe masai.
Sai dai ba ta gama shaƙe warin bakinsa ba, warin gashin kanta ya daki hancinsa, gashi ne fal Allah ya bata shi, sai dai kasancewar babu gyara babu tsafta, ya sanya yake wani irin tsami mara daɗin shaƙa.
Sai da ya ware gashin ya sauka bayanta, warin ya ƙaru har wani gafi gashi gashin yake yi, saboda tururin warin dauɗa da ƙazanta.
Ƙyale gashin yayi, ya cigaba da ƙoƙarin rabata da suturar jikinta, sai dai nan ma jikin ummi, warin dauɗa yake yi, da tsamin gumi, saboda rashin wanka da kula.
Har ɗauke numfashin sa yake yi, ita kanta ummin warin hammatar idiris ɗin ya hanata sukuni, yafi ƙarfinta nesa ba kusa ba, amma ba ta gaza ba wurin ƙoƙarin kare kanta.
Duk da a duhu ne bai hana shi, kifa wa ummi mari ba da dukkan ƙarfinsa, Allah ya sa hannunta ya samu ba fuskar ba, amma sai da ta gigice.
Marin da yayi mata ya sanya ta saka kataɓus, har ya cimma in da yake burin zuwa, sai dai wari da ƙarni mai haɗe da zarni ya bugi hancinsa sai da yayi baya, take ya ji cikinsa ya yamutsa masa, kamar zai yi amai, nan da nan zuciyarsa ta fara tashi.
Duk yadda ya so ɗauke numfashin sa ya kasa, wani irin baƙin ciki da takaici ya ninku a zuciyarsa, ya laluba ya ɗaukko fitilarsa ya hasketa, ta kare jikinta sai kuka take yi.
Ya tashi ya rufeta da duka, abun da ta fi tsana, ya din ga takata da ƙafarsa, sannan ya janyota ya hankaɗata waje ana wannan ruwan saman, ba tare da imani ko tausayi ba. Kuka take iya ƙarfinta, tana danna ƙofar ɗakin, amma ya saka sakata ta ciki.
Tsakar gidan ya shaƙe da ruwa, saboda rashin magudanan ruwa a unguwar.
Jikinta duk ya yage mata sutura, kuma a haka tsirara ya hankaɗota waje cikin ruwan sama.
Ga wani irin tsoro take ji, balle ta tafi ɗaya ɗakin, haka ruwa ya din ga dukanta tana kuka. Tun tana saka ran ruwan zai ɗauke, har ta zubawa sarautar Allah ido, ƙafafuwanta suka gaji saboda tsayuwa, ruwan saman nan ya ƙarasa zuba a kanta.
Ta din ga buga ƙofar ɗakin a hankali ta na cewa "Dan Allah yaya idiris ka buɗe mini na ɗauki kayana, sanyi nake ji dan Allah" tayi bugun har ta gaji, jikinta ya din ga wata irin karkarwa saboda sanyi.
Ruwan, bai gama ɗaukewa ba, ta fara takawa a hankali ta na ƙanƙame jikinta saboda ƙyanƙyamin ruwan da ya kwaso dagwalon unguwar ya shigo ya taru a gidan.
Ɗaya ɗakin ta nufa, sai dai kasancewar ba taga babu ƙofa, a buɗe yake, shima ta tarar ya malale da ruwa, babu in da za ta zauna, ta samu wuri ɗaya ta raɓe tana cigaba da kuka.
Har garin Allah ya waye ummi na tsaye, babu wurin da zata raɓa ta zauna, saboda an yi ruwa ba ɗan kaɗan ba.
Gari ya fara haske tana sanya ran ya buɗe ƙofa ta suturta jikinta, amma bai buɗe ba, ta din ga fargabar kar a zo gidan a tarar da ita jikinta babu sutura.
Sai da gari yayi haske tar, sannan ya zare sakata ya fito ya shiga banɗaki, tana hangen sa ta taga, ganin ya