Showing 21001 words to 24000 words out of 30903 words

Chapter 8 - MIJIN TA CE BOOK 3

20 Aug 2024

4869

mashin din a kofar gida na
ce ba zan sauko daga kai ba sai ya juya ya maida ni
Tukunya kamar yanda yayi alkawarin kai ni.
Ya soma rarrashi yaga alamar ba zan yarda ba,
sai kawai naji ya ce min, kine dai so ne kawai ki nuna
wa mutanen da suke zaune gindin bishiyoyin can
cewar eh da gaske ne kin fi karfina.
Kin ga sai suma su yarda da magánar da matan
cikin gida suke yadawa cewar ni din MIJIN-TACE
ne, ban sani ba ko Ado ya gane irin dukan da wannan
kalmar ke yi wa zuciyata ne in an fade ta yasa ya
gaya min hakan, don a firgice na sauko daga kan
mashin din na shige cikin gida, naje na tsaye bakin
kofa ina jiran yazo ya bude min in shiga.
Sai dai a gidan ban yarda kun zauna lafiya ba,

110
saboda na riga na gaji da yanda yake tsattsare ni yana
kokarin hana ni mu'amallah da kowa da kowa, har da
mutanen da nake tare dasu, wadanda matan yan
uwanshi ne.
Muna cikin wannan rikicin, Ado ya samu aikin
koyarwa a Makarantar Secondaryiyanmata ta
DANJA', shi kenan sai murnan samun aiki yasa
muka shirya.
A farkon samun aikin murna nayi ba kadan ba,
saboda ni da shi addu'a sosai muka yi akan aikin,
saboda irin bayanin da ya rinka yi min cewar, aikin
koyarwar shi ne aikin da yafi so a wannan lokacin,
saboda irin alherin da ke cikinshi.
Za ka koyar da yara mutanen da suke sune za su
girma, su zama al'uma ta gama shi a wurinshi babu
wani aiki da yafi koyarwa dadi, da kuma
muhimmanci aikin ne mai lokaci ga kuma. lokuta
daban-daban na hutu wanda zaka iya aiwatar da wasu
l'amuran naka da basu shafi Makaranta ba a lokacin.
Koda dai a wannan lokacin da muke ciki, ba
wani muhimmanci hukuma da wasu Jama'ar gari
suke baiwa Malami ba, shi a wurinshi darajar Malami
ba sai wani ya ce gata.ba, tunda Ubangiji da kansa ya
girmama shi.
Irin wadannan kalaman nashi ne suka kara cusa
min son aikin nashi, amma yana farawa ba a dauki

111

wani lokaci mai tsawo ba na gane ba sakandaren
'yanmata ba ne ta kamata a tura min mijin mawa ba.
Don ba a je ko ina ba na soma gani wasikun
yanmata da hotunansu a cikin Jakarshi ga waya akai-
akai, ga text na kalamai masu dadi irin ma wadanda
ban taba jin su ba.
A farkon al'aarin yana rarrashina ya gaya min
kalamai masu dadi da yake rage min 6acin raina,
amma daga baya sai kawai ya daku wai shi ba zai
dauwama kan rarashi da ban baki kan matsala guda
daya ba.
Don haka hanya mafi sauki ta neman zaman
alfiya kawai in daina yi mishi bincike in daina taba
mishi jakarshi ta zuwa aiki da kuna wayarshi in ban
taba su ba ai ba zan ga abinda ke ciki ba.
Kan ka ce meye wannan kuma sai ya fito da wata
ka'ida ta cewar, wai shi din tafiya tana yi mishi
yawa, kullum sai yaje Danja yayi aiki ya dawo
Dabai.
Don haka ba zai juri hakan ba, wahala tana yi
mishi yawa, maimakon ace kullum yana zirga-zirga
kan hanya da safe da yamma zai maida tafiyar tashi
ta zaa ranar Litinin da safe.
Ba zai dawo ranar ba sai ya kwana ya bada
darussanshi na ranar kala ta in an tashi sai ya dawo
ya kwana a gida, sai washegari aba ya koma da

112
safe ya kwana ranar ya wayi gari a can Alhamis in ba
shi da wani darasi na ranar Juma'a to ranar zai dawo.
Ba zai sake komawa ba sai ranar Litinin in kuma
yana da shi Juma'a to sai in yi hakuri sai Juma'ar zai
dawo.
A farkon bayanin nashi banga wani abin damuwa
a ciki ba don yayi min bayani sosai kan wahalar
zirga-zirga a hanya amma yana fara aiwatar da abin a
haka mutanen gida suka gane shi kenan sai aka soma
kace-nace.
Ya samu wata a can kenan ya ajiye, nan da nan
hirar gidan ta koma hirar mazan da ke ajiye mata a
waje, wato matan banza.
Cabdi! Ai gara mana irin namu mazan da ke
shigo mana da abokan zamanmu cikin gida suci daga
abinda muke ci, shi din kuma gashi nan a tsakaninmu
ya dai ishemu muna kuma kallonshi.
Amma matan banza hidimar da ake yi musu ai ba
irin ta nmatar gida ba ce, ga kuma ciwace-ciwacen nan
na zamani."
A wannan lokacin in na ce bana cikin tashin
hankali to nayi wa kaina karya, gashi dai a wannan
lokacin nayi matukar wadatuwa da abubuwan
rayuwa, komai da Ado yasan zan bukata ko zai yi
min amfani kawo min yake yi.
Albashinshi na farko ma da aka fara bashi saboda

113
anyi mishi biyan na wata uku ne gaba daya kamar
yanda all'adar aikin Gwammati take, kananan atamfofi
masu saukin kudi masu kyau turmi goma ya saya
min.
Ya bayar duka aka dinke min, dinki kuma mai
kyau ga takalma da gyalulluka da under wears, a
wannan lokacin kuma tuni ya canza min tsarin
abincina, a kowane lokaci ban rabuwa da madarar
fulani da shi yasan inda yake zuwa ya samo ta.
Bana rabuwa da naman kaji, bana rabuwa da
kayayyakin itace dangin kankana, gwanda, inabi,
lemo, ayaba, in zai kawo kumá masu kyau zai kawo
min. gashi kua ya tsare mnin girkin gidan.
Kullum ya zagayo kaina ko baya nan Furerah
zata yi don zai sa a kawo mata kudin cefanen ya ce
tasa a sayo wanda ta mafi son hakan.
Jikina yayi matukar yin kyau saboda yana samun
nau'o'in abincin da ya dace ya samu, amma na kasa
yin kiba in maida jikina ya zama kamar asalin yanda
nake kafin zuwan mu.
Sai ma kara ramewa nake yi saboda kullum a
cikin fargaba nake. Ni kuma gashi duk da wadatar da
Ado ya samu ban koyi adana ko kwabo a dakina ba,
hamsin-hamsin din da su. Baba suke bani yana ganin
sun taru zai sa hannu ya kwashe in ma bai diba ba in
dai ana zaune kalau ni da kaina ma zan ce mishi ga

114
Su.
Sai a lokacin da raina ya soma baci ne zan rinka
ganin ina ma adana abina nake yi da nayi amfani
dasu na tafi gidanmu.
Rannan abin ya ishe ni, bakin cikin Ado yana
nema ya maidani wata iri Alhamis ya zo bai dawo ba
na zuba ido ban gan shi ba cikin zuciyata na ce to
watakila sai Juma'a kenan.
Yayi sammakon dawowa don wani lokaci yakan
yi hakan sai kawai naga Bala da sassafe ya kawo min
cefane wai a gaya min sai gobe zai dawo ya tsaya
daurin auren Jalo.
A zuciyata na ce tafdijam! Wato ni babu abin da
nasan darajarshi irin ciki, don haka cefane na gashi
nan an kawo min babu fashi shi sai sanda yaga dama
zai taho.
A cikin gida kuwa rannan maganar da su
Ruwailah suka wuni suna yi kenan, amma akan wai
ban da ni ake yin hirar ba tunda ni da 'yan dakinta
ma ba wata doguwar magana ke hada mu ba.
Don ko nayi musu a lalace suke amsa min, ko a
yanzu da rashin Ado ke sani zaman cikin gidan wani
lokaci da sauran mutanen gidan muke hira, amma
yan dakinta ta hana su kula ni.
'Ko da yake dai nima ko da baya nan din na stare
dokarshi ta shiga dakin mutane, bana shiga dakin

115

kowa. Ina jin ta a gindin bishiya tana fadin au, to shi
namiji don ka tsare shi ka hana shi yin aure ai ba
wata birgewa ba ce.
In har baka hana shi ganin na banza ya ce yana
So ba, ta tsirtar da yawu nuna alamar kyaa, ta ce ni a
yanda nake da kyaman nan ai ba zan 1ya zama da
manemin mata ba.
To me zan yi da shi? Ai komai zai bani gara ya
bar shi ya tsare min mutuncin kanshi kawai yafi min,
ni nayi sana'ata in nemi abin da zan rufawa kana asiri
dashi.
Sannan abin tsiyar shi ne, sma kara kullewa a
can tana karakwace maka shi. In a farko kana
ganinshi şau uku a sat sai a koma biyu sai a koma
daya wani satin ma sai ka ji shiru.
Ai gara a hada mu mu hudu a gida kishiya dai
kowacce tazo Ubangiji zai bani hikima da basirar
zama da ita, in ta kunso wani abin tsiyarta ma a wayi
gari ya koma mata kanta ko ya kare tsakaninsu can
musu ita da wanda ya kawo ta, aifa kam- aifa kam
abin da yan amshin nata suke fadi kenan.
Rannan da daddare Inna ce na runtsa ta karya na
yi wa kaina. Washegari tun safe Ado ya dawo ya yi
sa'a kuma a wurina yazo ya same ni ban riga na rufe
na tati wurin hira ba.
Karbar da nayi mishi bata wani ba shi sha'awa

116
ba baki da lafiya ne? na kalle shi da gefen ido na
tambaye shi me ka gani? Yanayin ki ne na ganshi
wani iri.
Na ce ta dauro ne ka ganshi a haka ka kuma san
daurowa take yi a daure AIkali. Ya ce haka ne, to ga
leda nan nazo da shi juye abin da ke ciki don ba zai
juri zafi ba.
Na mike kamar zan juye abin da ke ledar na
wuce na tafi tsakar gida abin ban sake dawowa dakin
ba. A tsakar gidan kuma sai tambayeta ake yi ana
fara'a ashe maigidan ya dawo?
In ce eh sai ace kai madallah, hannunshi da
zuwa. Ina nan wurin a. zaune sai ga Ado ya shigo
suka gaisa da matan duka ya kalle ni cikin natsuwa
ya ce min zo mana Hunmaira, na ce to.
Na tashi na bi bayan shi don komai yaya ba zan
iya wulakanta mmijina a gaban wani ko wasu ba.
Muna shiga ya kalle ni ya daga ido ya kalli
agogo sannan ya sake kallona ya ce min, kin ga
wannan abinda ki ka yi min na farko kin yi min kuma
na karshe kin gane? In dawo daga wani wuri baki
karbe ni ba baki yi mi abida ya dace kiyi min ba.
Ki tafi ki bar ni awa guda minti sittin ina zaman
Jiranki, na yau din ya zama na karshe kar ki sake. Na
ce Inna sake din me zai faru? Ko me zaka yi?
Ya ce to ki sake mana ba ga ki ba gani? Na juya

117

da nufin sake fita, yayi maza ya kamo ni ya murde
min hannu, nayi karfi hali ban yi irin ihun da nakan
yi ba alamar na riga na saba da wannan wahalar.
Kar ki neme ai da fitina Humaira, bana so. Yana
ta nanata kalmar alamar bai son fadan da ya gane ina
so muyi. A zuciyata na ce ya san ba shi da gaskiya.
In wani abu nayi miki a laifi ki gaya min bai
zama min komai ba in ba ki hakuri ke kin san na saba
hakan bani da wannan girman kan me nayi miki?
Kullum naje aiki na dawo sai kin yi min sanadin
bacin rai?
Saboda kawai bana gida kina shiga cikin matan
da suke cusa miki ra'ayin da ba naki ba suna koya
miki abinda bai dace ba, wanda ban taba zaton zaki
yi haka ba, ke da ki ka girma a gida irin naku ki ka yi
karatun boko da na addini har yanzu ma kina yi.
Amma wai wadannan matan ne suke koya miki
abinda za ki yi wa mijinki.
Kalamanshi suka sanya ni bude baki na ce mishi
ni babu wata wacce take koya min wani abu,
halayenka da dabi'unka ne kawai suka gundure ni.
Ya dan saki fuskarshi kadan alamar bacin ran nashi
ya dan ragu.
Yana kallona cikin natsuwa ya ce wadanne a
Ciki? Ko duka? Ban amsa ba, sai ya ce to tunda ma
halayena ne matsalar ai duk ta kwana gidan sauki,

118
tunda ba cusa miki wani ra'ayi a kaina ba
Magana kawai zaki yi ki ce min Ado ko Kawun
da ki ke kirana halinka kaza-kaza da dabi'arka iri
kaza da iri kaza basu min ba, ka canza sai in ce miki
to.
In kuma canzan tunda ke ma sheda ce ni mutum
ne mai saurin canzawa daga wani matsayi in koma
wani ko daga wani hali zuwa wani duk ina iyawa,
don haka mu bar wannan maganar yanZzu anjima sai
muyi ta.
Yanzu zo kiyi min tausa in dan ji dadi in
wastsake gajiyata ta wannan satin kin kuma san
wannan karon kwana hudu nayi bana gida,
maimakon daya ko biyu da nakan yi.
Ko kallonshi ban yi ba kaina a sunkuye na ce
mishi can inda ka baro ba. ayi maka tausar ba ne?
maganar da nayin tayi matukar dukan Ado watakila
bai taba zaton ina yi mishi irin wannan zargin ba, ni
ayi min tausa a inda na baro Humairah me ki ke nufi?
Kina yi min mummurian zato ne? na ce kana yi
wa kanka, dai in ba haka ba me yake zaunar da kai?
Me yake tsareka daga dawowa gidan ka? Rikici sosai
muka yi saboda ranshi ya kai matuka wajen 6aci da
zargin da nayi mishin.
Amma duk da haka yayi kokarin hadiye fushin
shi ya zaunar da ni don yayi min bayani.

119

Tafiya nake yi Litanin in dawo T'alata in koma
Laraba in dawo Alhamis ko Jumaa in kin yi lissafi
da kyau za ki ga sau biyu ne kawai ko uku ba na
kwana a gida a sati.
A haka kuma kullum kina ganina ko kuma kiyi
fashin ganina sau daya to menene? Na kuma gaya
miki a gidan abokin aikina iro nake kwana wannan
satin kuma jalo ya kara aure na tsaya tunda mune
abokan ango.
Na ce gaskiya ban yarda ba sai dai cikin biyu ka
zabi daya ko dai ni in bika mu koma can ko kuma
kullum kaje ka dawo cikin natsuwa ya ce min ba zai
yiwu ba.
Humaira kina karatu kina aji shi da ba za ki bar
karatunki ba, sannan a can din ma ai ba ni da in da
zan ajiye ki sannan ni in yi ta wahala ina ta zirga-
zirga akan hanya ba za ki tausaya min ba, saboda wva
nake aikin nan ne? nayi maza na ce mishi idon ni ne
ka daina.
Gaba daya ban karbi rarrashin da Ado yayi min
ba, ban kuma yarda mun shirya ba, naja na tsaya kan
cewar sai lalle wannan karon nima ya bar ra'ayinshi
ya dawo nawa, tunda ni nayi mishi hakan wane dubu
wane dari bafulatani ya ce wai cabiyar din cegiya?
A haka yayi kwana biyunshi ya koma ban yarda
ya taba ni ba.

120
Ranar da ya tafi Litinin na zuba idon ganin
dawowarshi da yamma don in ga ya bar nashi ra'ayin
ya bi nawa, ko bai bi ba? Bai dawo ba talatan ma da
ya saba dawowa da yamman bai dawo ba, bai kuma
aiko da cefanen da ya saba kawowa a ranar ba.
Kamar yanda ya saba yi in zai yi fashin zuwa sai
ya tashi wani ya ba shi duk abinda ya saba zuwa min
dashi ya kawo mnin, ya kuma yi min bayani. To
wannan karon shiru ban ga Ado ba.
Sai ranar Alhamis da yamma, don haka ni kuma
ina zaune a dakin ina jin shigowarshi, amma ban
daga ido na. kalle shi ba, balle in yi mishi wata
magana. Tun bayan sallamarshi da na amsa wacce
itama don nasan amsatan wajibi ne yasa' nayi hakan.
Ban sake daga ido na kalle shi ba, balle in ce
mishi kaci kanka, kusan minti goma yana zaune bai
ce min ba ban ce mishi ba, sai naga ya mike ya fita
kamar zai je ya dawo ne.
Nima na mike nayi abubuwan da zan yi, ban
shirya ba shi abincina ba don haka ban ma shiga
kicin don yin girki ba.
Shiru ban sake ganin Ado ba har wajen karfe
takwas na dare, sai kawai ga Bala da manya-manyan
ledoji guda uku rike a hannayenshi, wai gashi ki duba
abinda babu ki fada aje a kar6o.
Na leka cikin ledojin, daya kayan shafe-shafena

121
ne sai su Sheltoze da Room freshner da su izal da
Detol, kayayyakin amfani dai da suka dangane
wannan, daya ledar ta kayan Tea ne madara Nido
babban gongoni da Bounvita shima babba sai kwalin-
sugar guda biyu.
Dayar kuwa nama ne da kifi, na kalle shi cikin
natsuwa na ce mishi shi fa? Wai don in san in da ya
tsaya yaje na raka shi yaje ya duba aikin lambunshi
daga can sai ya ce in raka shi tasha ya shiga mota ya
tafi Danja.
Kan uba, abin da nasan na fadi kenan, kafin nayi
maza na rufe bakina, saboda tsayuwar Bala a dakin.
Za'a karbo miki wani abu ne? na ce mishi a'a, jeka
kawai.
Yana fita na ce me zan yi in ba kuka ba? Kwana
nayi idona biyu ban runtsa ba, nayi kuka har na gaji,
nayi bakin ciki irin wanda ba zai kwatantu ba, wunin
rannan ban fita ko 'ina ba, ina kwance a dakina ko su
Goggo ban je na gaishe su ba sai da suka ga shiru ne
suka biyo suka gaishe ni a cewar bani da lafiya.
Sauran matan gidan ma suka yi ta zuwa, amma
don fitina wai sai da Ruwaila ta gane lafiyata kalau,
ina jin ta tana gayawa wata da suka zo duba ni tare
cewar, kalau dinta, bakin ciki ne kawai ya ishe ta.
To miji yayi mata shigo-shigo babu zurfi ya
dodana mata romo a baki ta dauka a haka za su

122
dauwama yanzu kuma bata yi aune ba sai taga ba shi
da lokacinta.
Jiya fa yana shigowa ko gaida su Baba bai tsaya
yayi ba ya juya ya tafi abinshi, yana Can wurin
wancan din, ni naji kamar ana cewa ma wai ciki ne
da ita sai ta haife za'a daura auren.
Ni kam a wannan lokacin na sakankance na
yarda na kuma mika wuya cewar bakin cikin Ado ne
zai kashe ni.
A wannan lokacin Goggo Ayalle da Babba
Tanimu sun yi matukar kula da ni, don su a nasu
ganin rashin lafiya nake yi, don ita na baiwa ma
cefanen da Adon ya aiko dashi.
Hajiya kuma tazo tayi min shara da duk wani
abinda ya kama na tsabtace min wurina, bana cin
komai sai in Goggo ta matsa min ne nake yarda in
sha ruwan tea ko farau-farau din da kullum Baba
Tanimu yake aiko min dashi.
Na rarne nayi matukar fita hayyacina, in ban da
kukan bakin ciki babu abin da nake yi, kewar iyayena
da 'yan uwana da dangina, musamman Babana tayi
matukar mamayar zuciyata.
Babu abin da nake nadamar shi irin sanya
Babana bacin ran da nayi akan Ado, gashi tun abin
bai je ko'ina ba ko shekara cif ba a cika ba har
alhakin shi ya kama ni, na soma ganin sakamalkon

123

abin da nayi 'kwai da dutse.
Kullum bayanin da mai babban allo yake yi min
kenan ya ce min basa karo, ya kan yi min irin wannan
bayanin ne kuwa a duk lokacin da na soma gaya
mishi abinda Baban nawa yake yi mana mu da
Innarmu.
Ashe ma Baban nawa mutumin kirki ne mai
kuma adalci ban taba sanin hakan ba kuma sąi a
yanzu, a wannan lokacin da nake dandanar bakin
cikin Ado.
Ran Litinin da sassafe ya zo gida babu wanda
yayi zaton ganinshi a lokacin tunda ranar nema ranar
da ya kamata ace ya tafi. Ni kadai ce a dakin ssai ko
Hasiyan da ke kai-kawon gyara min wuri.
Ina kwance a kan katifar ya wurgar da abin da ke
hannunshi yazo ya daga ni ya zaunar da ni na ki
zaman na koma na kwanta, kina hauka ne
Humairah? Kina hauka ne da ki ka maida kanki
haka?
Yanzu in ban da nayi wa Bala waya ya ce min
ba ki da lafiya sai kiyi ta zama a haka? Za ki kashe
kanki ne? ban tanka mishi ba, tun zuwanshi da safe
har Azahar ban bude baki nayi mishi magana ba.
Na riga na kudurawa zuciyata in dai zuwan da
ya yi ban yi mishi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login