Showing 12001 words to 15000 words out of 22968 words
a bakin aikinki" zaro idanu tayi waje sai tajima gaba ɗaya zafin mari ya kauce idan ta bar aiki tasan rayuwarta ta shiga wani hali.
Miƙewa Ayrah tayi suka fita daga office ɗin "Aunty Suhailat amma dai kin daɗe kina aiki anan ko?" "eh gsky na daɗe sosai Ayrah tun kafin zuwan wannan Mdee ɗin" "Alokacin wani Mdee ne azalumi. Kina so na baki labarinsa? gyaɗa kai tayi alamar eh "Okay Bari mu dawo daga sallah zan baki labarin"
ta faɗa dai-dai lokacin da suka isa masallaci.
Bayan sun idar da Sallah zama suka yi cikin lambu dake gefan gun
"Ada idan kikazo neman aiki tofa Mdee ɗin baya taɓa yarda ya ɗauke ki aiki Sai ya lalata ki. Idan baki yarda da haka ba toh sai dai salary naki ya zama zaku raba wannan dalilin yasa yan mata dayawa a lokacin suka shiga wata rayuwa wasu daka haka kuma suka koma karuwanci. Zaro idanu tayi tana kallonta "Amma toh Aunty Suhailat ke ya kika yi?" murmushi tayi "Alokacin da na zo neman aiki Mdee ya nuna min haka babu yadda zanyi saboda ina matuƙar bukatar aiki dan dashi zan taimaki iyayena dole ina ji ina gani yake raba salary na biyu ya ban rabi duk wata hantara idan ya tashi yimin yake haka ya mai dani p.a ɗinsa dan kawai ya cimma burinsa, da yake Allah shine mai kare bawansa sai Ubangiji ya tona masa asiri aka koresa duka daga wajan aikin
"Shiyasa zakiga wasu mata idan zasuje aikin Company suyita rawa kai wallahi ya wanci Company ma aikata su ko kaɗan babu Allah a ransu amma fa bana ce mike duka ba" "A'a wasu dan kin san a ko ina akwai nagari akwai na banza" "Haka ne Aunty Suhailat Allah ya sa mu dace" "Ameen ya rabbi" "Sannan ki dunga kula ba kowane zaina miki murmushi ba ki zaci sanki yake a'a wani yana da manufa a kanki ki yi a hankali sister ki san da suwa zakiyi mu'amala"
Sun daɗe agun suna tattaunawa kafin su meƙe su koma ciki "Kije office ɗin Mdee ko zai buƙaci wani abun, kiga lokacin tashi yayi" gyaɗa mata kai tayi ta na nufar left ta hau
Tana isa ta gansa zaune a ya na danna lapton ɗinsa da'alama kuma wani abun yake, zama tayi kan kujera sai da ya gama sannan ya ɗago ya kalleta "Yau bazan samu damar kai ki gida ba saboda ina da wani aiki so zansa drive ya Kai ki" "Toh shikenan nagode Sosai" "Ita kuma godiyar ta mece?" sunkuyar da kanta tayi batare da ta basa amsaba murmushi yayi ya cigaba da abun da yake
Fitowa tayi zuwa haraba Company drive na ganinta ya buɗe mata mota ta shiga, suna isa ta sauka tayi cikin gida, ta na shiga ta kwanta akan kujera "Wash Allah Mama wollah yau na gaji da yawa" "Ke kuma aikin me kika yi da kika gajin?" "Ni fa ba aiki na yi ba kawai gajiya na yi" "Raguwa ni nataɓa gani angaji ba tare da anyi aiki ba" "Allah Mama ana gajiya" ita dai Mama murmushi ta yi ta cigaba da abun da ta ke dan tasan idan ta biye Ayrah to bazata taɓa bari ta ba
[8/13, 4:06 PM] Masoyiya 🤗🔥: https://chat.whatsapp.com/BW8T7i1jpeZ5QpVVl4hxuZ
# SQUAD 2024
A WANI COMPANY
BY
HAUWAU OMAR
CUTIE MEEYRAT
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIONS
Fallow my account
Arewabook@hauwauomar05
Page_10_11
Washegari tun wuri Ayrah ta shirya tana jiran Suhail ganin lokacin sai tafiya yake ya sa ta tashi da sauri tanawa Mama bye bye. Tana fita bakin titi ta tsaida me napeep shiga tayi tana faɗa masa inda zataje. Suna isa ta fito tana bashi kuɗinsa ta nufi bakin get ɗin security da ke gun ta gaida tana shiga ciki, sai da tayi tafiya mai nisa kafin ta ƙarasa left ta hau
Tana isa office ɗin Mdee taji ƙofar a kulle nufar inda p.a take tai tana tambayarta Mdee baizo ba har zata mata masifa ta tuna magungun Mdee sai kawai tayi murmushi tana ɗaga mata gira "Yes Mdee ya je wani guri sai zuwa anjima zai ƙaraso nan so idan kinga bazaki iya jiraba sai ki koma gida sai ya dawo"
Bata ce mata komai ba ta juya tai tafiyarta abunta ƙasa ta sauka Suhailat ta gani da'alama kuma itama zuwanta kenan da sauri ta ƙaraso "Ayrah yau ke kaɗai kika zone? naga Kamar Mdee bai shigoba" "Eh Aunty Suhailat good morning" "Morning dear fatan kinzo lafiya?" "Lafiya qlau ta bata amsa yau kinga wani taro za'a yi a Company so karfe biyu kowa zaije gida sai bayan nan za'a dawo kamar 4:00 idan an tashi ki biyo ni muje wani waje dan shiryawa kinji" "a'a Aunty Suhailat zanje gida kawai sai na faɗawa Mam.. Kasa karasa maganar tayi ganin Mdee tsaye yana kallonsu da'alama kuma ya daɗe a wajan
Nufo su yayi ya na isowa wajan ya kalli Ayrah sai kuma naga ya cenza hanya yayi gaba abunsa murmushi Suhailat tayi "Maza kije ki kaima Mdee coffee kin ji" "toh tace tana bin bayansa suna isa office ɗin p.a ta gaidasa ƙasa-ƙasa ya amsa ya na nufar na sa office ɗin. Ya na shiga ta turo ƙofa ta shiga
Tunda ta shiga taga ko ɗagowa ya kalleta baiba, nufar wajan coffee tayi ta haɗa masa aje masa a kan table ɗin tayi wata tsawa ya daka mata wadda tasa gaba ɗaya hanjin cikin ta ɗaurewa "Ke wace kalar sha-sha-sha ce? kinji nace miki ina bukata ne?" ya faɗa a tsawace jikinta ne ya fara wani irin rawa dan-danan hawaye ya shiga zuba akan fuskarta so take ta bashi haƙuri amma bata da karfin haka tsaki yayi ya zauna akan kuje yana dafe kansa da hannu biyu "Ya salam" ya furta a hankali ya na rufe idanunsa shin me yake shirin aikatawa ne ohh ya Allah
Da gudu ta fita daga office ɗin p.a dake zaune takaleta tana mamaki dalilin da yasa ta fito tana da gudu tana kuka. Ƙasa ta sauka tashiga office ɗin Aunty Suhailat tana shiga ta rungumeta tana wani irin kuka numfashi tane ya fara sarƙewa dalama kuma ciwonta ke ƙoƙarin tashi Suhailat hankali ta ne ya yi mugun tashi da sauri ta kwanta da ita ta fita waje a guje ko left batai tunani hawa ba ta shiga haura bene da bibiyu gaba ɗaya ta shiga damuwa buɗe ƙofar tayi ta shiga tana haki p.a tsayawa tayi tana kallon ta ko bin ta kanta bataiba ta shiga cikin office ɗin Mdee ganin Suhailat a wannan yanayi yasa yayi saurin meƙewa yana kallonta nuna masa ƙofa kawai take ta kasa magana "Menene ya faru ki nutsi ki faɗamin" "Sir Ayrah" "Ayrah sir" tun kafin ta karasa ya fita da sauri ya na sauka ya faɗa cikin office ɗin p.a na biye da shi samunta yayi kwance idanunta a rufe da sauri ya ƙarasa ya na taɓata. Ɗaukarta yayi zuwa pearking lot tun daga nesa yake ƙwalawa drive kira da sauri ya taso ya zo ya buɗe masa motar shiga yayi yana ruƙe da ita suka nufi asibiti Company
suna isa asubiti da sauri Dr ya sa aka shiga da ita ɗaki gaba ɗaya Suhail ya rasa nutsuwarsa ji yayi hawaye na bin kunchisa da sauri ya saka hannu ya na gogewa ya san koma me ya faru shine sula shi yaja da baimata tsawa ba da hakan bazai faruba
Mama da ke zaune tan kaɗe gari dan bata so Ayarh ta dawo bata gama girkin ba tasan hali ji tayi gabanta yayi wani irin faɗiwa a hankali ta dafe ƙirjinta tana ambaton sunan Allah laila hailla anta subuhanaka inni kuntu mina zalumin shi take ambata a zuciyarta
Sai da suka ɗauki kusan 20m kafin su fito daga room ɗin. Da sauri ya miƙe ya na ƙarasawa dan jin me yake faruwa dafa kafaɗarsa Dr yayi kafin ya ce "Muje office sir" babu musu ya bisa suka shiga office ɗin nasa zama yayi akan kujera yana nuna masa shima kujera babu musu ya zauna, cire farin glass ɗin dake fuskarsa yayi ya na duban Suhail "Bakomai ne ya haifarma da wannan shiga yanayi da ba tashiga ɗinmuwa ne kasan a wasu lokuta mutum idan bai saba da abuba toh aduk lokacin da abun ya faru da shi ya na shiga gigici da ɗimuwa kuma ita yarinya ce qarama, dole ne sai an dunga kiyaye wasu abubuwa sir "Insha Allah za'a na kiyayewa, yanzu zan iya ganinta?" "why not yanzu haka tana ɗakin hutu zaka iya zuwa, zuwa anjima idan ta tashi zaku iya tafiya" godiya ya masa ya miƙe ya fita
A cikin company kuwa kowa ya ya fito a office ɗinsa sun tsa-tsaya sai mai da magana ake ita dai Suhailat tana gefe ta haɗa hannuwa ta biyu a fuska babu abun da ke zuba daga idanunta sai hawaye, gashi babu damar ta bi su Mdee hospital ɗin. Yana shiga cikin ɗakin ya tarar da ita kwance tana bacci karasawa yayi gaban gadon ya zauna ya na kallonta "Am sorry Ayrah ni ne naja miki kiyi haƙuri bazan ƙaraba kinji", ya faɗa Kamar ta na jinsa hannuta ya ruke cikin nasa kiran dad ɗinsa ne ya shigo cikin waya da sauri ya ɗaga a ɗaya ɓangaren kuma dad ya masa "Hallo son kana lafiya" "Lafiya qlau dad" "Masha Allah karka manta da taron yau fa ka san taren na da matuƙar muhimmanci ko?" shiru yayi dan shi gaba ɗaya ma ya manta da wata maganar taro 'Ko baka jinane?" "Ina jinka dad insha Allah bazan manta ba" "Toh Allah yasa muma munan muna shiri"
Yana katse kiran ya kira h.o.d cikin Company "Ku shirya komai da za'a bukata na taro, karku damu sai na zo no kuyi komai yadda ya kamata" "Okay sir Insha Allah za'a yi hakan" katse wayar yayi ya na duban Ayrah da ta ke bacci abunta 2hours later
A hankali ta ke buɗe idanunta ganin Kamar mutum a zaune a inda ta ke yasa ta saurin karasa buɗe idanunta murmushi ya sakar mata dauke kanta tayi daga kallon nasa "Sannu ya jikin" banza tayi masa tana tuna abun da ya faru wani sabon kuka ta fara "ya ilahi ki yi shiru Please ki daina kuka nan dan Allah" "Ni ka kaini wajan Mamana bana son zama anan" "Naji zan kai ki amma sai kin yi shiru" mai makon ma tayi shiru sai ta cigaba da kukanta tashi yayi har ya kai bakin ƙofa ya ce "Taso muje ai da sauri ta duro akan bed ɗin ta bisa a baya dr suka gani na ƙoƙarin shigowa murmushi yayi "Sir kace har kun fito" "Eh" ya bashi amsa a taƙaice su na isa haraba hospital ɗin drive ya ta so da sauri "Ka koma Company ni zan kaita gida" "Okay sir" ya faɗa yana buɗe masa motar zagayawa yayi ya buɗewa Ayarh ta shiga da gudu ya ja motar dai-dai wani ɗan ƙaramin stor ya tsaya ya siya mata abun da zata iya ci tare da kayan tea
Dawowa yayi cikin motar yaja suka tafi, suna isa ƙofar gidan da sauri ta buɗe zata fita ruƙe mata hannu yayi yana girgiza mata kai kwaɓe fuska tayi zatai kuka "Shiit ni bacewa na yi kimin kuka ba," ya faɗa ya na miƙe mata leda "Idan kin shiga gida ki gaida min da Mama sananan ki bari sai kinji sauƙi kya dawo aikin kin ji? Allah ya baki lpy kuma kiyi haƙuri nasan nine naja miki" "Babu komai nagode" ta faɗa ta na fita daga motar kwanta da kansa yayi a jikin kujera ya na murmushi shi kaɗai ya san abun da yake ji akan yarinya ganin har ta daɗe da shiga gida ya sa ya ja motarsa yayi gaba
Kai tsaye gida ya nufa dan baijin zai iya komawa Company a wannan yanayi ya na isa ya nufi falon ya nasa
Tana shiga Mama ta ta so tana tambayarta lafiya fashewa tayi da kuka tana rungumeta, ruƙeta tayi suka nufi cikin ɗakin suna shiga ta kwanta akan tabarma "Wai Ayrah menene ya faru?" "Kai nane fa ya ke ciwo" ta faɗa a shagwaɓɓe "Amma ke kam wai yaushe zaki daina kukan ciwon kai ni Allah na zata ma ko wani abune ya faru tashi toh ki ci abunci kisha magani" "A'a Mama ni na ƙoshi ta" faɗa tana miƙa mata ledar da Mdee ya bata "Ita kuma wannan ledar menene a ciki?" "Mdee ne ya siyamin kuma ma ya ce na gaidaki" "Toh Ina amsawa mungode sosai da ɗauwai niyar da ya ke" ita dai Ayrah bata sa ke cewa komai ba ta rufe idanunta
Da da dare suna zaune Ayrah ta dubi Mama "Wai Mama mu Shikenan haka zamu cigaba da rayuwa mu kaɗai?" shiru Mama tayi bata ce komai tabbas itama a koda yaushe tana wannan tunani shin idan rayuwa ta ciga da tafiya haka watara na fa zata mutum alokaci sai dai yar'tata ta yi itama rayuwa ita kaɗai, ganin hawaye na zuba akan fuskarta ya sa ai Ayarh saurin nufo in da ta ke "Dan Allah Mama kiyi haƙuri idan magana ta bata miki daɗi ba" murmushi kawai tayi tana rungumeta adaran dai haka suka kwana cikin tunani rayuwarsu
Washegari da wuri ya tashi ya shirya yana fitowa security ya buɗe masa motar ya shi, su na isa ya shiga office, Suhailat da dama zuwansa ta ke jira, ta tashi da sauri ta nufi office ɗinsa kanta aƙasa ta shiga da salama amsawa yayi ya ɗago ya na kallonta "Good morning sir" "Morning how are you" "fine" "Dama sir tambayarka zanyi ya jikin Ayrah" "Jikinta da sauƙi tana gida, sai bayan ta ƙara samu sauƙi zata dawo aiki" ya faɗa yana danna lapton ɗin dake gabansa "Okay Allah ya bata lafiya" "Ameen ya rabbi" godiya ta masa tana fita daga office ɗin
Tana fita p.a ta tare ta "Am me Mdee ya ce akan yarinya, har yanzu tana asibiti" wani kallo Suhailat ta mata tana wucewa abunta "Mtss kada Allah ya sa ki faɗa yar raini hankali, daga gani yarinya shikenan kunbi ku liƙe mata Allah shiƙara wallahi ni na so ma ace ta mutu muga ƙarshen iskanci"
[8/13, 4:06 PM] Masoyiya 🤗🔥: https://chat.whatsapp.com/BW8T7i1jpeZ5QpVVl4hxuZ
A WANI COMPANY
BY.
HAUWAU OMAR
CUTIE MEEYRAT
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIONS
fallow my account
Arewabook@hauwauomar05
Page_12_13
Yau kusan kwanan Ayrah uku agida bata zuwa aiki. Gaba ɗaya baya jin daɗin aikin ji yake Kamar akwai wani abu da yayi giɓi cikin aikin na sa. A hankali ta mike da ga kwance da ta ke ta na kallon Mama meƙewa tayi ta shiga toilet dan yin wanka, ta na fitowa ta nufi cikin ɗakin ta shirya tsaf cikin doguwa riga ta atamfa hajjab ta zura Masha Allah ta yi kyau sosai fitowa tayi ta na wa Mama bye bye ta fita sai da tayi tafiya mai nisa kafin ta samu mai napeep ɗin da zai kaita zuwa Company tana isa ta shiga ciki office ɗin Suhailat ta shiga ta na ganinta ta miƙe da sauri ta rungume ta "Oyoyo sister yau kinzo kenan?" murmushi tayi tana gyaɗa mata kai "ya jikin naki?" "da sauƙi Aunty Suhailat"ta ce" Masha Allah Mdee ya san kinzo ne?" "a'a yanzu na zo ai" ta ce"Okay maza kije zuwa anjima kya dawo kinji" fita tayi ta nufi office ɗin Mdee ɗago kai p.a tayi ta na kallonta dan ita gaba ɗaya ma ta manta da ita wuce wa tayi zuwa ciki yana ganinta ya ya yi murmushi, Murmushi ita ma tayi tana zama akan kujera ya ce" ya jikin na ki?" "da sauƙi" ta bashi amsa.
Kasa tashi tayi ta haɗa masa coffee dan tana gudu abunda ya faru ranan ya sake faruwa jita yi ya ce "coffee" jiki a sanyaye ta miƙe ta nufi wajan haɗa coffee ɗin tana haɗa masa ta zo kan table ta ajiye zama tayi akan kujera tana wasa da yatsun hannunta sai da ya gama tsaf kafin ya miƙe kallonsa tayi nufar ɗakin hutunsa yayi ita dai tanan zaune har ya shige kuma bai mata magana ba ta kai kusan 20munith kafin ya fito cikin cuz brown Masha Allah yayi kyau sosai.
hanyar fita yayi juyowa yayi yana kallonta ganin ba shi take kallo ba yasa ya ce "muje ko" ɗagowa tayi ta na kallonsa dan bata gane inda maganarsa ta dosaba "cewa nayi ki taso muje" babu musu ta miƙe ta bi bayansa p.a na ganinsa ta miƙe karasawa yayi "bani file ɗinnan" miƙa masa tayi har yayi gaba tace "am sir ko nazo muje tare ne?" "ban nemaki ba idan da ina da bukatar hakan da zan faɗamiki" shiru tayi bata sake cewa komai ba har suka fita zuwa waje
Shiga yayi cikin motar itama ta shiga suna isa drive ya fito ya na buɗe musu ƙofa tana ganin inda suka zo ta haɗe rai haka kurum a bar mutum shi kaɗai har ya gaji murmushi yayi ya na juyowa ya kalleta dan ya ji abunda ta ce ganin ya na murmushi ya sa tayi shiru suna isa ya nuna mata wajan zama karasawa yayi wajan meeting ɗin
Mrss Afif ne ya dubesa ya ce" muna bukatar gine mai kyau na zamani mun yi la'akari da kaf Company babu kamar wannan shiyasa muka kawo kwangila mu nan" haka suka cigaba da tattaunawa tun tana sa ran zai taho su tafi har ta gaji meƙewa tayi ta fita ganin ta fita ya sa hankalisa ya dawo kanta ko ina zata sai ya ji ya kagu su tashi daga meeting ɗin tana fita kai tsaye wani lambu mai kyau ta karasa lambu cike ya ke da bishiyoyi daban daban Kamar su mangoro, gwaiba, dabino banana, da dai sauransu ai ta na ganin bishiyar mangaro ta karasa da sauri ta na murmushi dan ta na matukar kaunar mangoro wani dutse ta gani agun da sauri ta karasa ta