Showing 69001 words to 72000 words out of 76784 words

Chapter 24 - WA ZAI FURTA COMPLETE HAUSA NOVEL

28 Oct 2024

15143

akwai rigima ko?
Babba ma kuwa suka kyalkyace da dariya tare da tafawa.
Ya wurga mishi ball din suka Fara bugawa cikin nishadi.
Yanzu ya zakayi kenan?
Zan siyi gidan nan Wanda naga angama sabo na darawa ko nawane yayi Masa kudin bala'i Zan biya Mata,sai ta zauna ita da Aisha da Maryam Amma banda khausar don bana son yarinyar... Daddy zai yarda?
Dolen sa ma, Zan Sanya Mata masu gadi sosai Nima na siya Mana gida bayan gidan redio zamu bar hostel...... Sadeeq ya buga tsalle amma ka gama birgeni nawan suka tafa suna dariya...
Na Kira VC na fada mishi ayi meeting wallahi duk lecturer din da ya Kara Kira mun Mata Zan daure Shi..... Sadeeq ya zaro ido ai FUDMA sun gama shiga uku Yanzu...... Suleiman Kuma na mishi text na fada mishi na auri Bilkisu kallonta idan yayi ya gama Jin dadi har abada don zai Kare rayuwar sa a prison..... Anwar kada ka firgita makarantar can.... Yayi dariya kawai.
Da mota zamu koma yanzu?
Ya kyalkyace da dariya Kai mota ce dakuwar ka Wai?
To motoci ba mota ba, Zan fito musu a mutum sak!
Nawaoooo... Sadeeq ya fada.
Bilkisu kuwa, Miskilancin ta da zurfin ciki ya hana ta fada wa mommy abinda ya faru ba.
Haka suka taru sukayi Mata nasiha cikin hikima na duk darasin maganar bai wuce ta kiyaye tarayya da shi Kuma ta kula.


*******************
*Federal University dutsinma*

Aisha da Maryam abun ya daure musu Kai, gidan tsoro ma yake Basu, har basa son fita saboda kattin da gewaye da gidan, komai an saka gida abinda ke gida ga masu aikin abinci da gyaran gida.....
Da yake sun rigata komawa da kwana biyu shine yakai su ya masu bayanin anan zasu zauna tare da Bilkisu ranar duk da suka gayyato wata kawa ko namiji wallahi sai yayi maganin su....
Su Kam sunyi tsuru tsuru gashi har yau basuyi waya da Bilkisu ba.
Misalain karfe shidda na marece jirgin ya ajiyeta motoci hudu an musu layi Yana tsaye ya goya hannu a kirji ta Fara saukowa da zumbuleliyar hijab har kasa ya kura Mata ido tun kafin ta karaso ya bude Mata kofa....
Tana shiga ya shiga suka rufe kofa aka fizgesu sai dutsinma.....
Ya kalleta ba gaisuwa hajia?
Ta danyi murmushi,
Kin gaji ko?
Ta ce hmm kawai,
Ya makarantar?
Ta tambayeshi tana kallon fuskar Wayarta,
Lafiya Lau, Amma fa ban shiga ba har yau sai gobe nima Zan Fara zuwa lecture... Ta Dan kalleshi saboda me?
Ya Dan yamutsa fuska haka kawai.... Sai tayi dariya.
Dariyar me kikeyi?
Naga kana mun karairaya kamar mace... Ya kyalkyace da dariya Wai Ina son in birgeki.... Ta dalla mishi harara.... Ya Kara dariya.
Su Aisha sun kagara ki dawo...
Kai meye hadin ka da Aisha???.... Ya zaro ido ya watsa hannuwa ba komai fa....
Sai tayi murmushi,
Anya Bilkisu???, Ya leka fuskar ta.
Ta rufe tana Yar dariya.
Kin iya mota?
Um.
Good, to na ajiye Miki tana nan, zaku zauna keda su Maryam, nima nabar hostel muna bayan gidan redio nida sadeeq, idan daddy ya Miki magana kice ninayi Haka, akwai masu gadi da ma'aikata Amma fa ki sani idan zakiyi mun abinci kada kisa kowa naki nake so kin gane ko?
Ta mishi banza.
Ko bakiji ba?
Karatu nazo ko girki?
Komai ma kinzo yi, kin sani cewa akwai Aure na akanki ko?
Gabanta ya bada ras!
A bakin gate ya fita yabar su suka shiga gidan driver ya fito yabar Mata motar tare da Mika Mata key, ta zaro ido Wai wannan motar ce tawa?
Ya sunya eh Hajia, ta amsa kawai tayi ciki..... Su Aisha suka kwaso da gudu tana ganin su ta fasa ihu itama sukayi ciki suna Murna.........Suka tsareta da tambaya Wai ya Haka?
Ta fada masu ya tura iyayen sa neman Aure Bata sanar dasu akwai Aure akanta ba.
Mufeeda kuwa hauka kadai ke batayi ba da taji Anwar ya siya ma Bilkisu gida ba.
Zuwanta biyu Amma ko layin gidan Bata iya kaiwa saboda body guard, shima ta gano nashi gidan cikin Daren Nan ma securities ne gewaye unguwar.....

Ta dunga kunduma ashar tare da Shan alwashin gobe sai ta ji dalili.
Bakwai suke da lecture ta munafuki Richard, akayi sa'a Aisha ma nada 7am
Suka fito abin mamaki har an goge motar...
Ta kalli Aisha wallahi kunyar hawan motar Nan nakeji Aisha..... Meye na kunya?
Kuma ba ga nikaf kin saka ba?
Kai nasan yau na gama shiga uku makarantar Nan..... Ke muje ni ki ajiye ni kada na makara ta bude motar ta shiga ... Ko Zaki ja mu....??? .... Ni??? Ta daki kirji.
Anwar yau ya mayar dani kauyen mu kike so ko?
Ba yanda ta iya dole ta shiga tare da bata wuta suma suka tayar da mota suna jiran ta fita su bita ( securities biyu ),, ta fita gate din a hankali tana Hawa titi ta chilla da gudu saboda sun kusa makara. Suma suka rufa Mata baya.
Duk da safiya ce duk tsiraren mutanen da wuce sai sunbi motar da kallo.....
Kai Anwar karshe ne, shida sadeeq kasa suka tako, a bakin gate ta wuce su, ya kyalkyace da dariya Sadeeq yarinyar can gudu take da mota fa...
Dan ubanka mu ba ka hana mu dauko ba?
Ya Kara dariya suna ta sauri....
Ta tsaya Aisha ta sauka saboda ba hanyar su daya ba ita ciki zataje Aisha Kuma nan farko farko.
Tana zuwa kowa yayo ma motar chaaaaaa..... Chinayye ta gane ta da gudu ta makale tana fadin Bilkisu oyoyo.....
Ya akayi Kika ganeni?
Ta fada a hankali , haba ya bazan gane ki ba?
Wai kinyi Aure?
Inji waye?
Eh Mana ance you are married woman now....no, not yet. But am engaged... With Anwar??.... Shigowar sa yasa ta Kyaleta, ya rufe idanun sa da facing cap abin mamaki kawai ya wuce baya yaki Zama kusa da ita.
Suleiman ya shigo sai kawai ya chanza layi ya koma can baya saitin Anwar din.
Sai mazurai yakeyi cikin facing cap.
Mugun na shigowa sai cewa yayi test... Hankalin kowa ya tashi, ko ajikin Anwar,
Nan da Nan Bilkisu ta Fara kyarma.....
Question biyu ce, ba Wanda ya sani Anwar kadai ya amsa da kyar Bilkisu tayi attempting ta biyun sai kuwa su chinayye.
Yana fita ya taso da sauri... Kin amsa?
Ta zumburo Baki Ina na sani?
Bakiyi ba kenan?
To me Zan rubuta?
Ya buga tsoki this man .
Nan da nan Yan class suka Fara kallon kallo.
Shi kuwa Suleiman Richard na fita shima yabar ajin.
Ya zauna bisa table Yana kallonta, budo in Miki bayani ya saboda gaba... Ta Mika mishi book din, duk nikaf din ta ishe ta ba yarda zatayi ne.
Ya Fara Mata bayani a hankali ya lura sai mutsu mutsu takeyi yace Wai ya akayi?
Nikaf din nan ta isheni wallahi Dan Allah in cire?
Ya danyi dariya cire Mana .
Ta kalleshi da sauri da gaske ko gatse?
Sai kawai yasa hannu ya cire mata..... Dai dai shigowar mufeeda.... Ta tabbata wallahi, kutumar uba... Anwar da gaske An daura muku Aure da wannan banzar..... Ji kake tasssssssss! Fassss.....ratssssss duk illahirin hankalinta ya bace ta gigice ta kidime shima ya razana ainun ganin Bilkisu tsaye tana wanka Mata wadannan marukan.............na rantse da Allah Akan *Anwar Zan iya kisa* don Haka ki kiyaye... Body guards suka gani cirko cirko nan da nan Yan ajin suka fara direwa ta taga saboda firgici.......✍🏼 Ayi hakuri da kadan.

*maman Abdallah*πŸ’–

*uwa Mai bada mama mom ( Maryam adamu tikau maman amannas) mom you are the best I love you so much Mom*

Wadanda ke cewa ba ni ke rubutawa ba a fada wa Mai rubutawa ta ci gaba da kokari Nima Zan dage wajen sharing.....πŸ˜„βœπŸΌπŸ€ *WA ZAI FURTA?*🀐
2⃣6⃣

*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( Hajia Rabi badawi Kano maman Ibrahim ), Allah ya Kara arziki ya shirya Miki zuri'a ya Kara Miki tsawon kwana. Amin.*


*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*

*Domin ki...... beloved sister Khadija Dahiru wowo miji na gari I pray*

πŸ‘‰πŸΌπŸ’žπŸ’•πŸ’• *RUKAYYA BAKO DAN BATTA I love you so much, remember this always*πŸ₯°πŸ˜πŸ˜˜.

**************
*Federal University dutsinma*

.......Ta shako wuyanta ta buga da table, gyalen ta ya fadi hular gashin da ke kanta itama tayo kasa, wani chukuikuyon kitso ya bayyana ba 'a ko ganin tsagar ga kegen can manne a wuya.....kaiii Bilkisu kina hauka...mAnwar ya fada a firgice..... Ta nuna Shi da hannu daya korar mun wadannan kattin ta kallesu tana zare ido.... *What the hell are you doing here*?????.... Wata Kara mufeeda ta saki ta dago ta da karfi goshinta ya Kara tsawo kamar wani bread da ake Kira danbisije na funtua...
Ya yunkura zai riketa ta Kara buga kanta a table....Zan nakasa ta Anwar wallahi...... Ya daga hannuwa sama okay ..okay... Ya kallesu kuje waje... Kofar class din da bakin tagogi students ne makil ...... Idanun ta sun kada sunyi jawur tana magana tana zare mishi ido...... Kai bazaka iya maganin ta ba ko? Zan ci ubanta yau saboda duk makarantar nan yarinyar nan ta tsone man ido..... Zan yi..wallahi zanyi maganin ta please kada ki janyo mun bala'i kada kiyi kisan Kai Bilkisu.... wannan cin fuskane ki barshi ta mayar da gyalenta please....Ta ingizata da karfi tayi baya ta fada cikin sit bayanta ya daki kujera da karfi ta saki wata Kara.... Yayi wurinta da gudu a firgice...... Tayi tsalle ta dira gabansa kana tabata Ina karairayata....... Chief security suka gani da wasu securities subhanallah meke faruwa anan.... Yana ganin Anwar yace ranka ya dade da kanka???
Dan Allah ku fita da mufeeda kuje da ita.... Magana yakeyi a harmutse duk ya rikice, Bilkisu kuwa ya dake ta Sha mur Kai baka taba cewa ita ce tayi wannan tashin hankalin ba....... Ya kalli security daya je da ita clinic.... Yallabai kuyi hakuri muje office... Ita ce tayi gaba...... Zuciyar ki tayi yawa Bilkisu wannan yarinyar ta wahala me yasa Zaki.... Ta dalla mishi harara , ka Sanya a daureni na daki sahibar ka kasa a kaini prison..... Ohh my God,
Da gudu sadeeq ya dawo cikin makaranta jin wannan mummunan labari,
Abin mamaki Bilkisu ta Sami shaidar lallai mufeeda ce ta Fara tsokanar ta..... Anwar ya shiga ya fita case ya mutu. Suka fito duk ta chukuikuye fuska... Sadeeq yarinyar kaga zata yi kisan Kai ko?
Bilkisu me...... Na rantse da Allah idan ka Kara mun maganar waccen Yar iskar Zan sameta har dakinta na Mata tsinannen duka Wai Anwar kasan Hali na kuwa?
Na sani a yau, na sani wallahi Dan Allah kada ki Kara kula ta zan kawo karshen matsalar..... Kada ma ka kawo zata ci ubanta.... Ya kalli sadeeq duk sukayi murmushi.
Kawo key din na dauko Miki motar sadeeq ku jira anan..... Ya wuce da sauri, sadeeq ya danyi dariya, duk kin hargitsa mun Anwar kin San Shi baya son tashin hankali..... Tunda takai fagen mufeeda ko? Ai Dole ya hargitse, wace irin masifa ce Suleiman ke bai gani ba?
Kasan Allah ka gaya mishi idan bai nesa da mufeeda ba sai na halaka ta...... Itama daga yau Dole ta shiga taitayinta kuma Zan fada mishi.
Ya iso, ganin baida niyyar fitowa yasa ta fada baya ta zauna Dole sadeeq ya shiga gaba.... Suna fita yayi hanyar gidan sa Yana fadin Bari ki Fara ajiye mu tukun ta mishi banza kawai.
Har ciki ya shiga da motar suna tsayawa ta fito ya dan koma gefe ta shiga wani mugun ribos da tayi sai da ta birge duk Wanda ke shiyyar.... Ya bita da murmushi kaiii sadeeq yarinyar can karshe ce..... Suka kyalkyace da dariya Ina so na ce ta dafan abinci amma duk na tsorata da ita.... Sadeeq ya kwashe da dariya Bilkisun kake tsoro????
.... wallahi tsoronta nake sadeeq, ya fada Yana dariya.
Kaga tsawar da ta daka mun Wai na ce su mustapha su fita???
Duk suka Kara kyalkyace da dariya.... sadeeq ya ce ko baba da babansa.
Mufeeda kuka kawai takeyi, ba dukan ya Mata zafi ba, irin yanda ta cire Mata hular gashi ta tozarta ta gaban jama'a..... Ta kasa daina kuka, kunya ta hanata fitowa daga clinic din ta tafi daki.
Hakuri kawai kawayenta ke bata, Asma'u ta ce Ina ga mufeeda ki shafawa kanki lafiya ki kyale Anwar... Wallahi ko Zan rasa rayuwata bazan hakura dashi ba..... Duk suka zaro ido.
Amina ta ce wallahi matar sa da gaske sunyi Aure mufeeda ki fita batun Anwar ki tsira da mutuncin ki nifa nake gane Miki Yanzu irin wannan cin mutuncin keda dadi?
Ta goge kwallan da suka zubo ko Zan kyale Anwar sai na Rama wulakancin da ta mun wallahi bata Sha lale ba..... Ai kuwa next ba ita ce zata nada Miki duka ba wadannan kattin da ke gadin ta..... Ku duk baku San abinda naji ba, wallahi Anwar fa shine *Hamza bushara* ...... Duk suka kwalalo idanu suna kallonta. Da gaske Asma'u?
Tayi murmushi wallahi kuwa, aini tuni na Fara sensing Anwar wani shege ne ko Kuma baban sa ne wani don gadarar gayen tayi yawa ko lecturers Kuna ganin shakkar sa sukeyi..... Mufeeda ta saki wani irin kuka irin shikenan ta shiga uku kawai..... Amina ta dafa kafadarta kiyi hakuri ba class din ki bane Anwar maganar gaskiya sai irin su Bilkisun saboda Kinga babanta wani me itama tsaye take.... Ba wani babanta wallahi ko Yar gidan malam shehu ce tunda Anwar na sonta shikenan.....Kuma idan Kun tuna zuwanta ance sun Sha fada sosai da ita dashi tun farko ta nuna Bata tsoronsa, ke kuwa mufeeda ke ce Kika bayar da kanki yaushe Zaki ringa bin namiji Kuma guy kamar Anwar kema ai kinsan kin siya ma kanki buhun wulaknci.
Tana kokarin parking Aisha sauko daga napep ta shigo da gudu...... Wai kin daki mufeeda?
Ta fada tana shessheka , ta fito motar, ta bi su mustapha ( body guard ) da harara tayi ciki tana fadin Aisha yarinyar nan Bata da tarbiyya Kuma duk laifin Anwar ne...Anwar Kuma? Shi meye nasa aciki?
Ta hayayyako Mata tafi karfinsa ne da bazai ce ta kyalesa ba? Me yasa sauran Yan matansa ke tsoronsa ita kadai ce zakakka????
Amma Yanzu kinji yanda ake Mata Allah ya Kara a school? Wallahi mufeeda ta shiga uku ko kunya ta isheta kinji labarin da ake yi kuwa?... Maryam ta kallesu ya akayi ne? Tana kwance falo suka shigo
Ta cire hijab ta fada bedroom dinta.... Aisha ta zauna...wallahi Bilkisu ta nakada ma mufeeda tsinannen duka har tana cire Mata hular gashi..ta karasa maganar tana kyalkyatar dariya.. Maryam ta tashi zaune bani in Sha.....
Hmm yarinyar nan ta debo ruwan dafa kanta Wai inba ita jakka ba waye zai shiga shirgin Anwar da Bilkisu soyayyar da kowa ji yake da kansa, soyayyar da sukeyi ma juna ta gadara wa ita ta shiga tsakani????
....ta danyi kasa da murya Wai kinsan an daura musu Aure Ashe?
Maryam ta zaro ido.... Tayi saurin Dora yatsa a lebe alamar tayi shiru....
Haba nidai wallahi nayi mamaki abun fa akwai alamar tambaya.... Kuma kin San waye Anwar?
Ta zaro ido tana girgiza Kai alamar a'a.... *Hamza bushara*..... Ta kwalalo ido ta dafe kirji..kice wallahi.
Tayi Yar dariya wallahi kuwa ta budo Mata waya duba ki gani... A nuna Mata. Ta Kara zaro ido... Bilkisu ta sani?
Tayi dariya wallahi ta sani yarinyar can hmmm kibar ta kawai..... *Bushara* Maryam ta maimaita... Yanzu Bushara takeyi ma wannan iskancin Aisha..... Aisha ta kama dariya fitowarta yasa duk sukayi shiru....
Ta zauna bisa kujera Maryam kinyi break?
Eh, ta fada a darare....
Aisha tace naji ana Kiran wayar ki kuwa.... Ta janyo jakar sai kawai tayi tsoki ta wurgar.... Bazaki dauka ba?
Kyaleshi Anwar ne..... Maryam ta zaro ido..
Aisha tace me yasa bazaki dauka ba?
Me zance mishi?
Duk wannan hatsaniyar waye ya janyota?...... Meye laifin sa Bilkisu?
Ta Sha mur, Aisha har Yanzu Ina mamakin me yasa yarinyar nan ta kasa rabuwa dashi?
Kina ganin ba laifinsa bane??
Ba laifin sa bane..... Ta Mike tare da buga tsoki tayi kitchen......yunwa nakeji Maryam Ina masu aikin?
Maryam ta kalli Aisha itama ta kalleta Aisha ta kyalkyace da dariya Maryam kuwa kasa darawa tayi. Ta rike Baki *Bushara*..... Kut!
Ya kalli sadeeq nifa wannan fitinar yasa naso na mayar da ita Abuja kaga Yanzu da alama ni ne nayi laifi.... Sadeeq yayi murmushi ai dole taji haushin ka mufeeda ta kasa kyaleka itama tana nuna bata tsoronka kaga kuwa Bilkisu Dole ta tuhumeka....
... sadeeq ya zanyi da yarinyar Nan? Wulakancin duniya wane ke ban Mata ba?.... Duk da Haka ya kamata kayi wani Abu da zata kyaleka... Kamar ya? Dukanta zanyi?
Zagi na gidan duniya na Mata amma Bata da zuciya domin Allah meye laifina?
Ka barta zuwa anjima kilan ta dauka..... Bilkisun? Tabbb, yarinyar nan wuyar lallashi gareta Yanzu kaga Ni ta janyo mun jidali shegiya.... Sadeeq ya kwashe da dariya....

Soyayyar ku na birgeni nawan.... Ya Kai mishi duka wane birgewa Dan ubanka ana ba juna wahala....Au Ashe Kai ma ka San Haka... Sadeeq ko zaka je ka bata hakuri ?
Eh, Amma Bari ayi sallah tukun.... Wai mu Dan ubanka baka kawo Mana masu girki ba?
... ....... Ba wani Mai girki da Zan kawo, Ni nafi son ta dafa mun.... To ka kirata a waya ko ka Mata text.... Bari dai ta huce.
Ya harareshi to ai kaga irin wannan ranar da aka kafsa fada mune Masha wuya ko?....
Ya Mike Bari na dafa indomie.... Please zanci.... Baka cinta Dan ubanka..ya wuce Yana banka mishi harara.
Sadeeq yasha tsayuwar Shi taki fitowa, inda Allah ya taimakeshi suna da lecture four.......
Tana fitowa ta Kira mustapha.. kuyi wa Allah basai Kun bini ba Allah Yana tare Dani, bana bukatar tsaronku don kuwa bana wasa da addu'a...
Ya danyi murmushi toh Hajiya,....tana fita suka rufa Mata baya.....
Yana tsaye bakin kofa, ko kallonsa batayi ba ta wuce tana Zama shima ya zauna.... Ajin yayi tsit kowa ya maida hankalin sa wurin su don kuwa basa gajiya da dramar su. ....
Wai fushin na menene Bilkisu?
Ta harareshi kawai.
Yayi murmushi ke me yasa kin na son dauran laifi babu gaira?...... Au Ashe ma baka da laifi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login