Showing 6001 words to 9000 words out of 21624 words
yayi wanka sosai yake zabga kamshi saboda irin sabulan da yayi amfani da su towel ya daura ya fito T-shirt yasa yar gidan puma blue black inda ya sanya wando equarter turaran al rayyan yasa sai ya haɗu da turaran wankan sa yake bada wani kamshi agogo rolex ya daura ya dauki wayoyin sa slippers yasa dayake ƙafar shi ya sa safa saboda sanyin da ake ya fito ko briefcase ɗin sa be biya ta kai ba ya nufi wata siririyar ƙofa da alama wani gun zashi abin mamaki wani tamƙameman floor ya shiga sallama yayi ciki ciki da sauri yan matan biyu da na miji daya suka ɗago cikin farin cikin dawowar yayan nasu suka amsa da sannu da zuwa yaya
"amsa musu yayi cikin deep voice ɗinsa yace
'Ina hajiyar mu take ?"
Basma ce tace
tana bed room ɗinta
"Okay kai musu'af baka koma makaranta ba zaman me kake ?"
Cikin rashin gaskiya da kame kame yace
Big brother yau mun dan sami hutu ne sai wani satin zan koma
"okay a kula kuma bana son inji wata magana ta biyo baya ,
Insha Allah yaya ba abin da zaka ji
"huce wa yayi wani ɗaki wata mata ce ta juya baya tana karatun qur'ani wasu haɗadɗun luxury funiture masu kyau da tsaruwa kallo daya zakai wa ɗakin kasan an kashe dukiya sallama yayi ga nin tana karatu yasa ya sami arm chair ɗin dake bedroom ɗin ta ya zauna ganin ta kusan idar da karatun ya sauko ƙasa wani haɗadɗan carpect ne mai taushi ash color da ratsin black color anyi flower da silver color ya tanƙwashe ƙafar shi tamƙar malami da ɗalibin shi ganin zata shafa yasa shima ya ɗaga hannu sa sukai addu'ar tare juyowa tayi farace tas kallo ɗaya zakai mata kasan buxuwa ce hutu da jin daɗi ya zauna mata
"hajiyar mu barka da dare da fatan na same ko lafiya ,
cikin kulawa da soyayyar ɗan nata tace
Lafiya qalau giwa ya aiki
"Alhmdllh hajiyar mu ,
Masha Allah giwa a yanzu bani da buri da ya huce in ganka kayi aure ka duba fa ka gani December ɗin nan da zamu shiga watan farko za akai kayan su mansur duk ƙannan ka sunyi aure dan Allah giwa ka nutsu ina so inga ƴa ƴan ka
"sosa kai ya shi ga yi cikin burin kunya yace ,
Insha Allah na kusan kawo miki budurwata kar ki damu
Buɗa baki tayi zayi magana yayi sauri yace
"addu'a kawe zaki ciga ba dayi ,
dungure mai kai tayi tace
Wallahi duk uncle bature ne yake daure maka in akai magana yace aure lokacine giwa ko dan lalurar ka kai aure
"dariya yayi in yana gaban daddy da hajiyar mu ji yake ba shi da wata damuwa ya koma kamar yaro yace,
"To, zanyi first love,
jin muryar husna ta ce
Hajiyar mu mun kammala abincin
"To, husna gamu nan zuwa ,
Kai ya lamgwaɓa yace
Hajiyar mu yau ta fitinan niyar yarinya na haɗu da ta duk ta gajiyar da ni
Juyo watayi ta fasa cire hijabin ta wannan shine karon farko da taji yayi mata zancan mace a rayuwar sa cikin salon jan yaro a jiki ta ce
"me ya haɗa ku my son ?"
hmm first love Allah shagwaɓabɓiya ce da ga nayi mata magana sai ta fara kuka
topa ita da haka za ai auran
Zaro ido yayi yace
Hajiyar mu bafa budurwata ba ce ɗaliibaaata ce ……………✍🏼
*RASHIN SANI*
By
Oum Yasmeen
Chapter 31-40
Zuba mai ido tayi ganin lokaci ɗaya ya sauya a jiyar xuciya tayi tana so taga ƴa'ƴan sa tunani ta shiga yi
Ganin tayi shiru yace
"hajiyar mu lafiya kika shiga tunani?"
Fir gigit ta dawo hayyacinta tace
"bakomai tashi muje dinner ya kammala "
Badan yayarda bakomai SBD batun yau yake ganin hajiyar mu cikin tunaniba to koma mene zai tayata da addu'a komai ya daidaita yace
"TO, muje ko ya buɗe mata ƙofa yana murmushi bakowa ke ganin wannan tsadaddan murmushin a fusƙarsa ba wasuma cewa suke sa baka dariya sai hamma
Jamai kumatu tayi cikin salon tsokana tace
"Ooni yau she wannan yaron nawa zai girma ko sai Ka kawomin girlfriend din kane ?"
Kwabe fuska yayi kamar karamin yaro yace
"Please hajiyar mu mubar maganar girlfriend Dan Allah ya hada hannuwa biyu alamar rokonta "
huce shi tayi ta barshi tsaye tana nunamai alamun yanzu ta fara kenan ajiyar zuciya ya saki ya fito shima
Tuni kowa ya hallara shikadai ake Jira kujerah ya ja ya zauna ya dubi mahaifinsa mai cike da kamala da nusuwa kallo daya zakai mai kasan hutu da jin dadi ya zauna mai yace
"Abba barka da dare "
Cikin kulawa yace
"yauwa ya aiki?"
Kansa akasa yace
"Alhamdulillah"
Duban Dan nasa yayi yace
🐘Giwa in mun gama cin abinci ka sameni a babban floor
Da sauri ya dago ya dubi mahaifinnasa Allah isa ba wata magana da ta shafi rayuwarsa za aimai ba duk da yasan sarkin tone tone ba lafiya da kyar ya iya cewa
"To amma ba wanda ya fahimci halin tsaka me huyar da ya shiga sai hajiyar mu da abba domin sunfi kowa sanin halinsa mutum na ukku kuwa ko mutsi giwa yayi yasan me yake nufi wato jadda
murmushin gefan baki abba yayi hajiyar mu da take jinsu bata ce kala ba. ta dubi basma tace
Basma yi saving din mu
Tashi tayi tace
"To hajiyar mu cikin nutsuwa take bawa kowa abin da yake so kan giwa ta xo tsayawa tayi ta zuba mai ido domin tasan balalle bane yaci abinci me nauyi ba bakin ta na rawa tace
"Big brother me zan zuba maka? "
da ido yayi mata nuni domin maganar da abba yayi ya daga mai hankali dayake yasaba musu ta fahimci me zaici a zuciyarta kuwa cewa take
"duk wacce ta sake ta aure yayansu ta shiga ukkunta da fi'ili kala kala karkayi wannan wannan nake so ga tsari yawa mace
chips ta zuba mai kadan sai ta tsiyayome fresh milk me sanyi ta bashi
kallo ta yayi yace
"Thanks"
dayake tana kusa da shi ta ji me yace
"Kai ta gyadamai kawe tadauko bowl ta dauko ta zuba farfesun hanta komawa tayi ta zauna ta fara Ci"
ba ka jin sautin komai sai na chokali da a.c sosai kuwa ya nutsu yana cin abinci ban da musu'af wanda sai muzurai yake yasan sarai shirun yayan nasu ba alkhari bane ko fadan daya saba gwara yaji yayi ko zai sami salama domin zuwa yanzu yasan ansanar Mai da abin da ya aikata
Tissue ya dauko ya gige bakin sa ya mike
kan abba a kan kwanon sa yace
''naga ko rabi baka ciba ka tashi ?"
Abba nako shi
Sai a yanxu hajiyar mu ta ga da cewar tayi magana tace
Abban giwa ka manta my son rainon uncle bature ne ?"
Duban ta yayi yace
"Hakane na manta "
Kallo musu'af yayi ya juya ya fita kai tsaye shashin jadda ya huce sai da yayi tafiya me nisa tukunna ya nufi tamfatsaitsan shashin nasa yawa Bana tsohoba ga kayan mure rayuwa sallama yayi
aa me gidana ashe Kai ne yanzunnan muke zancan ka tsohowar matar ta fada kallo daya zakai mata kasan tsohowar yar boko ce
samin kusa da jadda yayi ya zauna ya dauki tufa ya faraci yace
"hmm ya kamata tsohowa tun huri ki nemi mijin ki kin ga yaro me jini ajika kin ce mijin ki "
Pillow case na luxury sofa din ta ta dauka ta jefa Mai tace
Ai kai yaran gidan nan sunkusa fara ce maka kaka tsoho duk kannan ka sunyi aure sun bar Ka
hmm ai aure lokacine ni nawa be zoba
Ta shi yayi daga kishin gidar da yayi ya gyara glass dinsa yace
Ungo sa'eed yayi masa da kuwa
aa bara in tashi yau rigimar tsofaffi ta tashi yana fadar haka ya miki
cikin karfin hali jadda ya jawo shi domin karfinshi yayi rauni hausawa sun ce jiya ba yau....
La aboki bara in zauna kar in karyawa wa su uncle bature tsoho
dariya dadtijon tsuhon yayi duk gashin shi yayi fari amma duk da haka yana cikin hayyacin Shi yace
hmm da baka zauna ba da na karya ka
kai ya jinjina yace
Uhmm tsohon alkhali nan fa ba reburin Shari'a bane
tuni giwa ya motso mai wani abu aransa kalla ta taro a idonsa ya Kamo hannusa yace
"Sa'eed Dan Allah ko bayan raina kane mota ka bata hakuri wallahi kullun da maganar da ta fadamin da ita nake kwana duk da alokacin yarinyar jaririya ce amma wallahi ko yau na ganta zan gane ta sa'eed wannan shine kuskuran danayi bazan taba mantawa da shiba wannan shine tabon da dangin giwa yake da shi amma bakowa ya sani ba sa'eed a gaban ka akai komai sai de kai yarone ba komai zaka fuskanta alokacin ba muntafi mun barta tana kuka duk irin tausayina ban tausamata ba ban cika adalin shugaba ba"
goge masa kallar idonsa yayi yace
"ban taba ganin jajircaccan alkali be Ka mata Dan kayi kuskure daya kadamu kanka ka dinga jawowa kanka ciwo"
hmmmm sa'eed kenan
Cikin i don't care yace
wallahi sa'eed sa'eed sa'eed a kwai lokacin da zan baka mamaki inhar ba kai aure ba a cikin kannan ka zan zabo yarinya karama in hadaku aure da ita kuma kasan dangin giwa ba saki ba yaji
Da sauri ya dubi kakan nasa yasha farar shadda gashi ya tsofa amma zuciyar mazan jiya tana nan sosai yake mamaki rikidiwar kakan nasa cikin karfin hali yace
Jadda komai fa lokacine
Wallahi ina bayanka mijina
to ai daman haka zaki ce ba tunyau nasan bakin ku daya da jadda ba na tafi
muryar abba yaji yace
"Tsaya muyi maganar anan ba sai munje floor na ba "
tambas yau ya shiga tsaka me huya ga wayannan tsofaffin ga abba fita ta sai Allah jikin sa asanyaye ya koma ya zauna
wannan kenan
hello abbie dazu ka kirani mun fita nida Laila kakan su ba lafiya ban Sami damar dagawa ba
ayya kice ina yi masa sannu
Laila Abbie nayiwa jadda sannu
what fanna me kika ce kamar na taba jin sunan mutumin nan amma a American tuni zufa ta karyo mai anya komai baya Shirin tunuwa ba
Wata kila Abbie ai babban mutun ne ae
Da kyar ya iya saita nutsuwar shi yace
"Okay"
lafiya naga muryar ka ta canza?"
na tashi da murane
Allah ya baka lafiya
"Ameen"
Abbie yakuke ina nana ta take ?"
my princess yau aikin kwana nake kowa lafiya ya karatu ?"
Alhamdulillah Abbie
"To, kiyi karatu sai anjima ko banda tsokana
Nide nide kullun ka dinga yimin kallon matsokaniya
Hmm nasan halinki mamana tunkina yarinya a kula banda saurayi
Turo dan karamin bakinta tayi kamar yana ganinta tace
"To
Okay ahuta lafiya bye
Bye
lumshe idanuwanta tayi tace
"Laila wani zubin nakance nafi kowa sa'ar mahaifi yana sona "
Laila da ta zuba mata ido tace
Uhmm gaskiya kam wallahi kinyi dace we fanna yawa a India na ganki a jikin giwa wow hadin zaiyi kyau kinga ke kina da haske sosai shi kuma Ethiopian color ya'yan da zaku haifa sai an kallesu an kara wallahi
tuni wani bakin cikin ya tokare mata zuciya tace........✍🏼
🚴♀️🚴♀️ Topa me ke shirin faruwa ne
RASHIN SANI
By
Oum yasmeen
Chapter 41-50
"Lailah lailah lailah ki fita a idona in rufe ƙwafa tayi ta koma ta kwanta ta dauki wayar ta tana game,
Dariya lailah tayi tace
"Iyeee kin ji Hausa to na fito rufe idonki ta Giwa ,
Pillow cases ta ɗauko ta dinga jifanta da shi sosai lailah take dariya ganin ta kusan cin mata yasa ta buɗe kofa aguje ta fita tana dariya juyowa tayi jin ance
"Lailah Giwa ,
Tace
"Na'am najuwa bauchi yakike yau ke ce a hostel din mu ?"
Eh Wallahi nice nazo gun Fatima bichi ne
Okay ina tayi murna kin kusan barin S.D Giwa midwifery and nursing Wallahi ji nake dama nice zaki koma gida duk wani abu da ake a family ban da kai Wallahi bana jin dadi
Dariya tayi tace
"Kamar yau ne kema haka zaki ga kin gama nifa Wallahi ji nake ranar Monday Giwa midwifery and nursing tayi min kadan saboda murna amma ta wani fannin bana jindadi zan bar abokanan arziƙi ina fanna ?"
Wallahi zan can ki gaskiya domin nima ina tunanin ranar rabuwar mu da fanna tana ɗaki ita tama koroni
Okay ki gaishe mun da ita hmm me hali baya fasawa in kuna abu yawa yara
Zata ji insha'Allah Wallahi najuwa bauchi bakisan fanna ba
Mayafin ta ta gyara tace
"Gani nake duk ke ce da laifi shi yasa ta koroki fanna da take silent ba ruwa ta da magana ,
Hmmm kawe Laila ta ce
ganin ta tafi room 7 yasa itama ta shiga ɗakin su
Sosai hankalin ta ya tashi ganin fanna ta zuba ta gumi da sauri ta ƙarasa bakin gadon ta tace
"Fanna lafiya naga kin zuba ta gumi ?"
A jiyar zuciya ta sauke tace
Lailah mun shiga ukku na ɓallo ruwa
Gu ta samu ta zauna tace
"Ban gane kin ɓollo ruwa ba fahimtar dani ?"
jiki a sanyaye tace
Giwa yana ne mana yan zunnan naga an sa agroup na chemistry kinga reg number bata fa
Da sauri ta amshi wayar zaro ido tayi tace
"To ai naga test ɗin ba shi ne yayi mana ba sir David ne kuma ai mun cinye to me hakan ke nufi ?"
Lailai nima ban sani ba to Allah ya kai mu gobe sai ki raka ni inje gunsa Wallahi yau watana biyu da fara makarantar nan hanyar ofishin sa ma ban sani ba
Ni na sani yana kusa da lab biology
Ajiyar zuciya ta sauke tace
Wallahi Allah yana gani ba halittar da nake tsoron haɗuwa da ita irin Giwa bana so duk wata sabgar da zata hadani da shi ayi fusƙar mutum yawa hadari saboda haɗe rai ba annuri Wallahi Inna Ganshi gabana har waɗuwa yake Dan Allah du beshi yawa basamude saboda tsayi da kiba
Ajiyar zuciya lailah ta sauke tace
"Ke ba ke kaɗai ba kike jin tsoron Giwa,
Wannan kenan
Giwa dazu tsohon ministan manfetur ya samene a office ɗina a kan zancan ka da yar sa
Tuni gumi ya wanke shi da kƴar ya buɗe baki ya ce
Abba jadda Wallahi ko kadan ba zan iya rayuwar aure da Rumaisa ba tarbiyar ta da tawa ba ɗaya ba Abba ku ga farceni insha'Allah na kusan kawo muku surukar ku yanzu ina wani binki ce akan ta
Shiru Abba yayi domin shi a abun na Giwa anya ba aljana ce ta aure shi ba duba ga irin lalurar da take tare da shi a lokacin sun tafi hutu Germany cutar ta same shi yana da shekara goma sha takwas likitoci sun mai gwaji to shine zai ci gaba da addu'a Allah ya tsaremai imanin ɗan sa dama al'ummar musulmi Allah ya kare shi daga sharrin shaidan
Jadda yace
Amma Kasan iya daga kafa mun ma ko da za kace ba ka yarda da tarbiyar taba kai ma naga girman Turaine ko
Ƙasa yayi da idonsa be ce komai ba
Giwa ta shi ka tafi
Da sauri ya tashi ganin bakin tsohowa yana magana da alama wani abu zata ce
Bayan ya bar shashin jadda shashin sa ya nufa sai da ya gama gabatar da uzurin sa sannan ya dauki waya bugu ɗaya aka dauka yace
"Ka sameni a shashina "
Kitt ya kashe
Basma na shiga ukku big brother yana nema na
Hmmm lalle kana cikin matsala.......✍🏼
RASHIN SANI
By
Oum yasmeen
Chapter 51-55
Mussa'af shiru yayi yana lalibo mafita domin yasan Wallahi haɗuwar su da Giwa ba dadi
Wata uwar dariya Ihsan ta fara harda ruƙe cikin
A fusace ya biyo ta aikuwa ta zuba aguje ta bar shashin su baki ɗaya mom aysha mom aysha kinga yaya mussa'af ko
Wata mata nagani akalla zata kai shekara talatin taci ado da wani haɗaddan leshi pink colour anme adon flower blue saai ƙamshi take zubawa da sauri ta rumgume ihsan tace
"Haba mussa'af me yasa kullum kana girma kana ƙara shiga dawa mu da muke shirinyin yar gida ,
Saƙar baki yayi yana kallon ta
Cikin tora haushi tace
"Kaga yarinya kyakkyawa san kowa ƙin wanda ya rasa shine ka ta kurawa rayuwar ta to Ni de bazan bayar ba sai nasa mutum kuka babyn zo mu zauna ta kamo hannunta ta zaunar da ita a sofa ,
Shi kuwa mussa'af rasa bakin magana yayi ya ja ƙwafa yace
Mom aysha wa zai aure lukutar yar ki kiyi addu'a Allah yasa ta samo lukuti irinta amma ina ni ina jimgegiya amma bara in dawo daga kotun Shari'a ta Giwa zan zo mu zauna a samo muku mafita
Wani uban ihu ta saki tana buga ƙafafu tace
Mom aysha bakin ce adena ce min lukuta ba
Babyn kƴale shi we burin kunya yake yi
Hannu ya yarfa yace owo ku ta shafa Ni na tafi
Uncle sulaiman ne ya fito yace
"Habibty kamar Muryar mussa'af nake ji daman be koma makaranta ba ?"
Eh shine ya biyo min babyn Wallahi lamarin su har dariya yake bani yawa masu ganin hanjin juna shi girman kai ita tsoka na
Allah ya kyauta
"Ameen"
Uncle sulaiman ina huni
Lafiya qalau ihsan
Uncle ina my boy
Yana barci
A guje ta tashi zata ta doshi
Da sauri mom aysha ta sha gaban ta tace
Babyn bacci yaron ki yake ki bari inya tashi zan kawo miki shi
Zun ɓuro baki tayi tace
Zan faɗawa ya Giwa ya samo min jariri a asibitin shi tunda kullum hanani naki kike
Duban uncle tayi tana dariya tace
Ihsan kenan mala'ikan yara honey kaji abin da take cewa
Hmm so take a kama su ita da Giwa a Ina