Showing 27001 words to 30000 words out of 30903 words

Chapter 10 - MIJIN TA CE BOOK 3

20 Aug 2024

4871

ba zan sake hawanshi kayi
ta tsalle da ni a kan kunya ba."
Cikin natsuwa da nuna kulawa ya ce "Ba kunyaa
ba ce Humairah, hanyar ce babu kyan, na ce eh to
jeka. Ya sauka daga kan mashin din ya shiga tura
shi, ni kuma ina takawa da kafa muna tafiyar mnu
muna hirarmu mai dadi.
Mafi yawancin hirar kuma kan abin da ya shafe
mu ne, haihuwata da ta matso, gonarshi da kuma
aikinshi, kullum hirarmu bata wuce wadaunan
abubuwan guda uku.
Ranar Juma'a sha tara ga watan tara cikin
damuna sosai a lokacin da manoma suke matukar

140
taka tsan-tsan da dan abinda yai saura a hannunsu
saboda tuni karfinsu ya koma gona.
Ita kuma gcnar bata fara bayar da komai ba, na
haifi diyata ta mace lafiyayya, kana ganinta kasan
ubanta manomi ne, taci ta koshi.
Ado ya shigo gida cikin sauri a dalilin ya
kwana a dakin zauren gidanne saboda zuwan da
Sa'adatu tayi. Ina jin shi yana dariya yana tambayar
Goggo Ayalle.
Goggo wai yau ma an yi haihuwa a gidan nan
ko? Tana taya shi dariyar tana fadin "An kara
wata haihuwar. In ce ko dukansu ne suke shirin
haihuwar ne Goggo."
Goggo tayi dariya ta ce, to wa yasan musu ne?
wacece kuma ta haihu yau? Goggo ta ce a'a ashe
baka ji mnai baihuwar ba, ai Aisha ce."
Dib naji Ado yayi, yayi shiru na lokaci mai
tsawo yana sauraron bayanin da take yi, jarumar
yarinya ita kadai ta haihu sai zuwa Kanwarta tayi ta
tashe ni, hatta tsofaffin matannan da suka haihu
basu haihu su kadai ba, sai da suka taso mu muka
zo muka kwana muna zaune da su amma ita..
Ado ya katse ta ya ce to tsofaffin mata Goggo
ba sun san zafi da mutuncin kansu ba, amma ita fa
tana da hankali ne? Goggo ta rufe Ado da fada.

141

Wanne irin magania ne wannan? Yarinya tayi
kokari ba za ka yaba mata ba, bata hutar da kai
biyan kudin asibitin nan na zamani mai tsada ba?
To ni dai ban gode mata ba Goggo in tayi ne
don in yaba mata to ban yaba ba, ya juya ya bar ta
tana tayi mishi fada ina jin shi yana kwalawa
Sa'adatu kira, tayi maza ta fita ta tafi wurinshi.
Aka gama min komai aka dawo dani dakin
Goggo Ayalle wai a nan zan yi jegon, ina zama
Sa'adatu ta sake shigowa rike da kwano, ga
dabonon da Inna ta ce kar ki manta dashi.
Na kalle ta nayi murmushi na ce ai kuwa in ban
da kin tuna da na manta na karba ina ci ita kuma sai
kallon yarinya take yi tana murmushin jin dadi.
Ran Yaya ya 6aci, wai kin zauna kin haihu a
gida baki ga nima fadan da yayi min ba akan wai
ban je na gaya mishi ba. Na ce ai nima kukan
yarinyar kawai naji, in kai mishi ita ya ganta?
Na ce ke Sa'a, kin san nan gidan komai muka
yi za a iya cewa ba muyi daidai ba, ta ce haka ne.
naci dabinon sosai nasha ruwa kamar yanda Innan
ta ce a gaya min, na gyara nayi kwanciyata.
Kan ka ce meye wannan? Sai na ji ni garau
kamar ba ni ce nayi wannan uban wahalar ba.
Jimawa can Ado ya shigo dakin wurin ya nema

142
ya zauna suna gaisawa da Goggo cikin girmamawa
irin wannan alheri ya same muka tashi kana fada?
Ado ya ce kiyi hakuri Goggo raina ne ya baci ana
jaruntaka da wahala ne Goggo?
Ba za ta fada a san bata da lafiya ba? Ta ce to
tunda Ubangiji ya raba su lafiya ai sai muyi mishi
godiya, yayi murmushi ya ce haka ne.
Goggo taci gaba da yi mishi bayani ita haihuwa
ai duk ta wuce yanda ake maganarta, gida da
asibitin duk daya ne. Ubangiji ke yin ikonsa ayi ta
lafiya.
Yayi maza ya sake cewa haka ne Gogg0, mun
gode mishi. Ta tashi ta dauko yarinyar nan wai zata
ba shi ita kamar yanda ta saba kawo mishi sauran
yaran da aka haifa kafin ita a gidan.
Ya ce "A'a Goggo, ai zan ganta a hankali." Ta
ce ai haba? Ai na dauka ba za ka yi kunya ba, ta
maida ita ta ajiye ta fita saboda kiran da Baba ya yi
mata.
Yayi maza ya dawo bakin gadon yasa hannu ya
dauko ta ya kare mata kallo ya tofe ta da addu'o'i
ya maida ita yana kallona cikin murmushi.
Wannan yarinyar ta fito a jikinki Humairah ba
ki samu matsala ba ko? Ban kula shi ba, ya dan yi
waiwaye don kar yayi maganar da wani zai ji shi

143
ganin ba kowa yasa shi matso da bakinshi kunnena
ya fadi abinda yake nufin fadin.
Kallonshi kawai nayi ba tare da na ce mishi
komai ba, hidima sosai Ado yayi sai dai yaja ya
tsaya kan bai yarda ayi taron suna ba, tunda sauran
haihuwar ma duka ragunan suna kawai ya bayar
aka yi ysnka sai sunan da babu taro mai yawa.
Don haka nima ba zai yarda da gayya daga
wani wuri ba, Sa'adatun da tazo ita kadai ta isa.
Ni kam kuka nayi tayi, Goggo ma ta ce akan
me kuwa zaka yi haka? Wadannan yan uwa nata
ka ce ba za su sUnan 'yarsu ba?
Ya ce to 'yarsu tazo cikin tsululun damina
Goggo ba sai suyi hakuri ba, manomi yana hidima
mai tsanani ne da damuna? Goggo tayi dariya ta ce,
wannan shi ne iya shege.
Ni kamn da hankalina ya tashi da hana yan
uwana ziwa suna da Ado yayi sai da naji yana yi
wa Innata bayanin cewar shi din ya riga ya shirya
zuwana gida da zarar mun yada wanka, don haka
kar ayi wahalar zuwan.
Yanda Ado ya bada ragon suna guda daya a
duk haihuwar gidan da aka yi haka nan a wannan
sunan ma rago guda daya ya bayar da safe ranar
suna Baba Tanimu ya fadi sunan da ya sanyawa

144

yarinyar Umahmah.
Gaba daya kowa a gidan mamakin sunan yake
yi, wasu ma tambaya suke yi ina Baba ya samo
wannan sunan kuma? Sai da Baban ya shigo Goggo
tayi mishi tambayar naji yana yi mata bayani.
Sunan jikar Manzon Rahama ne, Goggo tayi
maza ta ce, (S.A.W), rannan da naje wajen wa'azi
naji ana tarihinta na ce to in aka yi wa Adamu
haihuwar ya mace sunan da zan sanya kenan.
Goggo tana dariyar farin ciki ta ce ai kuwa dai
Mallam tunda suna ne mai daraja, ya ce haba don
ma ba ki ji tarihin nata ba."
Duk da nanata haihuwar tsululun damuna da
Ado yayi tayi, hidima sosai yayi min. Mutane da
yawa kuma sun zo, mafi yawanci matan abokanshi
ne da kuma yan uwanshi, nawa yan uwanne
kawai ba su zo ba, shi ne abin da ya dan rage min
jin dadi.
Amma duk da haka na yi wa sunan kwalliya ta
burgewa da ban sha'awa. Lesuna masu tsada guda
biyu da atamfofi super suma guda biyu gami da
shaddojin gezna na asali suma guda biyu, dukkansu
a dinke.
Dinki kuma mai ban sha'awa ya kawo min
gami da takalma da jakakkunansu designers, ki

145
zabi wadanda za ki yi amfani da su.
Na daga ido na kalle shi cikin natsuwa na ce
mishi ya ya zaka kwashi kudi masu yawa haka ka.
saya min irin wadannan kayan? Bai kula ni ba sai
kawai yasa hannu a aljihunshi ya ciro wata sarka da
yan kunne mai kyau English Gold.
Ya miko min ki shirya in ga kwalliyar taki
kafin in fita don Kaduna nake son atfiya, kan
maganar nan da nayi miki. Kar dai ki fasa yin
addu'a ko kina zaune na gayawa Inna ma ta kara yi
min addu'a na ce mishi to.
Sa'adatu ta shigo itama tayi kwalliya mai kyau
atamfar super ce a jikinta itama Adon ne ya bata
don tayi fitar suna.
Nayi kwalliya sosai na kuma yi matukar yin
kyau, shaddar na fara sakawa saboda dinkinta yayi
matukar daukan hankalina.
Nayi dauri mai kyau na sanya sarka da
yankunne, ga agogo da zobe tunda nazo Dabai ban
taba kwalliya irin na ranar ba, mutanen da ban basu
taba sanina cikin kwalliyar da ta dace da ni, tunda
shima Ado kananan zannuwa yake saya min sai ko
yau dinnan.
Ina cikin gyaran daurina Goggo Ayalle sai
kallona take yi tana fadin iko sai Ubangiji sai ga

146

Sa' adatu ta shigo Anti wai kizo ki nuna mishi in da
linka din shi suke na kwatanta mata ta tafi ta dawo.
To kije mana kawai ki bashi tunda ya ce sauri
yake yi zai tafi, nabi maganar ta Goggo na nufi
dakin nawa da na kwana bakwai ban shige shi ba,
komai a kammale sai kanshi yake yi a tsakar dakin.
Na samu Ado a tsaye shima yayi kwalliya rigar
da ke jikin nashi sabuwa ce sai kamshi take yi.
Yana ganina ya rage fara' arshi kai ke kam ko
wayo baki dashi can zan biyo ki dakin Goggo in ga
kwalliyar sunan naki?
Ya sake kallona cikin wani yanayi na sakin
fuska da murmushi alamar ya gamsu da abin da ya
gani, ya ce wannan ita ce asalin Humairar da Inna
ta bani ba wacce na kawo na ajiye a wannan dan
tsukakken dakin ba.
Nayi murmushi don in rama mishi wayan nashi
ya ji dadi, sai na ce mishi ba fa Inna ce ta baka
Humaira ba, Baba da Mama ne suka baka ita.
Ya sake fadada murmushin shi tare da jawo ni
jikinshi har dankwalin nawa ya fadi a kasa,
kankame ni sosai yayi a jikinshi kafin ya ce minni
Inna ce ta bani ke Aisha, ita ce tayi dalilin da ki ka
sallama min kanki.
Ita ce ta biyo mu Dabai da umarnin da take

147
bayarwa ne na samu nayi sa'ar samun zaman lafiya
a gidana don haka ni a wurina ita ce ta ba ni ke.
Muka yi sallama ya kama hanya ya tafi nima na
dawo dakin Goggon in da ake sha'anin suna,
Goggo sai bina da kallo take yi tana kokarin ganin
idona, ko me take son gani oho?
Suna da kwana biyu Ado ya dawo yana
dawowan yaje ya sayo wani katon rago ya kawo
gida aka yanka yasa aka soya ya zuba shi a cikin
kwalla wacce itama sayota yayi ya hada da katon
din minti na malta sweet.
Da katon din cingam Bazooka 200 da goro dan
takarda biyu da dabino mudu biyar da shadda yadi
goma-goma, guda hudu da atamfofin super guda
uku ya tashi Bala ya ce mishi yayi wa Sa'adatu
rakiya zuwa gida gaba daya kayan ya ce a kaiwa
Baba a gaya mishi shaddojin guda hudu.
Shi daya Baba Yahya daya, Mallam Liman
daya, Mallam Harisu ma daya, atamfofi kuwa
Mama daya Innata daya, Zubaida ma daya, sauran
kuwa akai mishi a gaya mishi na haifi Umahmah ga
kayan suna nan a rabawa Jama'a.
Sannan itama Sa'adatu yayi mata tata tsarabar.
Kwanan Bala uku a can maimakon daya ko
biyun da Adon ya ce mishi ya yi ya kuma dawo da

148
shatara ta arziki.
Jego mai kyan nayi mai kuma dadin gaske na
murje nayi gwanin sha'awa in ban da ina lissafin
kwana kin tafiya ta gida ma ina jin da nafi haka
morewa jegon nawa.
Rannan Ado ya dawo gida daga Danja a
lokacin nan kuwa kwanana arba'in ne har da uku.
Yana shigowa dakin ya nemi wuri a bakin gadon
da nake zaune ya kama kallon yarinyar da ke ta
faman bacci.
NI wannan yarinyar da wa tayi kama ne? nayi
murmushi na ce wah yasan mata, wasu suce da ni,
yayi maza ya galla min uban harara wadanda basu
san ka ma iso ba ko?
Nayi shiru naci gaba da abin da nake yi, to wai
ni ba kin yi arba' in bane me kuma kike yi a naan
dakin? Nayi murmushi na ce to ai ban gama
wankan ba Goggo ta ce sai na kara.
Wai wata biyu ba kwana daya zan yi zamu bar
wankan yau ne gobe mu tafi gida. Ya tsuke fuska
ya ce a'a ban yi miki wannan alkawarin ba, na dai
ce in kin yi wata biyu za ku tafi amma ai ba daga
nan dakin za ki tashi kiyi tafiyar ba.
Nayi maza na ce ban gane ba, ya ce to kar ki
gane, kina nufin haka zan yi ta zama? An gama

149
hakurin tsohon ciki an yi na zaman jego sai kuma
in yi ta zama ina jiranki sai kin dawo daga tafiya?
Ki gayawa Goggo za ki koma dakinki yau sai
muyi ko kwana bakwai ne tare in yaso rana itayau
ma kiyi tafiyarki, na sunkuyar da kaina kasa na ce
ba zan iya ba.
Ya ce to shi kenan ni zan koma duk ranar da ki
ka gama wanka ki ka koma dakin naki sai in zo
muyi kwana bakwai tare kafin ki tafi, in kuma naga
raina ya 6aci da yawa ma sai in fasa tafiyar taka
gaba daya.
Da sauri na kalle shi "Me nayi maka?" Hawaye
suka soma ganagarowa daga idanuna, saboda
fargaba. Na matsa na matsu in je gida in ga Innata
da Babana dama sauran dangi baki daya.
To tun yaushe muke zaune ni da ke a haka
Humaira? Sai kuma ace ba za ki tausaya min ba ai
babu son kai a tsakanina da ke.
Goggo ta shigo ta same ni ina kuka ta soma
salati ina dalilin wadannan hawaye da suke zuba,
kai Ado me kayi mata? Ban yi mata amai ba
Goggo wai babu hali ne kawai ta ce ga yanda
za' ayi in ce a'a.
Ai kuwa dai ba zai yiwu ba. Goggo ta soma yi
min fada bakin cikin Ado ya kama ni don haka ma

150
ban sake daga ido na kalle shi ba balle in san
maganar da yake yi min.
Kwana uku bayan nan ya sake baro Danja ya
dawo gida ina ganinshi na tsuke fuskata, amma bai
hana shi yin magana ba. Wurinki nazo saboda naje
nayi wani sabon tunani.
Wanda zai yi mana amfani dukanmu, ki rinka
zuwa kina samuna adalci muna hira da daddare in
su Goggo sunyi bacci.
Na girgiza kai nuna alamar rashin yarda tare da
fadin ba zan...tun kafin in karasa maganar tawa ya
katse ni da wata irin rantsuwa na kuma san ba
dabi'arshi ba ne yin hakan.
To na rantse miki babu inda za ki in dai ba ki
yarda da wannan ba gaba daya na fasa tafiyar ki
zauna kawai tunda ni dama ba don ke na shiryata
ba, don nna ce nasan yanzu haka tana son ganinki
balle taji kin haihu.
Zata zo ta gan ki taga abin da ki ka haifa amma
duk da haka nasan in nayi waya na ce mata tayi
hakuri wani uzurin ya hana ki zuwa, ai zata hakura
tunda ita ba irin ki ba ce, ace mata baka da ikon
sarrafata.
Ba ka da halin ka ce mata ga yanda za'ayi ta ce
maka to sai a'a? sannan a rinka yimaka karyar

151
ladabi da biyayya ta musu? A haka fa muke zaune
ni da ke in kin yi min alherin kwana bakwai to sai
kin yi dalilin 6acin raina na kwanakin da ban san
adadinsu ba.
Cikin zuciyata kalaman Inna suka fado min
game da muhimmancin mijinka yasan alherinkato
ni yaushe ne Ado zai san alherina da kokarina akan
shi ya rike wannan yabon guda daya a mafi
yawancin lokaci yakan yabe ni ne a daidai lokacin
da abin yabon ya faru.
Amnma 'yan mintoci kadan bayan nan da zan yi
mishi wani kuskuren musamman ace kan abin da
ya shafi kankanshi ne ba zai tuna kokarina na baya
ba don haka naji hawaye sun fara zuba a idona a
dalilin zuciyata ta kuntata na fara kukan kenan sai
ga Goggo ta shigo.
Ni fa naji abinda ya ishe ni wai ina dalilin
wannan kuka ne na iya shege? Kai Adamu yayi
maza ya ce na'am Goggo ta ce na roke ka ka yi wa
yarinyar nan abinda take so.
Ya ce mata to Goggo ya tashi ya fita ya bar mu
ni da ita a dakin tana ta mita dama kin yi a hankali
namiji ne in ki ka zauna ki ka yi jegonki na gaskiya
ma ina ruwanki da shi yaushe za ki je kina daga ido
kina kallonshi.

152
Balle ki san abinda yake ciki ranki yana baci a
banza, taja tsaki ta wuce ta fita taje sanya mana
ruwan wankan yamma.
Mun kammala komai muna shirin kwanciya
Goggo kam ma tuni take ta faman gyangyadi jira
kawai take yi in gama baiwa Umahmah nono in
mika mata ita suyi kwanciyarsu da tuni tayi
barcinta, don tare suke kwana.
Muna cikin haka sai ga Ado ya shigo, Goggo
sai da safe ta ce mishi to sai da safe, ta amsa daidai
ta karbi yarinyar sunyi kwanciyar su.
Nan da nan ta soma minshari, ya mike tsaye
yana kallona muke ko? Nayi kamar ban ji shi ba, na
ce muke ko? Ko kina son yi min wulakanci ne? na
mike tsaye na fita na nufi wurin namu gabana sai
faduwa yake yi, shi kuma ya tsaya yana jawowa
Goggo kofarta wacce dama ba sakata take sanya
mata ba.
Ina shiga dakin na shaki wani irin kamshi mai
dadi ga kayaiyakin ciye-ciye iri-iri ya ajiye ga wasu
dunkakkun zannuwan da ban san da su ba a gefe.
Yana shigowa yayi murmushi, kici wani abu
mana ga kuma dinkunanki nan ki duba, na ce uh'uh
ai ba dadewa zan yi ba.
Bai kalle ni ba ya ce min dama kin saki ranki

153
don ba zan yarda da wannan dari-darin ba kin
gane?
A kan dole na saki jikina da Ado na bar shi
yayi abin da yaga dama, kuma wai maimakon yayi
la'akari da halin da muke ciki na satan jiki muka yi
na kawo mishi kaina bai damu be, bai yarda ya
hakura dani ba sai wajen karfe biyu na dare.
Ya rako ni na dawo dakin Goggo na hau gado
na kwanta yayi min sai da safe yaja kofar ya koma
wurinshi don yin wanka tunda ni kanm na riga nayi
nawa.
Na fara bacci kenan, Goggo ta tashen a dalilin
yarinya ta tashi na karbeta na bata nono.
Washegari da safe Ado ya shigo bayam munyi
wanka daga ni har yarinyar Goggo tana wurin
kosanta, zama yayi a bakin gadon yana wasa da
kafar yarinyar dake faman shan nono.
Zan fita amma ba zan dawo da wuri ba in na
dawo zan zo in sanar da ke don ki zo ki same ni, na
ce mishi kai...yayi maza ya katse ni da kin koyi ce
min to don ki rinka sarun cikakken lada.
Da daddaren kuwa sai da ya dawo ya zo yaja ni
muke je. Washegari ma haka tun ina tsoro sai kuma
na saki raina, rannan ina tare da shi mun yi matkar
sakin jiki mun shagala cikin al'amuranmu.

154
Gaskiyar magana ita ce daga ni har shi muna
Son juna, muna son kasancewa tare da juna, nakan
dai jawa Ado raine kawai in yi mishi yanga saboda
kawaici da kuma jan aji irin namu na mata.
Amma in ba haka ba kasancewa tare da shi
yana sanya ni jin dadi, ya sanya ni farin ciki da
nishadi, ya sanya ni in rinka ji da ganin tanfar
bayan ni din to babu wata. Barin komai yake yi ya
tarairaye ni ya gaya min kalmomi mnasu sanyaya rai
da tofar da zuciya.
Ya maida kanshi zama tanfar wani dan yaro ko
wani mara yawo a gabana, bai kuma gajiya kullum
muka shiga cikin irin wannan halin zai nanata
kalmarshi guda daya da ya saba gaya min ita ce ke
din matata ce Humnairah.
Ke ce matata kar ki taba ganin nayi aure a wani
lokaci kiyi tunanin zan mallaka mata kaina kamar
yanda nake mallaka miki ko zan zauna in yi mata
shagwaba da sakarci irin wanda nake yi miki.
Muna cikin wannan halin ne kawai naji Goggo
Ayalle tana kwala min kira a tsakar gida da
iyakacin karfinta, a cikin kua wannan tsohon daren.
A kidime fwarai nayi maza na bude baki da
nufin amsawa don in hutar da ita wage bakin da
take yi tuna yi min irin wannan kiran a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login