Showing 9001 words to 12000 words out of 22968 words
you son"
cigaba sukai da wayar ta su cikin farin ciki da kaunar juna su na gama wayar ya kashe lapton ɗin ya na lumshe idanunsa tabbas ya na natukar son mahaifansa baya iya haɗasa da komai
Tashi ya yi ya nufi ciki dan ya samu yayi bacci.
Cire kayan da ke jikinta ta yi ta nufi bayin na su ta watsa ruwa ta na fitowa ta tsaya a gaban wadrop ɗin ta su ta na kare mata kallo tinani kayan da za ta saka ta ke, ganin har kusan takwas ta yi ba ta fito ba ya sa Mama ta tashi ta shiga ɗakin tsaye ta ganta a jikin wadrop ɗin ta zu ba mata idanu murmushi ta yi kawai ta karasa ta na taɓata, da sauri ta dawo da kallonta kan Mama "Ke kuma lafiya? ki ke ta kallon wadrop Kamar kinga sabon abu" turo baki ta yi kamar zatayi kuka kafin ta ce "Ni to ba rasa kayan da zansa na yi ba" "Tofa yau nabanu wai Ayrah yaushe zaki daina wannan halayyar taki? ace kullum mutum in ya yi wanka sai ya ta ruwan ido, kafin ya sa kaya" Mama ta faɗa ta na janyo wata marron ɗin abaya cikin abayoyin da Mdee ya siyamata "Ingo wananan ki sa ka" karɓa ta yi ta na murmushi zura riga ta yi a jikinta wow Masha Allah yanda kasan dan ita aka yi riga, ba karamin kyau ta mataba ƙarasawa wajan mero ta yi ta shafa tirare da leps glows a bakinta kama kanta ta yi dan ɗaurewa tin ta na yi ta na ganin za ta iya harta fashe da wani irin kuka mai cin rai. ƙarasowa Mama ta yi ta kama kan ta na ɗaure mata da wani white ribom mai kyau, hula riga ta sa ka white sai belt na riga shima white ta yi rolling dashi, takalmi ta zura plat. ba ƙaramin kyau Ayrah ta yi ba yadda kasan yar turai. fitowata yi ta na ɗagawa Mama hannu. Fita ta yi waje ta na tunani ta yadda zata tari abun hawa ya kaita Company. Turus taja ta tsaya ganin wata arniyar mota kirar pontic gto(1964). Tsayawa ta yi ta na kallon motar a hankali ya sauke glass ɗin ya na sakar mata murmushi, murmushi itama ta yi ta na nufar wajan motar. Da sauri drive ya buɗe mata tashiga, godiya ta masa ta zauna "Good Morning sir" "Morning" "how are you today" "fine" ta bashi amsa a taƙaice
Su na isa cikin Company ta buɗe murfin, "Ba kiji ba"ya faɗa a hankali juyowa ta yi ta na kallonsa, ganin idansa har yanzu a lunshe kamar bashi yayi magana ba "Kinyi Kyau sosai" "Thank you very much" ta faɗa ta na fita a motar shima fitar ya yi ya nufi hanyar da za ta sadashi da left, sai murmushi ya ke shi kaɗai kamar wanda akaiwa bushara 😂
Ya na shiga ya nufi office ɗinsa da fara p.a ta gaidasa ko kallon inda ta ke baiba bare ta sa ran zai amsa mata. Jiki a sanyaye ta karasa kan kujerata ta zauna hawaye ne ya fara zarya akan kuncinta. Turo kofar ta yi ta shiga bakinta ɗauke da salama da sauri ta goge hawayenta ta na gallawa Ayrah harara, sunkuyar da kanta ƙasa ta yi tai gaba abunta ta na shiga ta nufi wajan haɗa coffee dan ta san zai bukacesa zuba mata idanu ya yi yana kallon yadda ta ke komai cikin nutsuwa samun kansa yayi da sakin wani murmushi wanda shi kansa bai son manufar yinsa ba
"Sir" "Sir" gaba ɗaya ya faɗa duniyar tunanin baima san ta na masa magana ba sai da ta bibuga table ɗin sannan ya dawo hayyacinsa karɓa ya yi ya na kaiwa baki ƙara lumshe idanunsa ya yi ya na kai kofin bakinsa sai da yasha sosai kafin ya ɗago ya kalleta. "Yau baki tawo da abinci Mama ba?" gyaɗa ma sa kai ta yi alamar eh "Dama ina son na maka godiya da kayanan nagode sosai Allah ya saka da alkhairi, Mama ma ta ce na maka godiya" "Babu komai na yi dan Allah so dan haka ni aganina ba abun godiya bane." "Sannan daga yau duk abunda da na baki ba na son godiya kinji" ya faɗa ya na kafeta da idanunsa ma su matukar kwarjini saurin sunkuyar da kanta ƙasa ta yi dan bazata iya jurar kallonsa ba.
Da salama ta shiga ciki office ɗin wanda baida wani girma samunsa ta yi zaune ya haɗa hannusa biyu akan fuskarsa da alama wani abun yake tunani. Murmushi ta yi ta na karasawa ciki, hura masa iskar da ke bakinta ta yi "Lafiya kai kuma ka ke ta fama tunani?" murmushi kawai ya yi ya na cije leɓansa na ƙasa "Hmm wallahi har yau na kasa mantawa da abunda Mdee ya min akan yarinyar nan" "Kaima kenan daba wani abu ya maka ba" "Ni tozartani ya yi agabanta😥 "Ni da na ke matsayin p.a ɗinsa amma ko ta ni bayayi, sai wata ƙaramar yarinya" tsaki ta yi mai sauti dan a duk lokacin da ta tuna wa ta irin wutar tsanar Ayrah ke karuwa tabbas ta yi alƙawarin sai ta wahala da yarinya wahala wadda ko aljan sai yaji tausayinta bare mutum. "Wai me ki ke tunani ne? ina miki magana kin min banza kin san fa ba na ɗaukar wulakanci ko" Abdul ya faɗa a hasale "Kaifa daɗina da kai rashin haƙuri ina tunani yadda zan wahala da yarinya ne, da yadda zan rama abunda tamin" wa ta irin dariya ya sheƙe da ita ya na kallonta "Ina jinki me kike tunani kenan?" murmushi ta yi ta na gyra zamanta akan kujera. Matsawa ta yi dab da shi ta raɗa masa wani abu akune wata irin dariya su ka sheƙe da ita su duka, su na tafawa "Sai yanzu na kara yadda da ke wace" "Kai dai kawai ka kasance cikin shiri dan a koda yaushe zakajini na nemaka" "Angama shugaabar mugaye duniya" wata dariya ta karayi ta na fita a office ɗin
rungumeta Hajiya ta yi su na kuka "Idan Ayrah ta dawo kice ma ta mun tafi" gyaɗa kai Mama Ayrah ta yi har sun shiga mota Habib ya fito "Aunty idan Ayrah ta dawo kice zan yi kewarta sosai, ki gayama zanzo na ɗauketa mu koma Australia tare" murmushi Mama ta yi ta na goge hawayen da ke fuskanta..
A hankali ya tashi ya nufi cikin ɗakin da ke office ɗin sai da ya kusa shiga kafin ya tsaya ya na duban Ayrah "Kije office ɗin su Suhailat, kuma bayan nan ban yarda kije ko ina ba" gyaɗa ma sa kai ta yi alamar toh fita ta yi da ga office ɗin kanta a sunkuye ganin p.a ba ta office ɗinta ya sa ta sa ki wa ta irin ajiyar zuciya mai ƙarfi, dan gaba ɗaya ba ta son ganin Suhailat
Da murmushi Suhailat ta tare ta "Yau sai yanzu ake ganinki" zama ta yi ta na gaidata amsawa ta yi cikin sakin fuska "Ina kika shiga yau?" "Babu ko'ina ina office ɗin Mdee" "Okay" Suhailat ta ce ta na chanza hira "ki na son wani abu ne?" "A'a Aunty Suhailat na ƙoshi" to ai ba cewa na yi nima baki ƙoshi ba, ina nufin kamar beskit chocolate da dai sauransu" murmushi Ayrah ta yi jin an ambato kayan kwaɗayi
[8/13, 4:06 PM] Masoyiya 🤗🔥: https://chat.whatsapp.com/BW8T7i1jpeZ5QpVVl4hxuZ
# SQUAD 2024
A WANI COMPANY
BY
HAUWAU OMAR
CUTIE MEEYRAT
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIONS
Fallow my account
Arewabook@hauwauomar05
Page_ 8_9
Ana tashi ta fito harabar Companyn don tafiya gida,ko office ɗin Mdee ba ta koma ba. fitowa wajan get ɗin tayi sai da tayi kusan 5minth bata samu abun hawa ba, hakan ya sa tashiga takawa da ƙafa ta na tafiya dafe kanta tayi saboda wata rana da ake gashi ko rabi bata yi ba, jin horn a bayanta ya sa ta yi saurin juyawa zuge glass ɗin motar ya yi ya na mata wani irin kallo, sunkuyar da kanta tayi ƙasa da sauri ta na wasa da yatsun hannunta
Nuna mata motar yayi alamar ta shiga, babu musu ta shiga kuma har lokacin kanta na ƙasa suna isa ƙofar gidan na su ta buɗe ta fita ko magana bai mata ba yaja motarsa yayi gaba jiki a sanyaye tashiga cikin gidan na su ganin bataga Mama a tsakar gida ba yasa tayi cikin ɗakin, samunta ta yi zaune ta na karatu al'Qur'ani mai girma zama tayi ta na murmushi.
Yana shiga gida faɗawa yayi saman kushin ɗin gaba ɗaya yau ya gaji lumshe idanunsa yayi ya na sauke numfashi tinani rayuwarsa ta baya da ta yanzu ce ta shiga dawo masa hawaye ne ya fara zarya akan kuncinsa tabbas bashi da wani gata sai na mahaifinsa mahaifiyarsa ta tafi ta barsa tin baisan ma menene duniyar ba haka ta watsar da shi ta tafi kawai dan basu da kuɗi alokacin. Allah kenan mai azurta bawansa a sanda ya so mahaifiyarsa taci amanar Daddysa taje ta auri abokinsa kawai dan shi baida kuɗi alokacin bata damu da rayuwar da zasu shiga ba haka ta barsu kuma har yau bata wai wayesu ba tuna irin waɗannan abubuwan ya sa ya kara fashewa da kuka mai cin rai idanunsa sun yi wani irin ja abun ka da fari nan da nan fuskarsa tayi ja a hankali ya kwanta ya na wani irin numfashi aduk sanda Suhail ya tuna waɗannan abun tofa yana shiga cikin wani irin hali ne . Tun yana numfashi a hankali har ya nemin fun ƙarfinsa miƙewa yayi ya shiga bathroom ya sakarwa kansa ruwa mai sanyi yana fitowa ya goge jikinsa da towel ne ɗaure a jikinsa ya kwanta yana rufe idanu kuma har lokacin hawaye bai daina zuba akan fuskarsa ba
Wanene Suhail?
Suhail Arif shine ai nayin sunansa asalin mahaifansa bature ne haka ma mahaifiyarsa
Austiralia. Calvary public hospital
Ihu ne ke tashi a dai-dai room 003 dake cikin hospital ɗin a hankali kuma ihu ya fara disha shewa kyakyawa mutune tsaye a bakin ƙofar idanunsa a rufe da alama yana cikin yanayi na damuwa jin kuka jariri da yayi ya sa yayi saurin shiga cikin ɗaki kwance take akan gadon na marasa lafiya daga ganin yanayi yadda take bacci zaka tabbatar da cewa a wahalce take da sauri ya karasa ya ɗauki jaririn dake gun yana rungumesa tsam a jikinsa kamar wani zai rabasa da shi sun kai tsawan muntina 20 a haka kafin ya ɗago ya kalli matar da ke kan gadon wani uban harara ta watsa masa tana jan tsaki nufar idan da take yayi da sauri ta dakatar da shi da hannunta "karka sake ka kusanci inda nake Arif saboda baka da wani amfani a gare ni cikin dake jikina ne na haife maka kuma na barmaka shi har abada bana fata ka faɗa masa yana da wata uwa wadda tai kaman ceceniya da ni talaka kawai wllh nayi nadamar auran matsiyaci kamar ka kuma ina so kasani aurena da Mahabub babu fashi" ta faɗa tana tashi daga kan bed ɗin ko damuwa da ciwon da jikinta ke mata bata yiba ta nufi hanyar fita da sauri ya karasa gabanta ya na haɗa hannuwansa biyu alamar taji tausayin su ratsesa tayi ta fita tana jan tsaki durkushewa yayi ya na fashewa da wani irin kuka mai cin rai tabbas Mahabub ya cuceshi ya ci amanarsa yanzu da gaske dama Sarah zata iya barinsa saboda kuɗi shin me yasa bata ji tausayin ɗan da yazo duniya ba yau duk wannan maganganu shi kaɗai ya ke yinsu kamar wanda aka tsikara ya miƙe ya ɗauki jaririn nufar hanya futa yayi daga hospital ɗin gaba ɗaya
Haka rayuwa ta ciga da tafiya Suhail ya taso wajan mahaifinsa kullum shi yake kaisa makaranta ya ɗaukosa bayaso ko wani ƙwarzane ya taɓa masa ɗa watarana ya dawo daga school ya nufi parlon su jun haya niya yasa yayi saurin tsayawa ya na saurare "Arif kenan ban fa na zo ne dan na tambayi ya kake ko ya ɗanka ya ke ba a'a nazo ne dan naji ance kayi kuɗi shine nazo dan kabani nawa kasan tunda dai dani akasha wahala" da wani kallon ya watsamata "Tabbas baki da imani Sarah baki ko tambaye ni ya ɗan ki ba sai Maganar dukiya abar banza wannan damuwarka ce ni koma ya yake bai dameni ba to bazan bayar ba Sarah ina lokacin da bani da kuɗin gudu na ki kai kuma ki maza ki fita a gidanan kafin nasa security su fitarmin dake" ganin da gaske ya ke babu wasa yasa tayi ƙwafa tana fita a ɗakin Suhail da idanunsa ke zubar da hawaye ya tsaya yana kallonta tsaki taja tayi gaba abunta da gudu ya shiga cikin parlon yana faɗawa jikin dad ɗinsa numfashinsa ne ya fara sarƙewa da gudu dad ya ɗauke sa zuwa hospital ɗin dake cikin gidan tun daga wannan lokaci Suhail ke fama da ciwo a zuciyarsa har izuwa wannan lokaci.
Wannan kenan.
Sai kusan la'asar ya tashi a bacci miƙewa yayi yana ambaton sunan Allah, bathroom ya shiga ya ɗauro alwala ya gabatar da Sallah.
Mama ce ta dubeta tana murmushi "yau kin daɗe Ayrah lafiya?" murmushi tayi tana bata labarin abun da ya faru "ke yanzu taya zaki iya zuwa gida dama a ƙafa karki kuskura ki ƙara wannan ganganci" "tom Mama insha Allah". "Kin san kuwa su Habib sun tafi yau ya ce na ce miki zai yi missing ɗin ki sosai kuma wai yanan zaizo ya ɗaukeki ku koma cen tare" murmushi "Allah sarki ya Habib nima zanyi Miss ɗinsa sosai Mama".
Washegari da wuri ta fita dan karta ɓata masa lokacin tana fita kuwa ta gansa cikin mota ganin kamar babu drive yau ya sa abun ya bata mamaki buɗe baya tayi zata shiga jin muryasa tayi yana magana "kenan niɗin drivern kine da zaki wani shiga baya?" fasa shiga bayan tayi ta buɗe gaban ta shiga.
"Dole ne kayi taka tsantsan saboda kar Mdee ya gani ta camera" murmushi yayi "haba wai bana ce miki na kashe camera office ɗinsa ba" murmushi kawai tayi suka cigaba da zuba abun ya a hankali ya buɗe office ɗinsa ya shiga itama shiga tayi ta nufi kujera ta zauna "kawomin coffee" miƙewa tayi dan kawo masa jin ta kasa tashi akan kujera sai ƙokarin tashi take amma abu ya gagara ganin tana ta ko kawa ya sa ya ce "me yake faruwa?" ɗago idanunta tayi wanda ya fara zubda ruwa "na kasa tashi" "what kin kasa tashi kamar ya ba yanzu kika zauna ba?" "Allah da gaske nake" ta faɗa hawaye ne ke ambaliya a fusakarta ganin tana kuka yasa ya miƙe dan ganin meke faruwa saka hannunsa yayi ya janyota amma ya ga ko motsi bata yiba durkusawa yayi dai-dai kujera yana dubawa murmushi kawai yayi ya nufi cikin wata drowa hannusa ruƙe da wata roba ya dawo ganin ya na zuba mata ruwa a jiki yasa ta fashe da kuka "sheet" shine abun da ya ce kin shirun tayi ta cigaba da kukanta ƙara janta yayi ta ko faɗa jikinsa wani irin faɗuwar gaba ce ta ziyarce sa sai yaji Kamar ya taɓa shork da sauri ya rabata da jikinsa ya na komawa ya zauna "kije office ɗin ƙasa zan nemaki anjima" tana sha shekar kuka ta fita wata irin dariya p.a ta tintsire da ita a lokacin da tazo wucewa ita dai bata kobi ta kanta ba ta fita abunta
Suhailat ganin hawaye akan fuskarta ya sa ta miƙe da sauri tana rukota "menene ya faru Ayrah?" hawaye ne ya kara zubowa "ki yi shiru Please ki faɗamin kinga kin tayarmin da hankali" bata labarin abun da ya faru tayi shuru Suhailat tayi tana nazarin abun kafin tayi murmushi kawai ta bar magana "to kiyi shiru kinji ina ga wani abune a wajan" goge mata hawaye dake fuskartata tayi ta na cewa "yauwa ko kefa nifa sai nagama kamar idan kina kuka kinfi kyau wollah" murmushi kawai tayi tana boye kanta akan cinyarta.
P.a miƙewa tayi da sauri ta nufi office ɗin Abdul ta na shiga ta tuntsire da wata muguwar dariya shima dariya yayi "albishirinki?"ta ce" goro" ya bata amsa "part one dai munyi nasara saura two" ya ce" a haba dai?" Ta ce" ai dama na faɗa wallahi Sai yarinya ta gane kuranta naso ma ace bai gane menene a kujera ba kasan nan gaba menene shirinmu?" girgiza mata kai tayi alamar a'a matsawa tayi ta raɗa masa a kune "gaskiya wannan shawara taki ta matukar yi tabbas ranar muna da shan kallo a Company nan" ta ce" sosai ma kai dai kawai a zuba eyes kaga yadda zan juya rayuwar yarinyar".
Mikewa yayi ya fita office ɗin h.o.d na Company ya shiga da sauri ya miƙa ya na gaidasa amsawa yayi cikin sakin fuska dan duk cikin ma'aikata gidan babu wadda ya yarda da shi kamar h.o.d zama yayi ya na masa magana lokacin "ɗazu kafin na shigo Company an kashe Camera dake office ɗina menene dalilin haka?" "sorry sir ɗazu p.a ke faɗamin wai na bada umarni a kasheta saboda za'a yi wani gyara ne a office ɗin naka wannan dalilin yasa na kashe" ya ce" ita p.a ɗin ce ta faɗamaka haka?" "eh sir" murmushi yayi yana cije laɓansa na ƙasa "sir ko haka da matsala ne" ya ce" a'a babu wani matsala" ya faɗa ya na miƙewa yana fita ya koma office ɗinsa zaune ya ganta tana danna waya a zafafe ya ƙarasa in da take ya ɗauke ta da mari wani irin taurari ta shiga gani suna giftawa ta fuskarta "sha-sha-sha mara tunani duk ranar da kika sake maka manci haka kin ji na faɗami Wllh