Showing 21001 words to 24000 words out of 76857 words
ko faɗa mana magana ni da matata..,
kuka ta saka tace '' dan Allah kai hakuri bana so wallahi ba kyau jadda ma yace duk me yi Ubangiji yana fushi dashi haka ma aka faɗa mana a islamiyyar mu...,
wani kallo ya jefe ta dashi, yace '' au Allah..?, mai maita abin da kika ji jawaher ta ce..,
da sauri ta zaro ido tace '' wallahi ba zan iya ba.,
au kina so kenan muyi ya fadi haka yana tsare ta da idanuwan'sa
zama tayi tana kuka tace '' a'a dan Allah kar kayi... cewa tayi kirjinta na ciwo saboda rashin ka..,
da sauri ya kalle ta yace '' haka kika ji..?
hawaye ta share ta daga mai kai
rigar'sa ya fara ƙoƙarin cirewa da sauri ta zunduma ihu tace '' wallahi haka naji tace..,
OKAY tashi ki fita..
tashi tayi da sauri tana kuka nufi kofar bude wa tayi ta fita tana ci gaba da kuka ta rasa wannan wacce irin rayuwa ce ta shigo ta , tana neman rasa mutuncin ga aljanin dare da jiya, ya azabtar da ita a parlour ta zauna tana share hawayen ta.
tashi tayi ta shiga daki kulle dakin'ta tayi ta kwanta bata ƙara sauraran girki ba ,
bata farka ba sai karfe biyu shima bugun da yake mata shi ya farkar da ita da sauri ta tashi tana mustsuka idanuwan'ta saka hijabinta tayi ta wanke fuskar'ta ta buɗe kofa ta ɗan leƙo kan'ta ganin sa da manyan kaya tamkar wani shehun malami sai abin ya bata dariya yawa ni haɗe girar sama data ƙasa ita kuma aunty JAWAHEER irin kaddarar ta kenan ko da yake ai taga baya mata masifa ba zato taji yace '' idan kin gama kallona sai ki fito..,
sosa ƙeya tayi ta turo baki gaba tace '' to ina kai ne ka hana ni fitowa ka tare kofar..,
okay ni na hana ni fitowa ko..?
ganin yana ƙoƙarin shigowa da sauri tace '' a'a bara na fito to matsa..,
yace za ki iya buge ni ki wuce..,
ƙasa tayi Da kanta zuciyar'ta na tsananin bugu.
turo dan ƙaramin bakin ta tayi tace '' kayi hakuri ka matsa min ni ba zan iya buge ka ba..,
matsa mata yayi tana fitowa daga corridor din dakin ta tayi turus ganin naki mace da mijin ta sai yar su.
kallon sa tayi tace '' yaya baki kayi ne..?,
JAWAD yace '' a'a ban sani ba...,
hmmm kawai tace ta ƙarasa sallama tayi da sauri suka juyo tare da amsa mata sallamar'ta durkusawa tayi ta gaisheni su, suka amsa cikin sakin fuska matar tace '' a'a tashi kanwata wallahi san tana kama da kai wannan ita ce copy dinka a komai bata barka ba wallahi Masha Allah kamar kai kaki ka zubar..,
a zuciyar NAJLAH tace '' to dan muna kama ai ba halin mu ɗaya ba..,
Hisham yace '' wallahi kuwa koni farkon gani na da ita da nayi dana je YOLA wallahi naga kamar su.,
tashi tayi ta shiga kitchen ta barsu suna hirar su.
ɗaukan tray tayi ta zuba snack sai lemo ya ajiye musu komawa tayi ta ƙarasa farfesun da take ta yi diban nata tayi takai musu godiya sukai mata matar tace '' sannu mun saka k hidima..,
Murmushi kawai NAJLAH tayi JAWAD kuwa tamkar baya gurin yana ta danna wayar sa yarinyar nan na kan cinyar sa Hisham ne yace '' wai ina Madam take ne..?,
JAWAD yace '' tayi tafiya ne..,
dariya yayi yace '' Allah ya dawo da ita lafiya idan kunyi waya ka faɗa mata mun zo yi mata ta ya jiki kenan kafar tata har ta samu sauki..?,
Eh wallahi NAJLAH barin wajen tayi tana taɓe baki shiga toilet tayi ta yi wanka ta chanza pad.
fitowa tayi daure da toilet tana tsane kan'ta ya shigo da sauri ta saka hijabinta yace '' ke wai baki iya tarbar baki bane kin tafi kin barsu..?,
Ƙasa tayi da idon ta , tace '' gani nayi ba gurina suka zo ba, kayi hakuri bara nayi saka kaya sai naje..,
kafe ta yayi da idanuwan'sa yana jefan ta da wani irin kallo ja da baya tayi ganin irin kallon da yake mata ta turo bakin ta ranta duk ba dad'i ta ita bata san wannan kallon wallahi..
matsuwa kusa da ita yayi yace '' ni kike wa kananun magana ko..?,
da sauri ta girgiza kan'ta tace '' wallahi ba abin da nace yaya kai hakuri..,
ta fadi haka a tsora ce domin tsoran yaya JAWAD ya ƙara shigar ta, ga halin muguntar sa ga wannan kuma sabon halin nasa ko lokacin da take gida idan yaje irin wannan kallon yake jifan ta dashi, ta rasa dalilin sa na yin haka ko su basma baya musu haka ita din ce dai
katsai mata tunani yayi da cewa kefa nake jira kin tsaya tunanin da ba zai amfanar dake komai ba
Ya Allah yaya JAWAD yawa me gani har hanji haka ta raya a zuciyar ta afili kuma sai tace '' to ka fita zan saka kayana...,
wani kallo yayi mata yace '' ba zan fita ba zo ki fitar dani idan har kin matsu na fita..,
da sauri ta kalle sa tace '' yaya kaya fa zan saka ..,
wani kallo ya jefe ta dashi da sauri ta hadiye sauran zancen ta tana ci gaba da ja baya so taka ta yi wuf ta shiga toilet idan ya gaji ya fita sai kace wata yar iska zata saka kaya a gaban sa idan shi yana ganin ba wani abu bane to ai ita tana da kunya...
****
ɗaukan kayan ta tayi ,
ta shiga toilet da gudu tana dariya shima abin dariya ya bashi ganin yadda ta faki numfashin'sa ta dauki kayan ta, ta shiga toilet saka kayanta tayi ta fito tana rara gefe.
haɗe rai yayi yace '' zo ki wuce tun da kin riga kin aikata a bin da kikai niya..,
bata ce komai ba, ta fita. bin ta yayi a baya har suka isa da sauri mubeena ta miko mata hannu amsar ta tayi tana cewa aunty ya sunan ta..
ai nayi fushi bakya so muyi zuminci ko tambaya ta sunana baki yi ba ,balle akai ga exchange number.
zama tayi tace '' kaina bisa wuya na kiyi hakuri yanzu dai fara faɗa min sunan yar tawa..,
Matar Hisham tace '' mubeena..,
Murmushi NAJLAH tayi tace ''
Masha Allah, Allah ya yara mana ita..to aunty ya sunan ki..?,
safeera..
Masha Allah ni kuma NAJLAH.
ta faɗa tana jan kumatun ta
tashi tayi ta shiga daki dauko wayar ta tayi ta buɗe wardrobe din ta shopping da abba yayi mata da zata tawo ta buɗe ta dauko turarurruka guda uku sai turaren kabbasa da aunty rafi'at ta bata da yake tana aure a Maiduguri to shi ne ta fara sana'ar saida turare ta zuba a wata jaka me kyau ta fito miƙa mata waya tayi tace '' ungo saka min number ki..,
amsar wayar tayi ta saka mata tayi Flashing itama ta , yi saving number ta.
ta miƙo mata amsa tayi safeera tace '' da wannan number kike chatting..,
Najlah ta ɗan saci kallon Jawad sai kuma akai Sa'a shima, ya ɗago kai fa sauri ta dauke kan'ta tace '' eh da ita nake yi..,
okay idan naje gida nayi miki magana ma dinga gaisawa tanan yanzu zumincin yanzu sai ta media amma dai zaki zo ki wunar min ko..?,
Najlah tace '' idan yaya ya barni zan je mana...,
Hisham yace '' hmmm wannan uban yan kullan tab..,
JAWAD yace '' maman mubeena har na kai shi..,
taɓe baki tayi tace '' ai duk halin ku ɗaya yar unguwar nan sai a sawa mutum ta kum kumin fita..,
Hisham yace '' ki faɗi gaskiya yafi ni ko zuwan mu gidan nan nawa zuwan jawaher nawa..?,
dariya tayi tace '' ai SAN ya fika ka iya kulle wallahi..,
kallon agogo yayi yace '' to hirar ta isa haka lokacin sallah yayi tashi mu je muyi sallah..,
cewar JAWAD.
tashi Hisham yayi suka fita dariya Hisham ya fara haɗe rai jawad yayi yace '' kai lafiyar ka qalau kuwa..?,
wallahi ina dariyar yadda akai kake tsoran wannan dan ƙara min abin nifa wallahi dani ne da tunani anyi an gama sai dai ta fashe kowa yaji warin ta ko kuma babbar hanya kake tsoro ne ban sani ba..,
uban babban hanya nake tsoro kawai dai akwai abin da nake jira ne is very young.
dariya Hisham yayi yace '' hmmm young fa, ai irin haka yafi dad'i kai zakai saitin ka yadda kake so saitin ya tafi.,
JAWAD yace '' hmmm kai dai wallahi Allah ya shirye ka muna ƙoƙarin sallah kana wannan zance..,
dariya Hisham yayi bece komai ba, alwala suka yi sannan suka tafi masallaci.
Cikin gida kuwa safeera ce ta tashi a tayi Sallah sannan ta dawo jan NAJLAH take yi da hira , dan sakin jiki tayi da ita saboda tana son yara ɗazu ma ganin JAWAD ya dauke ta , hakan ya saka bata kula ta ba gudun kar kuma wani abu ya biyo baya yazo yana mata ba dad'i.
jin sallamar su, suka yi amsawa safeera tayi Hisham yace '' to uwar surutu taso mu tafi Najlah ta , takura miki da zance ko..?,
girgiza kai tayi tace '' a'a naji daɗin zuwan ku ina zaune ni kaɗai ba , abokin hira..,
Kallon ta JAWAD yayi ya cije lips din'sa yace '' daga dawowa sai kace tafiya ai na zata sai dare..?,
a'a wallahi yanzu zamu tafi idan ka matsi da ganin mu, to ka biyo mu ka ramawa kura aniyar ta daman ka ajiye yarinya ba wani me debe mata kewa wallahi JAWAD hmmmm.
haɗe rai yayi salon Ya saka Najlah ta raina shi ya dauki mubeena da take wasa a cinyar Najlah dariya yarinyar ta shiga yi mai yana mata wasa.
tashi safeera tayi tace '' to auntyn mu sai na ganki a gidana sauran kuma SAN ka hana ta zuwa..,
murmushi yayi yace '' sai JAWAHEER ta dawo ma zo mu wunar muku..tun karfe 6 na safe za mu zo sauran kuma kuce yayi wuri..,
Kamar gaske Allah ya kai mu Lokacin
Cewar safeera
Amin ya Allah cewar Hisham da JAWAD
NAJLAH dauko jakar nan tayi ta miƙa mata amsa tayi tana mata godiya shima HISHAM yayi mata godiya tare da cewa JAWAD ka taya mu godiya
JAWAD yace '' to kudi ya dauko ya bawa mubeena suka ƙi amsa amma yace shi ba su ya bawa ba yarsa ya bawa.
Ba yadda suka iya ya daure su da jijiyoyin jikin su suka amshi kudi tare da yin godiya.
har wajen motar su suka raka su sannan suka juyo suna shiga Jawad ya rufe kofar parlour da sauri Najlah ta kalle sa wani kallo yayi mata yace ''hmmm wana kama wato ko a gida ma haka zaki ce na barki ke kadai ko ba abokin hira kin ce min kina son yin hira ne..?, wallahi Najlah ki kiyaye randa zan riƙe ki a hannuna zaki yi bayani ne abu ɗaya ne ya cece ki gift din da kika basu da yau hmmm kin fahimci wane ni..
ajiyar zuciya ta sauke ganin ta kubuta..
juyawa tayi ta kwashe kayan da, ta kawo wa su safeera takai kitchen ta dawo juyowa tayi taga still yana gurin nan a tsaye tamkar wani wanda ya haɗiyi sanda taɓe baki tayi ta juya ta shiga daki ta rufo.
tabar sa a tsaye yana tubka da war wara maganar da suka yi da Hisham ita ke tunowa yana nazari akan ta.
yana kuma hango wutar da take gaban sa a hankali ya furta ummi dafa kan'sa yayi yana rokon Ubangiji ya ganar da ita gaskiya kafin lokaci ya kure mata , besan wannan wacce irin tsana bace haka.
ajiyar zuciya ya sauke ya hau saman sa.
****************************
YOLA.
UNGUWAR DOUGIREI
ƊAN BUZU ESTATE.
Kyakkyawar tsohuwa ce zaune akan carpet gaban ta kayan ciye ciye ne kala kala duk da tsohuwa ce hakan be hana a gane ita din buzuwa bace ta usul gefen ta wasu yan mata ne zaune suna duba atamfofi ko wacce na fadar ra'ayin ta.
da alama jikokin tane dan ba'a ce ya'yan taba gefe bangon da yake kallon dining room katon photo JAWAD tare da wani farin tsohu ya rungume shi JAWAD da kayan lauya a jikin sa hannun sa rike da wata farar takarda kallo ɗaya zakai mai ka fahimci su dukan su, suna cikin zallar farin ciki anyi wa frame din ado da ruwan gold hakan ya kara kawata farin painting hannun dama kuma na cikin dining room din katon picture JAWAD ne da wannan tsohuwar sai tsohon nan ya ja mai kunne da ga gani shidin dan gaban goshi ne.
kallo ɗaya zakai wa hamshakin parlour kasan cewa ita din tsohuwar gata ce.
da tagaji da wanna uban musun da suke yi tace '' ku dai Allah yayi muku ruwan ido wallahi ni ina tsohuwa ma bana wannan abu da ni nake yi cewa za kuyi rikicin tsofa ne kunga waccan zata yi muku kyau ne adon blue blue din nan ba fari ba baki duk za tayi wa mutum kyau tun da wannan anko din ba iya gidan nan za a yi ba Aliyu ma yace ku yi maza ku zaɓa wanna sample ne sai ayi ta da yawa rabawa yan uwa da abokanan arziki...,
wata ce a cikin su ta daga wacce anni ke nuna musu tace '' ANNI amma ba zai saka a rubuta sunan ba ko..?,
ANNI tace '' basma ina zan sani..,
Gaskiya ANNI kice kar ya saka mana suna wallahi mu mun fi son ta a haka kuma ALLAH kin fadi gaskiya wannan ba wanda ba zata yi wa kyau ba
Cewar unaisa
hmmm Allah ya kyauta wannan kuma shi ya sani.
Dan Allah Anni Ki kira shi kice kar a saka suna.
wallahi ba da waya ta ba wato nice marainiyar wayon ku ko da JAWAD ne kuce ya fiye daure fuska shima Aliyu daure fuska yake yi ashe abin naku rainin hankali ne wallahi muhibba ku fita daga cikin idona na rufe.
tashi basma tayi tace '' ai dadin ta ma muna da wayar da sai ki kumburan zuciya da wannan maganar taki..,
Uhmmm wallahi bara Sharif yazo yayi min tsakani da ku ko da yake Allah ya kawo yaron kirki JAWAD wallahi shine maganin ku shima sharif din ai kun raina shi bakwa kallon sa da gashi..
dariya dukkan su, suka saka suna sai Anni
hade rai tayi ta soma lalubo number JAWAD da sauri muhibba ta karbi wayar tana cewa dan Allah anni kiyi hakuri, karki kunto mana kura da tsakar rana Allah sarki sister tana can tana fama.
basma tace '' wallahi kuwa tana can..,
ANNI tace '' hmm waya faɗa muku zai mata wani abu wallahi NAJLAH yar gata ce a gurin Jawad kuma za ku gani..tun tana yarinya yake dawainiya da ita yake nuna mata kulawa...,
ANNI har yakai ya MUNEEF da ma baya son ɓacin rainta..?
Cewar ramlat
Dariya ANNI t@yi tace '' yaro man kaza ko wanne allazi da nashi amanu kunga shiga ta daki ba za a yi wannan musun da ni ba... bani waya ta...,
Mika mata tayi suka bita da kallo suna mamakin abin da ANNI tace sai kuma suna ci gaba da sabgar su cikin nutsuwa.
**********************
TARABA STATE JALINGO
POV UMMIN JAWAD
wallahi Ummi idan baki tashi tsaye akan yaya ba za su saka ma gaba ki ɗaya yace bake kika haife shi ba ga har muka tafi be fito da waccan shegiyar ba.
balle ya biyo mu ya bami hakuri
kar kaɗa ƙafa ta shiga yi ranta duk a ɓace ta buɗa baki za tayi magana taji sallamar SAMHA da sauri ya juyo ita da ALTAB ne yana riƙe da kayan ta a cikin. Lugaggage ga jakar ta ya riƙe ta a hannun sa yawa wani yaron ta, ga wata kwandaleliyar sarka a wuyan sa da wani three-quarter wando jikin sa duk sarka daga shi har ita ba , wanda ya cire takalmin sa haka suka shigo cikin parlour.
sakar baki tayi tana mamakin rashin kunyar ALTAB Allah me iko.
zama SAMHA tayi tace "' sannun ku..,"
ta faɗa tana dauke kai haɗi da sakin kwai tana latsa wayar ta shi kuwa zakara sarkin neman suna hana rike da jakar ta ya saba ta a hammata yace '' ahhh ummi baki ji tana gaishe da ke ba..,
tabbas idan ba tayi da gaske ba bakin cikin JAWAD ALTAB yana neman kashe ta kwanan ta be ƙare ba su biyu ne mazan ta kamata yayi ace taji dad'in su, sun faranta mata sun mai da ita yar gata abin kwatance amma gashi nan suna neman halaka ta kwanan ta be ƙare ba me ake da auran yar tasha duk da shima ɗan nata dan tasha ne amma da ace ya samu matar arziki ai da sai ta shi za tayi cikin kunar rai ummi tace '' ALTAB ka fita daga kai har sharar matar ka bana kaunar ganin ku..,
wani kallo SAMHA tayi mata sai kuma taja kwafa ta tashi tsaye tace '' wallahi ni kabewar ƙabari ce baƙin cikin me taushe ni da kalin majina ce dole idan aka hau ni a zame..,
amma wallahi yaya sam halin ka be yi ba kana gani take faɗawa mahaifiyar mu bakaken maganganu..?
Ke saurara min tun da nazo gurin nan ban saka dake ba , balle ki dauki kaso kuma sannan kina ina Lokacin da momcy ta zo gidan nan taci mata mutunci amma duk da haka ina kallon ta a matsayin UWA wannan faɗan su, su ta shafa ba mu ba ko ba haka ba HONEY 🍯..?
ta ƙarshe maganar tana yi wa ALTAB wani irin kallo irin na gogaggun yan bariki..
Altab da ta kusan kunce mai kai yace '' kyale ta so take nayi kasa kasa da ita zo mu fita idan ta wuce ma dawo ke AFNAN ki dinga tofa mata FALA'I DA NASI three three a ruwa tana sha sai Ayatul-kusiyyu maganin sheɗanu domin daga gani ummi ta samu shafar aljannuuuu...,
jiri ne ya fara ɗiban ta ta dafa bango da kujera zuciyar ta na tsananin bugu ita yau dan da ta haifa yake faɗawa tana da aljanu aga ban matar sa tabbas ba tayi lalacewar da haka zata faru a kan'ta ba wallahi sai ta nunawa SAMHA din mahaifiyar ALTAB
27, July 2025
Maryama
Dan Allah oum yasmeen nayi nayi ya shiga rin na karanta yaki Yi sai book 1 yake ta nuna min