Showing 123001 words to 126000 words out of 214133 words

Chapter 42 - CUTARWA AYSHERCOOL COMPLETE HAUSA NOVEL

01 Sep 2024

22057

zaci da gaske ba, sai da ta ga su Alhaji Tahir sun zo.

Alhaji Tahir ya koma gida, ya kira mami sashinsa, Hajiya na tare da shi, sai dai bai gaya mata ba ita ma, sai da Mami ta zo, ta tarar da su ta wani haɗe rai tana harare-harare.

Alhaji Tahir ya ce "To ke fa abun arzki ya same mu, ban sani ba ko mun yi laifi"

Mami ta ce "Meyafaru?"

"Babban mutum ya zo mini da magana, ya je zance an ritsa shi an ce in je in gabatar da kaina idan da gaske yake, dan yau ma daga can nake da ni da su Alhaji Hamza, nan da sati biyu zamu koma mu kai kuɗin aure"

"Ikon Allah, kuma shi ne ba a saka ni a maganar ba sai yanzu?"

Hajiya ta ce "Masha Allah lallai babban mutum an girma, Ubangiji Allah ya sa abokiyar arziki ce, Alhaji a ina take zan yi shishshigi"

Alhaji Tahir ya ce "Au kema babbar aminiyar ta sa bai gaya miki ba? Wai wata yarinya amm.. ammi ne sunan nata ne ko ummi ne, wai ƙawar maryam ce dai".

Hajiya ta ce "Laaa ko dai Ummi, Ummi dai da suka yi islamiyya tare?"

Ya ce "Yes of course haka ya ce mini"

Cikin tsananin mamaki da takaici mami ta ce "What! Wannan kwazgwamar yarinyar baƙa ƙirin?"

Ayshercool
08081012143



FOLLOW ME ON WATPAD VIA THIS LINK.

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

Masu neman free books ɗina, da free pages duk akwai a kan watpad account ɗina. Irinsu
Abduljalal
Wata kissar sai mata
Wuta a masaƙa
Cutarwa
Ƙanwar maza
Gaba da gabanta
Aƙidata
Ruɗin ƙuruciya

Zaku iya samun paid pages ɗin a Arewabooks @ayshercool7724. Ko ku tuntuɓe ni kai tsaye ta lambar wayata.
08081012143.

And also don't forget to subscribe my YouTube channel via this link.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ayshercool.

PAID ADVERT!.

Ina uwargida, amare, har ma da ƴan mata masu burin zama gaba gaba, wurin yin amfani da turarruka na kece raini, masu daɗi da ƙamshi.
Mafaka gidan ƙamshi da ke, Ring Rord western bypass kanawa park sun kawo muku

Oll types of Turaran wuta
Sandal
Halut
Irik
Difur
Gab Gab
Kajiji
Habil
Nabak
Humra
Kulakcha
Dilke da kalta
Kayan
Garan jiki
Muna turara
Kaya
Kujerar garan jiki
Kannada
Madarorin turare masu kamshi
Man garan gashi
Indai kamshine kuzo MAFAKA GIDAN KHAMSHI karshene Sai Sai kin zamo abin kwatanche
Ku nememu a wan nan no 08065728702 08025453921

*TALLA!TALLA!TALLA!*
*INA MANYAN MATA, UWARGIDA DA AMARE KAI HAR DA ƳAN MATA MASU SON KECE RAINI, DA SHIGA TA ALFARMA, MUN SHIRYA TSAF DOMIN KUWA MUN TANADAR MUKU LAGOS LACE MANYA DA ƘANANA, DAIDAI ALJIHUNNKU BA TARE DA TSAUWALAWA BA* *HAKAZALIKA INA MASU SON ƘAWATA GIDAJENSU DA HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN, UNIQUE DA SAI AN KALLA AN SAKE KALLO, MUN TANADAR MUKU HAƊAƊƊUN KAYAN KITCHEN NA ALFARMA NA GIDA DA NA WAJE*.
*BAMU TSAYA IYA NAN BA, DOMIN KUWA MUNA SAYAR HAƊAƊƊUN SUPPLEMENT NA GYARAN JIKI, MAYAR DA TSOHUWA YARINYA, GYARAN JIKI DOMIN DAUWWAMAR DA HASKEN TAURARUWARKU A WURIN MAZAJEN KU, TARE DA KECE RAINI A CIKIN SA'ANINKU*
*MUN SHIRYA TSAF DOMIN SHARE MUKU HAWAYNKU, DOMIN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU A KAN LAMBAR WAYARMU 08166117985, SAYEN NA GARI MAYAR DA KUƊI GIDA*

BRIGHT PENS A SHIRYE MUKE, WURIN KARƁAR TALLACE TALLACENKU CIKIN FARASHI MAI SAUƘI.

                        *CUTARWA*

*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143

MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.

32

Alhaji ya ce "Meye kuma na wata kwazgwamemiya baƙa? Ba mutum ba ce ba?"

"Ban gane ba mutum ba ce, ta girme shi fa ƙawar maryam ce?"

Ya ce "To shi ne me? Idan har shi zuciyarsa ta nutsu da ita ba shikenan ba, ni na yaba da tarbiyyar gidansu"

"Wallahi da sake, tun wuri ma dole a janye wannan maganar. Na zaɓa masa yarinya ya ƙi sai ya jajibo wannan mummunar yarinyar? Gidan da take zaune ai ba gidansu bane ba, zaman boranci ta yi a gidan kamar ƴar aiki"

"To kin ga kya samu lada ma, idan ya aureta ya kula da ita"

Kamar zata kama da wuta dan bala'i ta ce "Wallaahi ba zan lamunta ba, shi ne dan munafunci ni bai gaya mini ba, kawai sai yau ka zo mini da wannan zancen, a'a wallahi"

Alhaji ya ce "Ni dai in kin ga na fasa zancen auren nan, sai dai in shi ne ya dawo ya ce mini ya janye ya fasa, amma ba zan zama mutumin banza ba, shima sai dai in yi masa jagora ya je ya samu ubanta ya ce masa ya fasa"

Hajiya ta ce "Banda abun ki, ai ummi yarinyar kirki ce, nutsatsiyar yarinya ce, shi kyau ba shi ne abun dubawa ba, nagarta ake da cancanta ake dubawa"

"Kin ga malama ki rufa mini baki, ban saka da ke ba, idan nutsatsiya ce, ki haɗata da makakkun yaranki mana, sai ɗa na dama na san wannan duk kitumurmurarki ce, ke ki ka shirya wannan abun aka yi ban sani ba"

Hajiya ta ce "Allah ya baki haƙuri, nima ban san zancen ba sai yanzu, kuma su makakkun ƴaƴa ba laifi na yi wa Allah ya bani ba, jarrabawa ce, kuma da da nutsatstse a cikin su na yi sha'awar sanya ɗaya ya aureta"

Har mami za ta yi magana, Alhaji ya yi mata wani mugun kallo, hakan ya sanya ta yin shiru tana huci.

Hajiya kuwa tuni hawaye ya cika mata ido, tana jin zafin gori da cin mutunci da mami ke yi mata a kan yaranta, gani take yi kamar dabarar ta ce ta sanya Allah ya bata shiryayyun yara.

Alhaji ya kalli mami ya ce "Tun da kin saka mini mata kuka, sai ki bani wuri zan kula da ita"

Maganar ta sa ba ƙaramin fusata mami tayi ba, ta tashi ta ce "Haɗiyeta ƙarewar soyayya" tayi waje fuu rai a ɓace.

Ya dubi hajiya da hawayen fuskarta suka fara zubowa, ya rungumota jikinsa a hankali ya ce "You are brave woman, kar ki karaya, ki yi haƙuri ke ce fa mai Kwantar mini da hankali da rarrashina, ki yi haƙuri in sha Allah zaki ga tanadin da Allah ya yi miki sakamakon haƙuri"

Ɗan ƙara sautin kukan nata tayi, hawayenta ya ɓata masa riga, amma bai damu ba ya cigaba da rarrashin ta.

Kira uku raihan ya yi wa ummi sannan ta ɗaga, tayi masa sallama.

"Meyasa baki ɗaga ba, missed calls uku fa na yi miki"

"Ina aiki ne a kitchen, wayar tana ɗaki"

Raihan ya gyara kwanciyarsa ya ce "To ya ki ke sweetheart" wata irin kunya ce take kama ummi, idan ya ce
sweetheart ɗin nan, wai raihan ke ce mata sweetheart abun da kunya.

"Ba zaki amsa ba?"

"Ina lafiya" ta amsa a taƙaice.

"To yaya, su Alhaji sun zo ko? Na ga ya dawo ɗazu ina jiran ya kira ni ne"

A sanyaye ta ce "Eh sun zo"

"Yauwwa masha Allah, daga nan zuwa kowane lokaci zaki zama matata baby"

Ummi ta ce "Dan Allah ka din ga ce mini ummi kawai ko salma"

Raihan yayi murmushi ya ce "Ba kya son babyn saboda me? Ba daga bakin yaro kamata ki ke son ji ba ko? Kar ki yanke mini hukunci a yanzu, ina da kyakywan tanadi a kanki da rayuwarki ummi, zaki ji daɗin zama da ni sosai da sosai ki yi ta yi mana addu'a kin ji my Salma".

Ta amsa masa da "To" amma tunanin yadda za ta yi rayuwar aure da raihan take yi, ita yanzu gaba ɗaya ma kunya yake bata.

Faɗowar mami afujajan ɗakin ya sanya shi tashi zaune, ya ce "Zan kira ki" sai dai kan ya katse wayar ta ce "Sannu shashasha, ni zaka je ka aurowa wannan mummunar yarinyar?" Kan ya katse wayar ummi ta ji me mami ta ce.

"Mami meyafaru ne?"

"Uwarka da ubanka ne suka faru, in ce maka ga safiyya ka aura amma ka yi burus, ka je ka kwaso wannan yarinyar uwar mata ka yi yaya da ita? Ta girmeka ba sa'arka ba kawai saboda baka da hankali ko dan ba ka da mafaɗi?".

Raihan ya ce "Mami, dan Allah ki kwantar da hankalinki, duk fa ba abun ɗaga hankali bane ba. Ke ki ka gabatar mini da ita da kyawawan halayenta, na ji ina jin tausayinta. Ki ka kawo mini maganar aure na ga ita ta dace da ra'ayina, idan kowa ya ce ba zai aureta ba mummuna ce shikena sai ta rayu a haka, ba tausayawa babu kulawa?"

Rufe mini baki kan na daki bakin naka ya fashe, kai ne ɗan sarkin taimako, wani ya taimaketa mana a waje, ta girmeka ba sa'arka ba ce ba, ita ba ƴar uban kowa ba, kawai ka jajibo mana ita, to wallahi idan ma wannan matar ce ta zigaka dai-dai nake da ku. Kuma umarni nake ba ba shawara ba, ka je ka samu mahaifinku, ka janye wannan maganar da zancen auren nan da komai, dama ai ni na kawo maganar auren to safiyya na zaɓa maka, ita kuma ummin na san yadda zan yi da ita"

Cikin sauri ya ce "Dan Allah mami kar ki yi wa ummi komai, ni zaki yi wa ni na ce ina son ta, dan Allah kar ki sakata a damuwa, dan Allah mami ki yi haƙuri"

Galala ta saki baki tana kallon sa, "Au kar in sakata a damuwa? Har abun naka ya kai haka kenan? Dole na san abun yi"

Ta juya ta fita.

Ummi kuwa a hankali ta sauke wayar hannunta, fes abun da ta ji mami ya faɗa yake dawo mata, tabbas! Ta san a rina ta san zata fuskanci wannan ƙalubalen, tayi ta ƙoƙarin ankarar da raihan, amma bai gano ba, ta san yanayin mami ƴar ƙarya ce, mace ce mai iyayi da son nuna isa, ta san dama abu ne mai wuya mamin ta amince.

Dr. Ya yi sallama a ƙofar ɗakin ummi, ta amsa masa ya shiga, ya kalleta cikin farinciki da kulawa ya ce "Ummana, ke ashe ɗan manya ki ka samo mini siriki, ai ni gatse na yi wa saurayin naki, ganin yayi yarinta da yawa, na ce ya turo mini babansa ni na ma manta, kin ga sai ga su sun zo" Ummi ta yi shiru ta sunkuyar da kai, tamkar ta ce wa dr. Dan Allah ya warware maganar.

"Alhamdilillah, ina jin labarin Alhaji Tahir ashe babban mutum ne, mutumin kirki ne, kamar ba mai kuɗi ba, yayi mini bayanin komai, na ɗeba musu sati biyu, zan ne na yi bincike a kansu da yaron, in dai lafiya ƙalau nan da sati biyu za su kawo kuɗin auren, Ubangiji Allah ya kusa kawo miki ƙarshen zaman gidan nan, Allah ya baku zaman lafiya, ya kawar da fitina.
Dama wani jinkirin alkhairi ne, ki kwantar da hankalinki ummi, kar ki ga yaro ne ƙarami, ki saka a ranki Allah ne ya duba ki, ya kawo miki miji.
Ita nagarta ba a shekaru take ba ko tarin dukiya, babban fatan Allah ya tabbattar da alkhairi, dama ke mai biyayya ce, dan haka ki ƙara dan sa'anki ne kar ki ce ba zaki bi shi ba, Allah ya sanya muku dukkan alkhairi"

Ummi a ranta ta ce "Ji kawu da wata magana, har da nasiha kamar an ɗaura auren, akwai ƙura fa' sama-sama take jin sa, ya gama nasiharsa ya fice.

Farida kuwa har Abdul ta tambaya, ko ya san suwaye baƙin dr., Amma ya ce mata shi ma bai sani ba.

Bayanin da Alhaji ya yi wa raihan ne ya rage masa damuwar abubuwan da mami ta yi masa.

Ya ɗora da cewa "Mahaifiyarka ta fara tutsu, a kan ba ta san lamarin, idan har da gaske kana son yarinyar kana son tainakonta, ka tsaya a kan hakan, ka cigaba da addu'a, ni dai yarinyar ta yi mini, ban ga aibunta ba, wani muni wani waye hotonta da ka nuna mini ban gani ba, ban sani ba ko dan kana sonta ba ka ga munin bane ya sanya nima ban gani ba.

Ka je ka cigaba da shirye shiryen ka, a duba fili ɗaya ka gina abun ka yadda ka ke so, ba wata matsala in sha Allah"

Cikin girmamawa raihan ya ce "Na gode sosai Alhaji, Allah ya ƙara maka lafiya da nisan kwana"

"Amin babban mutum"

Hajiya ta yi sallama hannunta ɗauke da tray, da kayan shayi a kai.

Tana ganin raihan ta ce "In fara guɗa tun yanzu ne, ko in ɗan jira?"

Murmushi raihan ya yi yana sosa ƙeya.

Hajiya ta zauna tare da faɗin "To kai raihan daga ganin ummi, har ce maka fa na yi wa ina yi wa yayanka kamu, kawai sai ka lallaɓa"

Ya ce "Wallaahi hajiya tausayi take bani a lokacin, na din ga damunta har muka fara sabawa. Hajiya ummi na da matuƙar kirki da tarbiyya"

Hajiya ta ce "Sosai kam, ina fatan Allah ya sanya alkhairi, na yi maka murna raihan, in dai mace ta gari ake nema, aka samu ummi to a gode Allah.
Sannan shekarun da ke tsakanin ku ba abun damuwa bane, shekaru lambobi ne kawai, ka riƙe ta ka kula da ita, ni dai ina son ta saboda Allah, tun tana zuwa gidan nan lokacin maryam tana nan, akwai ɗa'a da ladabi"

Raihan ya ce "Kuma wallahi ta iya girki sosai hajiya, ba ki ga yadda take bani abinci ba, ban taɓa cin abinci mai daɗin nata ba"

Alhaji ya dungure masa kai ya ce "Sannu ciki muka kawo duniya " suka yi dariya gaba ɗaya, gaba ɗaya sai ya manta da damuwar da yake ciki.

Ummi na zaune na tilawar litattafanta na addini, wayarta ta fara ringing, baƙuwar lamba ce, tayi zaton ko raihan ne, dan akwai canza lambobi.

Sai dai tana kai wayar kunneta, tayi niyyar sallama, ta gimtse sallamar jin uwar ashariyar da aka lailayo mata.

"Sannu asararriya ƴar wahala, baƙin kunurci, saboda asara da taɓewa kana da rashin kyakykyawar makoma, ummi ki rasa wa zaki ce zaki aura sai ƙanina ummi, na yi dana sanin saninki, saboda kin zama guzuma muni yayi miki katutu shi ne ki ka yi wa ƙanina asiri, saboda zalamar abun duniya, to wallahi ummi ki kuka da kanki, ko ki janye wannan maganar ta auren raihan, ko kuma in ƙasƙanta ki a idon duniya, in muzantaki kin san zan iya"

Jikin ummi yayi sanyi matuƙa, ta kasa magana, har maryam ta yi tijararta a waya ta gama, ta kashe wayar, kamar shashasha ummi ta bi wayar da kallo.

*Sweetheart, ki yi bacci cikin aminci da salama, zan so kiranki in ji muryar ki, amma na san wataƙila kin yi bacci, ki kula mini da kanki, ina son ki* message ɗin raihan ya shigo wayarta.

Ta miƙe ta tafi gaban mudubin ɗakinta, tana ƙarewa kanta kallo.

'to shi raihan ya aka yi baya ganin munina ne? A wajen ina munin nawa yake da yake ɓuya a idonsa baya gani?'.

Abu kamar wasa, mami ta sako raihan a gaba, ta daina amsa gaisuwar sa, ta daina shiga sabgarsa ta ce lallai sai ya je ya cewa Alhaji ya fasa auren nan.
Duk taurin kan ɗa, fushin uwa masifa ne, hakan ya sake jefa shi cikin damuwa da wasi-wasi, idan ta ce ya rabu da ummi, sai ya ji kamar ta ce ya raba jikinsa da rai.
Gefe Hajiya da Alhaji suna ta ƙarafafa masa gwiwa a kan auren ummi.

Ga lokacin kai kuɗi na cigaba da kusantowa, ga pressure office, ga ummi gaba ɗaya ta canza ta koma masa kamar wata baƙuwa, taƙi sakin jiki da shi, kamar ma ƙara nesanta kanta da shi take yi.

Yanayin aiki ya ƙara takura raihan, dan haka ko wurin aikin bai fiye samun damar binta ba, ga yawan barin ƙasar da yake yi.

Gefe guda maryam ta saka ummi a gaba da cin mutunci da zagi na cin zarafi kala-kala, ban da saƙonni da kuma barazana da take yi mata, ummi ta rasa in da za ta saka kanta, daga kuka sai addu'a, dan ta rasa yadda za ta yi da al'amarin gaba ɗaya.

Duk da mami ba ta shiga harkarsa, hakan ba ya hana shi zuwa in da take, da la'asar bayan ya dawo daga aiki, yayi niyyar zuwa yau ya je ya ga ummi, ya nufi sashin mami ya je ya tarar da maryam ta zo gidan.

Sanin halinta ya sanya ya tsuke fuska, dan ya san ba wai zuwan Allah da annabi ba ne ta yi shi haka.

"Mami barka da yamma" banza ta yi masa, daga baya kuma ta ce "Kar ka sake zuwa gaishe ni, muddin ba ka aiwatar da umarnin da na baka ba, bana buƙatar ganinka a sashina ma gaba ɗaya"

Maryam ta kalleshi ta ce "Wallaahi ka bayar da maza raihan, me aka yi aka yi ummi? Meye da ita meye abun burgewa a tare da ita? Sannan menene aibun Safiyya, amma na lura kamar ba a hayyacinka ka ke ba, wannan annakiyar baƙin zaka ɗaukko ka kawo mana mugun iri cikin family, wannan yarinyar da mujiya.....

"Dalla malama dakata!" Ya yi wa maryam tsawa.

"Islamiyyar da ki ka yi ba ta amfane ki da komai ba, da baki san daraja karramawar da Ubangiji ya yi wa ɗan Adam ba, ki tsaya iya matsayinki, idan mami tayi matsayinta ne, ke kuwa ko kusa ko a nesa ba ki da alaƙa da aurena, dan haka ki zuba ido idan zaki iya idan ba zaki iya ba ba zan juri cin zarafin matata ba, idan kin yi mata a baya ba ta da bakin ramawa, ni dai-dai nake da ke"

A tare suke shiga karanto "Innalillahi wa Innalillahi raji'un"

Mami ta ce "Au raihan har ta zama matarka ma ashe? Yanzu a gabana ka ke gaya wa ƴar uwarka haka saboda yarinyar da ba ka aureta ba ma? A wayance kana nuna mini babu gudu ba ja da baya kenan sai ka aureta" raihan ya yi shiru yana huci.

Maryam ta ce "Taɓɗijan, akwai ƙura mami, ita ma munafuka na kirata a waya ta ƙi magana, da yake ba ta da gaskiya, munafuka uwar son abun duniya, sumi-sumi da ita garin yayime-yayime na, na yayimo mana masifa"

Cewar ta kira ummi ya fi komai ɗaga masa hankali,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login