Showing 3001 words to 6000 words out of 27913 words
ke faɗa min sai kuma ya rinjaya. Ya numfasa. "Ni ma dai Babyn ya fi min daɗi, amma zan kira kowanne in na so ko?" Na Ɗaga kai alamun eh.
Ya yi 'yar gyaran murya "Baby gaskiya ina son ki kamar yadda na faɗa ɗazu, in har ki na sona to aure ya kawo ni kamar yadda na faɗawa Abba ɗazu. Sanna bazan ɓoye miki komai ba,ina da yara uku duka mata,kowacce mun rabu da mahaifiyar ta... Saboda me? Na jeho masa tambaya ba tare da na sani ba. Ya ɗan yi dim, sannan ya ce "Saboda Allah, kar ki damu sannu zaki san komai. Ya ci gaba Ni ƙaramin ɗankasuwa ne ina tsare shagon mai gidana a Kantin kwari. Fatan kin fahimta?" Na ɗaga kai tare da faɗin umm. Take zuciyata ta sare kuma ta soma tuhumarsa. Mata uku, kuma ba ko ɗaya yanzu, gaskiya ya kamata insan dalili. Ya katse min tunani da cewa, "Baby ta bakin ki na ke son ji ko kina so na kuma za ki iya aure na? Ni dai komai na ki ya yi min. Na numfasa cikin sanyi jiki na to gaskiya ni dai bansani ba ko ina son ka domin ban taɓa samun kaina a cikin shi ba to bansan ya yake ba. Sannan magana aure Allah shine mai ƙullawa, in har ya ƙaddari hakan zan amsa hannu biyu. Yace "Har yanzu dai ban samu amsa ba,amma zan baki zuwa jibi, kiyi nazari kuma ki ƙoƙarta ki gano ko kina so na." Na ce, to na gode kuma zanyi yadda ka ce. "Bani lambar wayar ki zan kira kafin jibin inji wannan sanyayyar muryar." Na ce sai dai in baka ta Ummanmu, saboda har yanzu Abbanmu bai sai min ba, yace sai mun gama walimar saukar ƙur'ani. Yace to bani ta ta ɗin, na faɗa masa sai ya yi flashin yace, "Inkin shiga sai kuyi sebin domin inna kira kai tsaye kinsan ni ne." Nace, to. Yace "Nine ɗan auta a gurinta, kuma ni kaɗai ne namiji, yayinda huɗu duk mata, Yaya Zainab ce babba,sai Maryam A'isha da Fatima duk suna aure a nan cikin gari." Na ce masha Allah kaji daɗinka. Ni kam bani da yaya hasalima ni ce 'yar fari sai ƙanena uku Jamila da Jafar da kuma Habu,sai wanda za a haifa mana yanzu. Yace "Allah ya sauke ta lafiya dama ina ganin Abba na raya a zuciyata cewa ƙila ke 'yar fari ce." na ce Ameen, gani ka yi ba tsoho ba ko? Na tambaye shi ina 'yar dariya. Yace "E mana." Shima cikin dariya ya amsa. Nace, haka in 'yan makarantarmu suka zo sai su ce wai Ummanmu Antinmu ce. Muka ƙara yin dariya tare. Ya ce "To Ni dai bari in zo in tafi kar dare ya yi sosai,na kalli kekensa nace danma kana da abin hawanka balle ma ka ce zaka rasa ɗansahu. Yace haka ne." Nace, Ka gaida Hajiya da kyau. Ya faɗaɗa fara'a "Zan faɗa mata Insha Allahu." Shine ya nannaɗe tabarmar ya tako har bakin soro yana faɗin in gaida su Umma.
🖊️🖊️🖊️
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko Katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Free Page 2*
Har tsakiyar dare bacci ya ƙi zuwa min sai juyi na ke akan "yar katifarmu Jamila ta na ta baccin ta, tufka na ke ina warwara abu biyu ke ɗaga min hankali,menene dalilin rabuwa da matansa? Kuma komai nasa dole sai Hajiya ta sani? Zuwa yanzu nasan cewa Hajiya dai ba matarsa ba ce, ko dai mahaifiyarsa ko kuma uwar ɗakinsa. Da safe ina raba mana abin kari awara ce da koko duk muna tsakar gida harda Abbanmu. Umma ta dube ni,"Ke kuma lafiya duk jikin ki a sanyaye?" Nace, lafiya lau, kawai yau kasala nake ji. Ta dubi, Abbanmu tace, "Abban Baby kace ka yaba da saurayin nata jiya?" Ya ce gaskiya Salamatu na yaba sosai, in har sun dai-daita zanyi farin ciki domin alamu sun nuna shi mai hankali ne.Umma ta ce "To ɗan unguwar nan ne?" Yace, A a yace min shi ɗan Gama ne can aka haifeshi amma yanzu suna nan haka ko gurin Janbulo ne, ya ce da ɗan gidan sa a gurin da ya gina suna zaune da mahaifiyar sa. Kuma yace a kwari yake tsaron shagon wani mai gidansa, amma yace asali su 'yan Gaya ne. Umma ta ce "To, Allah ya daidaita su.
Ni dai bance komai ba,mutumin ya maƙale a zuciyata duk yadda na auno matsaloli sai zuciyata ta kawo wani uzri ta wanke shi. Haka nan har naje makaranta na dawo ina tunanin Aliyu Shamaki.
Da dare muna 'yar hira da Umma, ta tambaye ni da cewa "Ni ko Baby mutumin nan ya yi miki kina ganin cewa zaki iya aurenshi?" Na ce to Amma Ni dai ina ta waswasi. "Game da me?" Ta katse ni da tambaya. Na ce aurensa uku duk sun rabu da matan, 'yayansa uku duka mata kuma duka sunan mahaifiyarsa ya saka, sai ina jin tsoro ko mahaifiyarsa ce bata barin matan. Umma tace "Karki fara lamarinki da zargi, tabbas dole ki damu game da rabuwa da matansa, shawarar da zan baki shine ki sa hankalin ki sosai ki gano raunisa da fushin sa, ta haka zaki iya samun zaman lafiya da shi. Baby a irin tarbiyyar da nake baku ina sa rai ko mutum yana fidda wuta ta baki dan bala'i za ki iya zama dashi, haka duk wata kissa ko kisisina, ko shirka bai kamata kiji ɗarba." Na yi 'yar dariya haka ne Umma.
wayar Umma ta yi ringin Jamila tace Yaya Baby lambar jiya ce da kika ajiye. Gabana ya faɗi harda juyawar ciki,take naji banɗaki kawai na ke son shiga. Na amshi wayar na shige ɗakin Umma ina jinshi yana sallama, sai da na zauna sannan na amsa sallamar da wata murya da bansan ina da itaba. Na gaida shi,ya amsa na tambayi Hajiya da yara,yace duk suna lafiya. Yace, "Shine ko ki kira ni kiji ya naje gida jiya." Na ce to kayi haƙuri amma gaskiya na so in kira ka sai kuma na yi tunanin kar kana kan Kekenka kuma in tsaida kai, har kuma bacci ya ɗauke ni. Ya numfasa "To na amshi uzrin ki, amma ya kike gani zuwa yanzu a zuciyarki ta kuwa fara sona?" Na kwanta tare da ƙara manna wayar a kunnena. Ba zan iya tabbatar da haha ba Yaya,sai dai ka faɗamin yaya son ya ke ko zan gane.
Ya yi yar dariya. "Bani labarin bayan rabuwa kin tuna da ni? Sau nawa? Kina tuna hirar mu? Wacce a ciki?" Na numfasa, gaskiya na tuna ka sosai amma ban lissafa dadin ba. A hirar mu dai nafi tuna batun auren ka guda uku,sai in ji fargaba. Yace, "Alhamdulillah Baby kin fara so na, karki damu da maganar matan da na rabu da su, ko tunanin dalilin rayuwar mu, zai fi kyau ki maida hankalin ki akan irin rayuwar auren da za mu yi. Zanzo gobe,ki tanadi labari mai daɗi da za ki bani." Nace,to Insha Allahu Allah ya taimaka a gaida Hajiya. "Zan faɗa mata." "Yaran ki fa?" Cikin sauri na ce agaida min su don Allah, koda bansan sunayen su ba. Ya ce "Haka ne ban faɗa miki ba, dukansu sunansu Zeena." Kamar yaya na tambaye shi cikin rashin fahimta. Yace Ƙwarai kuwa duk sunan Hajiya suka ci, amma kowace da laƙaninta Babbar Meema, mai binmata Mubina sai ƙaramar su Anisa." Na sauke ajiyar zuciya, gaskiya abin ya birge ni kuma har naji ina son in gansu. "Karki damu ke da 'ya'yanki kuma ke ma zaki haifa mana wata Zeena ɗin ko?" Kunya ta sa na yi saurin faɗin sai da safe, na kashe wayar sannan na yi rigingine a gadon ina jin farin ciki gami da fargaba. Dole in yi magana da Umma.
Kamar kullum ya zauna a gefe yana jan carbi yana jiran Hajiya ta gama addu'o'inta kafin ya gaida ita kuma su yi 'yar hirar da suka saba. Bayan ta kammala suka shafa tare, ya matsa gabanta sosai ya rusuna ya gaishe ta. Ta amsa tare da kai hannu ta shafa masa kai tana faɗin "Allah ya albarkaci rayuwarka, da ta 'ya'yanka, ya yi albarka a cikin neman ka, ya albarkaci abinda zaka samu. Allah ya tsare ka daga dukkan sharri mutum ko Aljan da duk wani abinƙi." Shi kuwa yana ta maimaita ameen. Bayan sun kammala sai ta gyara zama sannan ta ce, "Jiya Maman sani ta zo game da maganar abincin sadaka na ranar juma 'a wasu abubuwa sun ƙare, na ce ta lissafi kamar yadda aka saba, kuma ina son wannan karon za'a saka sunan mutum ɗari a kayan salla yara marayu, sai mu ba Zeena Foundation dama su nemo yaran da suke dace da buƙatar tallafin nan a ba su. sannan ɓangare kayan ɗaki Amina ta. Kawo sunan mutum biyu kuma sun gama bincike tabbas yaran mabuƙata ne duk marayu ne na ce taje gandu su yi magana a Zeena funitures da manajan kamar dai kowane lokaci. Ya ƙara yin ƙasa da kai cikin girmamawa to Hajiya duk yadda ki kayi dai-dai ne. Ta dubi fuskar shi, "Baka sanar da ni ko ka tattauna da yarinyar nan ba." Eh na samu ganin mahaifinta kamar yadda ki ka bani shawara, kuma ya min 'yan tambayoyi kafin daga bisani ya shiga ya turota. "Kamar wace tambaya ya yi maka?" E ya tambayi unguwarmu sannan ya tambaye ni game da addini da sana'a da aƙida. Ya gamsu duk da ce masa da na yi ni yaron shago ne, yace buƙatar kawai ace da sana'ar komi ƙanƙatar ta Allah shine mai buɗawa in yi magana da ita in har mun sasanta ya bani ita. Hajiya ta ɗan yi jim,sannan ta ce, "Mecece hikimarka ta ɓoye matsayinka? Ya gyara zama, Hajiya ina son in samu soyayya ta tsakani da Allah bata abin hannu na ba, ina son in shimfiɗa sabuwar rayuwa ba irin ta baya ba." Ta yi ɗan murmushi cikin ƙasaita ta ce "Wannan yaro na ne, tabbas akwai hikima cikin abinda za ka yi. Na amince da haka, to ita yarinyar ta karɓe ka ya kuka yi?". Ya sunkuyar da kai,to har yanzu dai ban same ta sosai ba, na yi mata uzri yarinya ce sosai yanzu ne zata gama Sakandire su za suyi sauka a Islamiyyar su, haka nan kuma ni ne saurayin ta na farko. To ta kasa gane ko tana sona. Hajiya ta yi hiru cikin nazari, sannan ta ce Allah ya zaɓa mana abinda yafi zama alkhairi, za mu ci gaba da addu'a." Ya ce Ameen ina godiya sosai. Haka suka kasance cikin tattaunawa har zuwa lokacin da Juma ta shigo ta na jera flas na ƙosai da hankali da wainar ƙwai da na ruwan zafi ga kunun gyaɗa ga kuma kayan shayi. Shamaki da kansa ya Haɗawa Hajiya Shayi mai kauri kamar yadda ta buƙata, ya shirya mata komai sannan ya saka abinda kanshi ke so ya shiga ci suna ƙara tattaunawa.
🖊️🖊️🖊️
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu 600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko Katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*
Mamakin kansa ya ke yadda ya ƙosa dare ya yi yawan murmushin da ya ke in ya yi shiru ya sa yaran kantin suka soma tsegumin cewa maigida ya faɗa soyayya, musun da suka yi ya sa ɗaya daga cikin yaran mai suna Ɗahiru ya ce bari ya gwada shi. inhar haka ne zai gane. Ya kunna waƙar Hamisu Breaker ta soyayya. Yaje ya zauna a bakin Office ɗin yana ci gaba da shi'anin gaban sa. Daga ciki kuwa Shamaki ya yi tsam da ransa yana sauraron yadda mawaƙin ke yin falsafa akan so, sai kawai ya ƙwala wa Ɗahiru kira, ya amsa ya shigo cikin girmamawa yace "Gani Alhaji." Wai ku bakwa rabo da jin wakane duk da ita wannan naji ta yi daɗi da ma 'ana, amma waye ya yi ta ne, tura min ita a waccan wayar in yi wani nazari a kanta. Ya ɗauki wayar ya fita yaje yana basu labari suna dariya. Ranar haka ya yini jin waƙar. Da yamma ya kira Malam Bala direbansa ya ce a wanke mota zai fita bayan Isha'i. ya kuma fara lissafin zai bi ta Zeena Store ya kwashi alawoyi yaje Zeena Factory ya haɗa mata kayan ƙwalam na Snacks. Kamanta gurin wa zaka kuma wane matsayin kake a idon ta? Zuciyarsa ta jeho masa tambaya. ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya ce sai dai in nemi ɗata ko yalo? Ɗan tsaki ya saki sannan ya yi maganar da ƙarfi Ayaba da Lemo zan siya. Hassan dake cikin Office ɗin yana rubuta wani rasit ya ce "Karɓo wa za ayi Alhaji?" Ya dubi Hassan me nace? Yace,"Naji kana maganar Ayaba da Lemo." Ya yi ɗan tsaki eh da za a karɓo ne amma bari sai na fita sai in siya kawai.
Nikam kafin Isha'i na shirya tsaf, ba sallah zan yi ba don haka na kame ina jiran zuwansa, gabana kuwa sai faɗuwa yake ina ayyana yadda zanji idan mun kasance muna hira,ina ta baiwa kaina shawarar ya kamata ace ina zaɓo kalamai inzan furta masa,sannan kuma kar inyi masa magana da irin muryar da nake yi wa kowa hakan zai sa in ƙara birge shi. Take na gamsu da hakan,kuma na yarda shi na musamman ne.
Shamaki ya wahala kafin ya samu kayan da za su nuna shi a talaka,suma dai yadine fari mara nauyi, yanada mugun tsada amma ba kowa zai iya gane hakan ba sai wanda ya san kaya. Ya zube wayoyinsa guda huɗu a kan gadonsa, sannan ya saka mai boturan wadda ya sawa sabon layi domin ita kaɗai a alajihu agogo da zobe na azurfa duk ya zube su. Ya nufi sashen Hajiya.
Ta ƙare masa kallo sanna ta amsa gaisuwarsa. Ya ce zanje gurin Rabi a ne kamar yadda na sanar da ke tun shekaran Jiya. Ta ce "Na fahimta,kaje Allah ya bada nasara,kuma ka ce ina gaisheta. Sannan ka tabbata ka sami zuciyarta a yau,domin na lura kana matuƙar sonta. Allah ya yi muku albarka gabaɗayan ku." Ya ce Ameen sannan ya miƙe ya fice da sauri. Ta bishi da kallo a fili ta furta akwai matsala ya kamu da yawa, ni da nafi son ya samo wadda ta fi son sa dole inyi wani abu.
Ya dubi Malam Bala yace, in ka isa gurin masu Lemo na ɓawo za ka karɓo. Da suka isa ya rasa na nawa ya kamata ya siya yace Malam Bala ga dubu biyar su yi kashi biyu. Da aka kawo ya ga da yawa yace Malam Bala ka dauki kashi ɗaya. Sai da suka gota lungun sannan ya sauka,yace ka je zan kira ka nan da awa biyu. Ya taka da ledoji biyu a hannunsa ya dawo ya shiga lungu.
Jafar ya shigo da ledoji suna rinjayarsa, yace Umma wai gashi inji wani mutum wai yace Yaya Baby taje. Cikina ya juya da sauri na ɗauki buta zan shiga banɗaki, Umma ta ce "Ke dakata lafiyarki da tun ɗazu kuna zaune sai da yazo zaki tarki shiga banɗaki?" Nace wallahi Jafar yana faɗa sai naji cikina ya juya, na shige da sauri. Ina jiyo Jamila tana tsaki tana mitar "Yanzu da wari zaki gunsa?" Na fito na sake shafa turare sannan na fita na samu har Jamila ta shinfiɗa masa tabarma ta aje masa ruwan fiyawata.
Cikin girmamawa na gaida shi, na kuma tambayi Hajiya da yara. Yace tana gaida ni kuma duk suna lafiya. Nace shine harda wata ɗawainiya haka? Ni fa karka matsawa kanka a irin wannan yanayin ba sai ka min wata ɗawainiya ba. Ya ce "Karki damu, ina da halin yin hakan ne, yanzu ki bani labarin soyayyata. Na ƙosa mu soma musayar ta ni da ke, domin har na soma zama wawa ina kasa jurewa tunaninki." Nace koda bansan so ba, na tantance kai na musamman ne, duk wani kai kawo nawa kana zuciyata kuma na kasa gano aibunka, zuciyata tana faɗa min cewa in maka uzri kuma in amince ka zama mijina. Na gamsu sosai da shawarar zuciyata kuma na amince ka zama mijina in ina gidanka sai ka koya min soyayyarka. Na kai ƙarshen maganar tare da rufe ido. Ya ce "Alhamdulillah wannan yanayin da ki ke ji shima alamun so ne Baby, yanzu sai mu yi maganar aure, zuwa wane lokacin ya kamata mu zama miji da mata?" Nace ai wanna da su Abba zaku yi magana. Ya numfasa "An saka ranar da zakuyi walimar sauka?" Nace har an fitar da katin manyan baƙi an raba tun wancan satin. Na mu sai wannan satin insha