Showing 174001 words to 177000 words out of 209775 words
T A_*
Page 89
________________________
https://chat.whatsapp.com/DT97XBDyEfyEwniN0a09Cz
*_assalamu alaikum warahmatullah_*
*_kina ta ganin kaya kala kala online?,kinason siya amma kina tsoron damfara?,tsada ko rashin ingancin kaya?_*
*_wannan tsoro da taraddadi ya yanke miki indai da HUGUMA CLOSET_*
*_muna da nau'ikan kaya kala daban daban bisa farashin da ba kowanne dan kasuwa ke iya bada kayansa akan hakan ba_*
Shadda
Laces
Atamfa
Kayan yara English wears dana jarirai
Qawatattun handbags
Mayafai
Abayas da jallabiyas
Inner wears
Huluna na maza da mata yara da manya socks
Takalma na maza da mata yara da manya
Lafayas
Sarqoqi agoguna banguls da rings
_kai komai daya danganci kayan ado na fita kunya wa dan adam_
_bisa farashin da zaiyi daidai da buqatarka_
*_Me kike jira sallah na gabatowa?,ana can ana ruwan suturu daidai da qarfin kowa?_*
*_masu manyan qarfi da matsakaita?_*
*_ki dinga siya da kadan kadan kina saka kudin kina tara abinki har sukai sanda zaki karba?,ko ki siya lokaci daya a kai miki_*
*_muna aika kaya ko ina a duniya in sha Allah_*
*MUNA BONONZA LOKACI LOKACI NA DUKA ABINDA RABO YA TSAGA*
*_MASU REPOSTING DA MASU SARI DUKA BA'A BARSU A BAYA BA,KI SIYA KI SAIDA KI SAMU RIBARKI HANKALI KWANCE,BA TARADDADIN INGANCIN KAYA KO WANDA KIKA BAIWA KUDINKI_*
*_KIYI JOINING KI TURAWA 'YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI_*
*_INGANCI RAHUSA GASKIYA DA AMANA SHINE TAKENMU_*π«Άπ½π«Άπ½βπ½βπ½βπ½βπ½
https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr
_________________________
PAGE 89
"Enter" Jordan yace dashi yana jiyowa sosai gareshi gami da nuna masa cikin motar. Bashi da abunda zai ce don shi kansa yasan nan din ba wajen wasa bane,ya daga qafafunsa da yaji sun fara masa nauyi yana sanya jikinsa cikin motar,yana kuma jin yadda gumi yake tsargo masa daga kowacce kafa ta jikinsa.
Set din dake opposite nasa ya masa nuni,hakanan ya zauna yana qoqarin gyara lab coat dinsa yana hadiye wani miyau me kauri. Idanu kawai fu'ad din ya sake zuba masa duban daya sanyashi kasa nutsuwa ya dinga gyare gyare,daga gyara agogo zuwa gyara rigar jikinsa da kuma hannun rigar.
A nutse ya janye masa idanun,sannan ya motsa bakinsa
"Ya sunan doctor din?"
"Ni....Dr kamal......sunana Dr kamal". Kai fu'ad ya jinjina yana lumshe ido gami da budesa sanan ya maimaita sunan a hankali
"Good Dr kamal,ina maka murnar samun damar zama likita ga mahaifiyata......am.....inaso nasan da meye da meye suka ce ka gaya mana a matsayin cutar dake damunta?". Sosai maganar ta rudashi saboda tazo masa a bazata,ya dubi fu'ad yana qoqarin nuna masa gaskiyarsa
"Su waye?.....Ni ba wanda yacemin ga abinda zan fada sai abinda bincikena ya gano".
"Kamal!" Fu'ad ya kira sunansa da wata irin deep voice dake dauke da amo me tsoratar da wanda ake magana dashi.
"N...na'am"
"Lookat me......" Ya sake fadi masa yana tsareshi da idanunsan nan da suke sanya Dr kamal jin kamar zaya narke.
"Kayi haquri yallabai" Dr din ya sake fada kansa tsaye ba tare da fu'ad din ya sake cewa komai dashi ba. Wani irin rudani da firgici suna ratsashi.....gaba kura baya sayaki,yasan hajja harira ba sanin shanu ba,amma ta yaya zai yadda yayi jayayya da mutum irin muhammad jadda din?,wanda yayi imanin ita kanta inda hajja harira ta gama sanin wayeshi da kyau ba zata saka kanta cikin wannan wasan ba.
"Yallabai......sunce zasu biyani bayan barazana da hajja harira tayimin......sunce na kwantar da ita kawai na saka mata ruwa wanda zai qara mata kuzari ne kawai...........sunce tabbas zakazo...idan kuma kazo din na kambama ciwo da kyau,na nuna muku zaman kadaici da kewa ce take damunta,wanda muddin ba'a kula da ita da kyau ba.....an samu wani cikin wadanda sukafi kusa da ita take kuma yawan ambatarsu su zauna tare da ita ba to tabbas zuciyarta zata iya bugawa ayi hasararta......sunce idan.....". Dakatawa yayi ba tare daya qarasa fadin abinda zai fada din ba saboda daga masa hannu da fu'ad yayi. Shuru ya ratsa motar,abinda ya sake ruda Dr kamal,ya sanya hannun rigarsa yana goge gumin fuskarsa bayan ya cire gilashin idanun nasa.
"Sauka kaje....kaci gaba da riqeta.....zaka sallameta,but sai daidai lokacin da na baka umarnin yin hakan"
"Okay sir" Ya fada da gaggawa yana juyawa gami da laluben hanyar fita daga motar,don zaman motar duk da laushin kujerunta da sanyin Ac da wani ni'imtaccen qamshi da yake fita......amma ji yakeyi kaman yana zaune ne cikin qabarinsa.
"Dr" Ya sake kiran sunansa dab da zai sanya qafafunsa a qasa. Adan zabure ya waiwayo yana qoqarin saita kansa.
"Banda wannan harqallar.....ka tabbatar babu wata sauran haramtacciya ko miyagun harqalloli da kakeyi a boye......don idan hakan ta kasance ka tabbata ba zaka tsira a hannuna ba"
"Wallahi ranka ya dade ba ruwana......ni din mutumin kirki ne ka tambayi kowa ma"
"In kuwa hakane ka kyautawa kanka".
"Sauko malam" Jordan yace da Dr kamal din a dake cikin rashin son wasa.
Jinsa ya dinga yi kaman zai kifa sanda yake komawa cikin asibitin. Inda ace yasan da gaske take ita din mahaifiyarsa ce ta yaya zaiyi wannan kasadar?. Fadan giwa da damusa waye yake shiga?,sai wawa sai mahaukaci,shi kam qaura zaiwa asibitin bazai sake shigowa ba sai gobe,duk da yasan bashi da inda zaije yace ya guje masa.
Duk wani mamaki da maamah zata bashi a yanzu ya biyo bayan wanda ya gani a yanzu da shekarun rayuwarsa ta baya. Ko daya bai sake komawa asibitin ba,saidai kuma bai hana kowa zuwa ba. A kwanakin ma gaba daya yana qoqarin ganin ya gyara wasu abubuwa da yake ganin suna qoqarin tasowa can qasan kamfanin,wanda idan har ya bari matsalar tayi girma zata iya jawo asara mafi muni fiye data kudadensu da suka zirare.
A cikar ranar lahadi kusan kowanne bayani ya kammala samunsa,ya shigar da komai cikin documents,sai la'asar ya kammala,don haka daga nan alwala yayi ya wuce masallaci. Daga masallacin ya sake dawowa gida,ya leqa anni da bata jima da dawowa duba maamah ba,sai ya zauna falon bayan ta sanya amna ta dama masa yoghurt da fura.
"Muhammadu" Anni ta kirasa,sai ya dauke idanunsa daga tasha alhadath dake nuna yadda bani Israel ke dake ragargazar Palestinian,hankalinsa ya fara nisa kan hanyar da zai aika musu tallafi ya kuma isa garesu kai tsaye
"Na'am" Ya amsawa annin yana dubanta
"Jiya abbanku ke complain....ko sau daya ance ba'a ganka a asibiti ba......ni kaina ko sau dayan banji kace zaka je ba,sai zama da kaketa yi a sassanka?".
Hannu ya sanya ya karbi kyakkyawan tray din da amna ta jero cups da bowl me kyau dake dauke da dammen yogurt din,ya aje gabansa yana cewa
"Thanks lovy dovy". Qaramin murmushi ta saki,ta juya tana komawa kusa da anni ta zauna.
"Jikin nata da sauqi ai anni......infact ma tun ranar ta samu lafiya.....yau ma zasu sallameta". Ya amsa ba tare daya kalli annin ba,don yasan yana yin hakan zata dago wani abu
"Duk da haka muhammad wannan din baiyi kyau da tsari ba....."
"Yanzu daga nan can zanyi anni kiyi haquri". Kalmar haquri idan ya fadeta da gaggawa haka to tabbas baison bacin ran annin ne,ta gama karantar hakan.
Jujjuya furar yayi sannan yayi bismillah yakai bakinsa. Fuska yadan bata ya daga kai yana duban amna
"Yaushe kika koma sakamin sugar a abin sha?". Kai tadan langabe
"Hamma.....kadan fa na saka maka wai don bakinka yayi taste"
"Zoki dauke abarki" Ya fada yana dan ture bowl din. Da sauri ta miqe tana fadin
"Ayyah hamma.....kayi haquri kada magauta suji kanmu....bari na hada maka wani wannan sai BB farouq yasha"
"Kayi zaton amnan taka tayi hankali ne?,kaima kai ka sowa kanka wannan gallafirin......wai sai yaushe zaka fidda mace ne Muhammadu?,bakasan duk girman namiji aure shike cikashe wani gibi ba?,gibin da babu abinda zai cikeshi face auren?......ita kanta amna yaushe ta fara iya riqe abinda ya dace da itama ballantana ta riqe abinda ya dace da waninta?". Waiwayowa tayi tana duban annin kamar zata saki kuka
"Wayyo anni.....yanzu duk qoqarin da nayi baiyi ba?,hamma don Allah ban canza ba?" Wani sassanyan murmushi ya kubce masa,ya maida kallonsa ga anni
"Tsokanarki fa anni takeyi.....kin canza sosai amna ta,kinyi kuma hankali,yauma nasan akasi aka samu,ki dama min wata ki sakamin apple a ciki da grapes ki ajiyemin,idan na dawo zan sha".
Tabe baki anni tayi tana kauda kanta
" Ai daman.....indai abu da laifin amna duk girmansa saika maidashi qarami......da tashi kayi kaje ka shiryadinma da zaifi maka". Murmushi ya saki ya miqe a nutse. Duk wani jini na anni girmansa yake gani martabarsa yake gani hakanan qaunarsa yakeyi.
"Hamma na shirya na rakaka?" Ta fada tana tallafe da tray din.
Bayason zuwa da ita,saboda ya tabbatar ba zata samu marabtar data dace da ita ba,amma bazai iya cewa bazaije da ita ba,don haka yace
"Ki shirya.....but be fast....banson jira"
"Yanzun nan hamma" Ta fadi tana qara hanzarin barin wajen.
Suna hanya tana cikashi da labarai kala kala wanda hakan yake masa dadi da debe masa kewa. Don amna din wajen quruciya da sakalci irin na autanni ba daga baya take ba.
Koda suka isa cikin asibitin sai ya kalleta
"Ko ki zauna a nan,ko na yiwa Jordan magana ya kaiki ki zabi duk abinda kikeso.....kina da 30 to 40minutes"
"Yay!.....thank you hamma na" Ta fada da tsananin murna.
Zaune take daga bakin gadon da kwata kwata cikin kwanaki ukun a duniya taji ba abinda ta tsana sama da kwanciya a kansa. Kwanciyar da babu alamun nasara a tattare da ita,kwanciyar da bata amfaneta da komai ba saima sake haska mata rashin nasararta muraran da ake sakeyi.
"Ba alamun nasara hajja......zuciyata tafi karkata akan na tafi plan C.....a plan C ne kuma nakejin cewa koda sharadina zai zama silar rugujewar fu'ad wannan karon basan sassauta masa ba......a wannan karon a shirye bake na gindaya masa sharadin da nayi imanin bazai iya tsallakeshi ba.....a wannan karon hajja......ban yarda koda da darsawa a rai ba zuciyata ta darsamin wai bazanyi nasara ba.....dole dole dole nasara ta kasance a tsagina.....hajja a yau zan bar asibitin nan,ina da buqatar na huta saman gadona nayi bacci me lafiyar da zai bani damar tsara komai da kyau cikin kwanyata.....na kuma wayi garin litinin da wannan shirin".
Kai hajja ke gyadawa tana kuma sake juys Plan C din maamah data tabbatar zaiyi wahala idan ba abinda take hasashe bane ba.
"Hakan ma yayi,abun ni kaina ya soma shallake tunani na.....amma mariya anya shima baida hatsabiban da suke masa aiki?" Shuru maamah tayi,ko qwalqwalwarta bata kama muhammad yana biye biyen nan ballantana hankalinta. Tun daga haihuwarsa zuwa tasowarsa kawai tasan ya banbanta da sauran yara,quruciyarsa ma ta daban ce a cikin yara,zuwa sanda ya cika shekara goma cas a sannan ta sake ganin banbanci mabayyani a kanshi.
Shigowarsa dauke da cikakkiyar sallama sai ta zama tamkar amsa ga tambayoyin hajja harira. Bakinta yana dan rawa tana kamo amsar sallamar da qyar ta hada kalaman tana amsa masa.
A nutse ya tako ciki idanunsa akan maamah din data dauke kanta daga gareshi gabanta tana ji yana faduwa. Haka kawai ita kanta sau tari sai taji ya mata kwarjini,fargabar kada dai ace yaji wani sashe na tattaunawarsu yana cikata.
Duk yadda hajja ke qoqarin ankarar dashi tana wanze a dakin ta hanyar jera masa sannu da zuwa amma ta gaza samun hankalinsa. Bawai kuma don baijita ba,aah haka kawai yakejin wani abu na daban game da matar,sannan kuma kwanyarsa a kullum idan ya ganta takan yawaita qoqarin tunata cikin jerin sahun mutanen da yaga gilmawarsu a shekarun da abbansu yake raye.
Kaman bai lura da sauyawarta ba,yaja kujera gaban gadon ya zauna yana gaidata. Ta amsa masa tana hadiye bacin ranta. Fada takeson masa sosai ko zata samu sassauci amma kuma idan ta tuna a gobe akwai nata plan din dai ta danni zuciyarta,saidai duk da hakan sai data b'ara
"Kasan ina nan amma fu'ad ka banzatar dani?,ko ka manta ba'a canzawa tuwo suna?"
"Kiyi haquri" Ya jefeta da kalmar nan da har ta fara tsanarta saboda yawan fitarta daga bakinsa.
Shuru yaci gaba da ratsa dakin ba tare da kowa yace da dan uwansa komai ba,kafin daga bisani aka turo qofar.
Dr kamal ne,ya qarasa shigowa cikin takatsantsan da tsantseni,wanda dukkan me hankali yana kallonsa zai fahimci hakan.
"Kwanciyar haka ta isa?,xaki iya komawa gida?" Ya tambayeta a tausashe saidai kuma kalamai ne masu harshen damo da yawa a ciki.
Juyowa tayi tana dubansa maganar tana qoqarin fassara kanta da kanta cikin qwalqwalwarta. Ta zargi wani abu,amma kuma yanzun ba muhallin wannan bane,don haka ta dauke dubanta ta maida kan Dr kamal
"Ina buqatar sallama Dr,naji qwarin jikina".
" Yanzu in sha Allah" Ya fadi yana bude file dinta. Hannunsa yana dan rawa yayi rubuce rubuce ya maida ya rufe,sai fu'ad ya miqa masa hannu Kai tsaye,yadan kalleshi sannan ya miqa masa file din salin alin.
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 90
*_MONDAY_*
*_Tushen aiki,ko nasara na tsoronki_*
Cike da confidence take shiryawa cikin tsadaddiyar dubai abaya budaddiya data lullube jikinta ainun.
Wine color wadda aka qawata qasanta da kuma qasan wandon abayar da wasu irin stones da zare ruwan gold masu daukan hankali.
Gaban madubi ta matsa tana saka brush tana sake kwantar da doguwar sumarta me yauqi da rashin cika sannan ta ware madaidaicin mayafin abayar tayi rolling dinsa saman kanta,abinda ya bawa kyakkyawan fuskarta daman fita tarwai ta kuma haska da wine color din abayar jikinta.
Siririn agogo ta sanya gold me dan adon wine,wanda yake suwa set da komai nasa,ta taka a hankali ta matsa ta dauki purse dinta da wayarta ke ciki tanata haske.
Kiran ta daga ta sanya a kunnenta tana aza idanunta kan huda dake zaune gefan gadon,kai kace mata ket ta zura da gudu
"Okay.....gani nan fitowa" Ta furta tana maida wayar jaka sannan ta maida kallonta kan huda. Suna hada idanu boyayyun hawayen dake qasan idanun hudan suka yiwa kansu hanya.
"Adda.....ina tsoro" Ta fada tana jin zuciyarta tana nauyi. Taku biyu Sabrina ta isa gabanta,ta kuma kamo hannunta
"Duk duniya.....duk wanda yace zai tabaku bazan qyaleshi ba muddin ina da iko da qarfin hakan......ba yau ba,ba kuma sau daya ba ina jan kunnen Naseer yayi qoqarin fidda rayuwarsa daga kaina......ya sanyawa ranshi bai taba haduwa da wata basma ma ba amma baiji ba........a wannan karon ya kamata nayi masa general hukuncin da zai sanya a rage ire irensa baragurbi cikin mutane......kada kiji tsoro,babu abinda zai faru" Ta bata tabbaci tana matsa hannayenta.
Iska me zafi maamah ta furzar daga bakinta sanda suka kammala zama saman qawatattun kujerun da aka zuba saboda zaman cin abinci ko shan wani abu ga baqi maziyarta wajen.
"Wai nikam mariya.... Meye hikimar tattaunawarmu a nan?" Hajja harira ta tambayi maamah tana kallonta.
"Harira.....gani nakeyi kaman akwai wani information nawa da yakeyin leaking.......yadda fu'ad yake samun damar kaucewa kowanne tarko nawa abun yana da matuqar daure kai......inaso mu koma gida da wuri don a yau nakeso A YITA TA QARE!"
"Ina saurarenki" Hajja ta furta tana hade yatsunta guri daya tare da bawa maamah hankalinta.
"Hajja......aure zanwa fu'ad!" Sosai maganae ta zowa hajjan a bazata,wanda hakan yaso hautsinata tare da haifar mata da fargaba......fargabar yiwuwar rushewar plan nata da rashin cimma interest dinta tsakanin wasan da ake murzawa yanzun.
"Aure kaman yaya mariya?,ya samo matar auren kenan?" Kai ta girgiza tana sake matsowa kaman hajja din bata jinta sosai
"Ya akayi kanki ya kulle hajja?,zanwa fu'ad aure da yarinyar da duk na zaba masa don ta zamemin tsanin MALLAKARSA".
Shuru hajjan tayi wuta tana neman dauke mata. Ba wai kuma mamaki ta shiga ba,aah tanason adan taqin tayi tunanin amsar da zata bawa maamah wadda zata bayu ga tafiyar lissafinta daidai. Duk yadda taso kuma ta kwalkule maganar ta fiddata a daidai ta gaza,don harbuwar maganar zuwa kwanyarta tazo mata ne da wani irin katsuwar hanzari da gajere kuma tsukakken lokaci
"Yimin bayani dalla dalla qawata".
"Yanzun nan" Cewar mamah tana komawa ta zauna sosai.
"Zan nema yarinyar da na tabbatar babu soyayya a zuciyarta sai soyayyar kudi......zan nema yarinyar da zata iya aikata komai indai akan