Showing 66001 words to 69000 words out of 114708 words

Chapter 23 - TUBALI book 2 complete hausa novel

18 Sep 2024

19345

cikin dan yanayin tausayawa yace.

“Haba Rayyern Meyasa kakeson yin wasa da lafiyarka? kasan yanda ciwon nan keyi maka idan ya tashi, please dan Allah kana kiyayewa, kasani bawai kai kad’ai kake da buk’atar lafiyarka ba, su Abba da Mamy suna da buk’atar ka, can you imagine yau ace bakanan, mekake tunanin zai faru? bana fatan haka Rayyern Dan Allah kana kulawa da kanka, yanzu tunda yau mun fito da wuri kaje pharmacy ka saya maganin.”

Kai Rayyern din ya jinjina kawai, tare da mikewa tsaye, batare daya sake cewa komai ba kaitsaye ya nufi wajen motarsa.

Ganin hakanne kuma yasa Dr. Sulaiman had’a sauran Doctors dinsu, suka tare taxi dan komawa masaukinsu.

Rayyern kuwa yana shiga cikin motar yayi mata key, kaitsaye wani babban pharmacy dake gefen Hospital din ya nufa, Koda yaje bai samu maganin nasa ba, saidai sunyi masa kwatancen wani pharmacy, wanda suke da tabbacin cewa zai iya samun maganin idan yaje can.

Agajiye sosai yakejin kansa shiyasa bai iya jurewa, tafiyanba kaitsaye restaurant ya biya ya saya abinci, saboda yunwa yakeji sosai.

Isowarsa gidan kenan yana gama dai-dai-ta parking din, motar ya fito hannunsa rike da ledan abincin da kuma suit d’insa, ya nufi cikin gidan.
Ahaka ya shigo falon da cikinsa ya riga ya d’an d’auki dumi, saboda na’urar d’umama d’aki da Jannart din ta kunna.

Ahankali ya zauna akan kujera, tare da bud’e ledan abincin, take away d’aya ya ciro tare da bud’ewa, Ahankali ya d’auki spoon tare da Kai loman abincin bakinsa.

Idanunsa ya d’an rumtse tare da ajiye spoon din, kana ya maida jikinsa ya kwantar, Hannunsa na dama ya d’aura akan cikin nasa dake ciwo, domin zuwa yanzu ciwon nata k’ara tsumuwa...!






By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:53 - 🥰🥰: K’asa kafun Idanunta sukai ga jikin nasa ne kuma, yayi saurin k’arasa jawo boxer din nasa jikinsa.
Wanda hakan yasa ba taga privet part din nasa ba.

Jannart kuwa ganinsa haka babu riga da tayi ne, yasa ta saurin juyawa tare da rumtse Idanunta, saboda bata saba Ganin Namiji haka agabanta ba.

Rayyern din kuwa Ganin Jannart din ta juya ne, ya sashi d’an lumshe idanunsa tare da kama k’ugunsa, cikin muryarsa dake nuna gajiya yace.

“Bani.”

Hannunta dake rik’e da wayan ta mik’o masa, batare da ta juya Idanunta ta kalleshi ba.

A kokarin ta na mik’a masa wayarne kuma, Hannunsu suka hade awaje daya.
Wani irin sanyi taji acikin tafin hannunta, wanda hakan yasa ta d’an janye hannun nata baya, saboda ba zata iya jurewa hakan ba.

Shid’inma kuma Rayyern hakan yayi, zare hannunsa daga kan nata hannun yayi, tare da karb’an wayar ya kara akan kunnensa, ahankali kuma cikin sanyin murya irin ta mararsa lafiya yace.
“Abbana.”

Daga can b’angaren Abba ya d’an saki murmushi, cikin tausayawa da kuma k’aunar Rayyern din yace.

“Na’am Rayyern ya jikin naka?”

Idanunsa ya d’an lumshe, kana ad’an kasalance yace.

“Da sauki sosai Abba Ina Mamy da Ramadan.”

“Duk suna lafiya, nasan anjima zasu kiraka”.
Ba tare da ya bari yace komai ba ya kuma daurawa da cewa.
“Dan Allah Rayyern kana kulawa da kanka, kada kana yawan wasa da magungunan da aka baka, yanzu irin yanda ciwon nan naka ya tashi, inda ace babu Jannart akusa dakai da yaya kake ganin abun zai kasance? Dan Allah kana kulawa da kanka kaji Rayyern.”

Abban ya fadi haka cikin tausasawa.

Rayyern din kuwa jin abunda Abban ya fad’ane ya sashi sake lumshe idanunsa.
Yayinda acikin zuciyarsa yake maimaita sunan Jannart.

Jannart dake tsaye kuwa Ganin yanda ya lumshe idanunsa, batare kuma da ya saka kaya ajikinsa bane, yasa ta d’an kalli saman chest d’insa, inda kwantattun gargasa suka k’awata wajen.

D’an d’auke idanunta daga kallonsa tayi, kana ahankali cikin tafiyarta na nutsuwa ta juya ta nufi hanyar fita daga d’akin.

Jin takun tafiyarta ne kuma yasa Rayyern din bud’e idanunsa ya sauk’esu akan bayanta.
Yanayin yanda hips dinta ke motsawa ya kalla, lokaci daya kuma yayi saurin d’auke idanunsa, saboda yanda shape din hips din nata ya bayyana sosai, kasancewar kayan da ta saka yabi jikinta.

Abba kuwa jin Rayyern din yayi shiru ne, yasa shi katse wayar ta hanyar cewa, zai kirasa anjima.

Rayyern kuwa dama hakan yakeso, saboda har yanzu bashi da wani karfin yin magana.

Ahankali ya sunkuyo tare da d’aukan kayan da Jannart din ta ajiye masa.
T-shirt ne da kuma dogon wando irin mai yawan aljihun nan.
Ahankali ya zura wandon ajikinsa, bayan ya saka t-shirt dinne kuma, ya d’an saka hannayensa duka biyu ya d’afa bango.
Saboda wani irin jiri da yakeji, gaba d’aya kwata kwata jikinsa babu k’wari.

Bayan ya d’an huta ne kuma ya soma sauk’e numfashi akai-akai, tare da hawa kan sallayan da Jannart din ta shumfud’a masa ya tada Sallah.

Ab’angaren Jannart kuwa tana fita daga d’akin Rayyern din, kaitsaye d’akinta ta wuce, kayan dake jikinta ta rage, cikin d’an kuzarin da take dashi kuma ta shige bathroom dan had’awa kanta ruwan wanka.

Sanin da tayi kuma cewar gari ya soma haske ne, yasa bata wani b’ata lokaci awajen wankan ba ta fito.

Wani d’an k’aramin towel ta d’auka, ta tsane jikinta, tare da shafa body lotion ajikin nata, kana ta fesa sassanyan turarenta mai dadin kamshi, dangane da kwalliya kuwa powder kawai ta shafa akan fuskarta, sai kuma lipsgloss mai d’an shek’i.

Ahankali ta k’arasa wajen trolley dinta, tare da bud’ewa ta zaro wani had’add’en doguwar rigar engilsh wears, sai kuma hulan sanyi irin wanda ta saba sawa.

Koda ta zura rigar ajikinta d’as tayi mata, saidai duk da cewar rigar bata da tsawo sosai, amma tayi mata kyau ajiki, hulan ta saka akanta tare da d’aukan hijab mai girma ta saka.

Bayan ta shumfud’a sallayane kuma ta tada Sallah.

Adai-dai lokacin kuma Rayyern ke idar da nashi sallan, bayan ya d’anyi addu’o’i da azkhar ne kuma, ya gyara zamansa akan sallayan tare da maida kansa, ya jingina da jikin drawer.

Idanunsa ya d’an lumshe ahankali, acikin zuciyarsa kuwa yana me tunanin maganganun da Abba ya fad’a masa, har zuwa yanzun kuwa moment din daren jiyan ya kasa fita daga cikin tunaninsa, domin aduk sanda ya tuno da sautin kukanta, sai yaji tsikar jikinsa na tashi, zuciyarsa kuwa haka zata shiga bugawa da sauri.

Ga kuma wani irin shegen kasala da yakeji, musamman akan abunda tayi masa d’azun, har yanzu jin marar tasa yake wani iri, Yayinda penis d’insa ke maaifar harbawa, tamkar Wacce take fitar da numfashi wanda hakan ya kasance mishi bakon yanayin da bai san dashi ba idonshi ya lumshe sabida duk sanda ya tuna sai yaji wannan harbawar.

Ahankali Jannart din ta mik’e tsaye, bayan ta idar da sallah tare da sa hannu ta zare hijab din dake jikinta, baby pink jacket ta d’aura akan kayan nata, kana kaitsaye ta fice daga d’akin, tana me nanata fad’ar.
“Hasbiyallahu la’ila ha illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim.”

Koda ta fito falo ledodin abincin da Dr.Sulaiman ya kawo mata ta bud’e, tare da zaro takeways din ta soma bubbudewa, Ganin duka abincin babu wanda ya b’aci ne, yasa ta d’aukan ledodin ta nufi kitchine.

Acikin plate ta juye chicken pepper onin sauce, da kuma saurce na liver sai kuma pancake, wanda aka yi masa gashi na musamman.

Warming abincin tayi bayan ta kammala ne kuma ta had’a musu coffee,

Acikin wani d’an tray ta saka musu abincin, kaitsaye ta nufi d’akin Rayyern din.

Ahankali ta tura kofar d’akin ta shiga, bakinta d’auke da sallama.

Jin motsin shigowarta ne kuma yasa, Rayyern din bud’e idanunsa, Ahankali kuma ya d’ago kansa ya kalleta.

Kyakkyawan shigan da tayi da kuma fuskarta ya zubawa idanu, wanda kuma tun kafun ta k’araso k’amshinta ya riga daya cika masa hanci.

Jannart kuwa cikin nutsuwa ta k’araso inda yake zaunen, batare da ta lura da irin Kallon da yakeyi mata ba.

Ahankali ta d’an durk’usa ta ajiye tray din agabansa, kana itama ta zauna tare da tank’washe k’afafunta, sai alokacinne kuma ta d’ago idanunta ta kalleshi.

Karab kuwa idanunsu suka had’e acikin na juna, saboda har yanzu Rayyern din kallonta yakeyi.

“Ina kwana.”
Ta fad’a tana meyin k’asa da Idanunta.

“Lafiya.”
Ya amsa mata asanyaye tare kuma da janye idanunsa daga kallonta.

Itakuwa Jin alamun ya daina kallonta ne, yasa ta d’an gyara zamanta, tare da d’agowa ta kalleshi, tray din abincin ta sake turowa gabansa, kana cikin d’an yin k’asa da murya tace.

“Naan ga abinci kaci sai kasha magani.”

Bud’add’un idanunsa ya lumshe, tare da fesar da numfashi ahankali, saboda Jin yanda sautin muryarta ke fita, yasa duk yaji tsikar jikinsa ya tashi.

“Nakoshi.”
Ya fad’a ta hanyar motsa y’an k’ananan lips d’insa.

Jin hakan ne kuma yasa Jannart din d’agowa, ta kallesa da sauri, lokaci d’aya kuma ta kwab’e fuska.

“Please Naan kaci abincin please.”

ta fad’i hakan tana me langwab’ar da kanta gefe.

Lips d’insa ya dan cije saboda, yanda yaji tayi maganan tamkar Wacce take tsokalo wani abu daga sashi na jikinsa, akaro na farko kenan da yaji sautin muryarta na neman zautar dashi, abunda bai tab’aji ba arayuwarsa.

“Banajin yunwa.”
Ya sake fad’a atak’aice saboda bashi da wani k’warin jiki.

“Please ko coffee kasha.”
Jannart din ta fad’i haka cikin tausasawa.

Jin hakan da yayi dinne kuma yasa shi, d’an ya motsa fuska, tare da mik’a mata hannunsa alaman ta bashi cofin coffee din.

Da sauri kuwa ta mik’a masa kofin, Ganin da tayi ya soma shan coffee din ne kuma ya sata tashi, Anutse ta cigaba da tattare masa d’akin, bayan ta kammala ne kuma ta wuce falo, magungunansa ta d’auko tare da dawowa cikin d’aki’n.

Kallon yanda yake sipping coffe din ahankali tayi, yanayin yanda bakinsa ke d’an motsawa ne, yasa ta jin wani iri ajikinta.
Ahankali ta k’araso inda yake zaunen.
Zama tayi agefensa tare da d’ago Kanta ta kalleshi.

“Naan.”
Takira sunanshi da wata irin unique voice, dinta Wacce tasa duk wani gargasan jikinsa mikewa.

Idanunsa ya kuma lumshewa, tare da Dan motsa bakinsa saidai bai iya amsa mata ba duk da zuwa yanzu ya gama fahimtar sunan data raɗa masa kenan (Naan) ya kuwa gane ƙarshen sunansa ta ƙawata ta bashi kekkyawan lafazi.

Ita kuwa Jannart dama bata damu daya amsa mata ba, plate din abincin ta d’auko tasa akan cinyarta, cikin dan tausasawa hadi da shagwab’a tace.

“Please Naan kaci abinci, ko kad’annne, kaga babu kyau mutum yasha magani batare dayasa komai acikinsa ba, coffee bazai rik’e ka ba, please Hamma Nanu karkace a’a.”

Ta k’are maganar tana me Kallon fuskarsa, tare kuma da karyar da wuyanta gefe.

Akasalance ya bud’e idanunsa ya kalleta, Ganin irin Kallon da yakeyi mata dinne kuma ya sata mik’a masa plate din.
Babu musu kuwa ya karb’a, saidai bawai Dan yanajin zai iya cin abincin ba, pancake d’aya ya d’auka yasa abakinsa, tare da soma taunawa Ahankali.
Idanu Jannart din ta zuba masa, domin daga Ganin yanda yake tauna abincin bayajin dadin bakinsa.

Amma duk da hakan taji dadi daya karb’a yaci, saboda magananin zaifi saurin yi masa aiki.

Lomansa biyu kacal ya zare hannunsa, tare da daukan tissue ya goge hannun sa.
Akasalance ya d’ago oily eyes d’insa ya kalleta.

“Jannah Nak’oshi.”
Ya fad’a yana me sake gyara zamansa.

Murmushi tayi tare dasa hannu ta karbi plate din, magungunansa dake hannunta ta b’are hade da daukan goran ruwa ta mik’a masa.
Babu musu kuwa ya karb’a yasha.

“Muje ka kwanta.”
Ta fad’a tana me mik’ewa tsaye.

Tare da mik’a masa hannunta alaman ya kama.

D’an Kallon hannun nata yayi, kamar bazai kama ba kuma sai ya cije labbansa, tare dasa hannun nasa acikin nata, Ahankali ya Mike tsaye bisa taimakonta.

Ganin ya tsaya ne kuma ya sashi zare hannunsa acikin nata, tare da d’an matsawa ya kwanta akan gado.

Kusan Atare suka sauke sassanyar Ajiyar zuciya, shida Jannart din, saidai kuma kowannensu da manufar sauke tasa Ajiyar zuciya.

Fararen tafin k’afansa ta zubawa ido, Yayinda shikuwa ya maida nasa idanun ya lumshe.

Dai-dai lokacin kuwa kunnuwanta suka soma jiye mata knocking kofar falon da akeyi.

D’an kallonsa tayi ganin ya rufe idanunsa ne kuma yasa kaitsaye ta nufi falon.

Ahankali ta daura hannunta akan handle din kofar tare da budewa.

Dr. Sulaiman da kuma su Dr. Sadiq ne tsaye, abakin kofar shigowa falon, ganinsu da tayi dinne kuma, ya saka ta sakin murmushi, kana cikin sakin fuska tace.

“Bismillah ku iso sannnunku da zuwa.”

“Yauwa Jannart.”
Dr. Sulaiman ya amsa mata shima fuskarsa d’auke da murmushi.
tare kuma da yiwa sauran Doctors din jagora, suka karasa shiga cikin falon.

Anan cikin falon suka zazzauna.
Yayinda Jannart kuwa Kai tsaye kitchine ta wuce, inda ta kawo musu ruwa da drinks.

Amutumce suka gaisa da sauran Doctors din, bayan sun gaisa dinne kuma Dr. Sulaiman ya kalli Jannart din, Cikin kulawa yace.

“Ya mai jikin, Ina fatan babu wata sabuwar matsala da ta kunno ko.”

D’an murmushi tayi tare dasa hannu, ta gyara zaman jacket din dake jikinta, murya asake tace.

“Jikinsa Alhamdulillah, tun jiya daya sha maganin dai ciwon bai sake tashi ba.”

Kai Dr Sulaiman ya jinjina, cike kuma da samun gamsuwa yace.

“Masha Allah ai haka akeso, amma daren jiyan ya samu bacci kuwa?”

“Eh ya samu, yanzu ma yana kwance inaga baccin zaiyi, but bari nayi mishi magana.”

Ta fad’a tana kokarin mikewa tsaye.
Saurin dakatar da ita Dr. Sadiq yayi, ta hanyar cewa.

“No basai kin taso sa ba, zamu dawo anjima da yamma nasan zuwa lokacin ya sake samun k’arfin jikinsa, ga wannan mu zamu wuce wajen aiki.”

Ya k’are maganan yana me ajiye wata babban ledan restaurant dake hannunsa.

Ganin hakanne kuma yasa sauran Doctors dinma duk suka mik’e.

“Mungode sosai.”
Jannart din ta fad’a, tare da taka musu har bakin kofar fita daga falon.

Saida taga tafiyarsu kuma kafun ta dawo ta zauna, ledan da Dr. Sadiq din ya kawo ta bud’e, tare da ciro takeway daya na African dishes ta soma ci.

Bata wani ci sosai ba kuwa ta ture abincin gefe, tare da daukan bottle water tasha ruwa, sauran ragowan abincin ta Kai kitchine.

Kana ta dawo kaitsaye ta wuce d’akinsa.

Ahankali ta murd’a handle din k’ofar ta shiga bakinta d’auke da siririyar sallama.

Yana nan kwance kamar yanda ta barshi, Yayinda kuma har yanzu idanuwansa ke lumshe.

Ahankali ta k’araso jikin gadon, tare da matsowa inda yake kwance.

Kyakkyawar fuskarsa ta zubawa ido, bata ko kyaftawa, daga gefe guda kuwa anutse kunnuwanta, ke jiye mata sautin fitar numfashinsa.

“Yayi bacci.”
Ta fad’a abayyane cikin kuma sanyin murya, yanda tasan bazai jiyota ba.

Zama tayi ad’an gefen gadon,
tare da d’aukan hannunta na dama, Ahankali ta kife tafin hannun nata akan goshinsa.

Wani irin b’oyayyar ajiyar zuciya ya sauke, tare kuma da d’an motsa hannunsa batare da ya bari taga hakan ba.
Taushi da kuma laushin hannun nata, hadi da daddad’an kamshin turarenta, shiyasa shi jin wani iri acikin jikinsa.

Itakuwa Jannart sanin da tayi cewar bacci yakeyi, shiyasa ta sauko da hannunta ahankali zuwa kan lallausan sajensa, wanda daga jiya zuwa yau take matukar jin dadin tab’ashi.

Ahankali ta d’an shafa sajen nasa, tare da lumshe Idanunta cikin sanyin murya tace.

“I pray wish you quick recovery Naan, soon zaka samu sauki Insha Allah, then babu wata cuta da take d’aurewa aduniya, you’ll be okay Insha Allah Naanu.”

Ta k’are maganan tana me gangaro da hannunta, kan wuyansa, tare da tura yatsun hannunta acikin wuyan rigar sa, wanda kuma hakanne ya bata daman jiyo sautin bugun zuciyarsa.

Idanunta ta lumshe ahankali, hade da sake saukar da hannunta k’asa, har ta iso kan mararsa.

Lallausan tafin hannunta ta kife akan mararsa, cikin kuma tsananin tausayinsa da takeji, murya araunace tace.

“I’m sorry Naan ai nasan zakaji sauki, maranka zai daina daurewa haka ma cikinka zai daina ciwo, so Sorry.”

Ta fad’i hakan ashagwab’e, tare da soma d’an shafa masa saman marar, wanda kuma ta nayin hakanne, da tunanin bacci yakeyi.

Shikuwa Rayyern saukan dumin tafin hannunta akan D d’insa, ba k’aramin tayar masa da tsikar jiki yayi ba, saboda yakanji hakanne amatsayin wani salo na musamman, sannan yakanji kansa acikin wani irin yanayi a duniya ta musamman.

Idanunsa ya d’an rumtse da k’arfi, tare da fusgar numfashin da ke neman k’wace masa.

Allah yasani bai tab’ajin irin abubuwan da yakeji ayanzun ba.
Musamman Idan hannunta na yawo asaman marar tasa, yakanji duk wasu jijiyoyi dake jikinsa sun motsa, haka ma Rayyern d’insa da yakejin na harbawa.

“Yah Salam.”
Ya fad’i haka acikin zuciyarsa, Yayinda abayayyane kuwa ya fesar da wani irin zazzafan numfashin da yasa Jannart din ta d’ago ta kalleshi.

“Naan.”
Ta d’an kira sunansa ahankali, tare kuma da zare hannunta dake kan marar tasa.

Duk da cewar ya jiya amma sai yayi shiru bai amsa taba.

Itakuwa Jannart shirun da yayi dinne, yasa ta tashi daga kan gadon.
Ahankali taja blanket ta rufe masa jikinsa.

Kana ita kuma ta koma k’asa nan kan carpet ta zauna.

Rayyern kuwa jin da yayi Jannart din tabar kusa da shi ne, yasa shi sauke Ajiyar zuciya, tare da d’an gyara kwanciyarsa, ta yanda ba zata sake samun daman tab’a saman marar tasa ba, domin yayi imani Idan taci gaba dayi masa hakan, zata iya d’aid’aita tunaninsa da nitsuwarsa dama rayuwarsa gaba ɗaya ya tabbata yana gab da sakin kuka idan har zatake sashi cikin wannan yanayin.

Jannart kuwa Koda ta zauna akan sofan, wayarta ta d’auka tare da soma latsawa.

Tana nan zaune kuma wayarsa ta soma k’ara, da sauri ta jawo wayar tare da saka ta a silent saboda, batason karan wayar ya tashe sa daga baccin da yakeyi.

Wani kiran ne ya kuma shigowa, cikin wayar tasa Ganin da Tayi sunan Riyyam na yawo, akan screen din wayarne kuma, yasa ta picking call din, tare da kara wayar akan kunnenta.

Daga can b’angaren Riyyam kuwa jin anyi picking call dinne, ya sashi gyara zama tare da cewa.

“Hamma Rayyern.”

Ajiyar zuciya Jannart din ta d’an sauk’e, kana murya ad’an sanyaye tace.

“Riyyam.”

“Na’am Aunty Jannart ya jikin Hamma Rayyern, yanzu Yah Ramadan yake fadamin wai jikin Hamma Rayyern ya tashi sosai jiya, Dan Allah ina yake ya jikin nasa kuma, Ina fatan dai ya samu sauki.”

Riyyam’n yayi mata duka tambayoyin, alokaci daya kuma cikin dan yanayi na rudewa.

Jin yanayin Riyyam dinne kuma yasa, Jannart sakin ranta, cikin son kwantar masa da hankali tace.

“Jikinsa da sauki Riyyam, yanzu haka ma ya samu bacci, saidai jiya na tsorata sosai Riyyam, naji tsoro kada ya mutu barni a wannan duniya da ban san kowaba.”

Ta fad’i hakan hawaye na cika mata idanu, lokaci daya kuma duk wani raunin ta ya bayyana.

Riyyam kuwa jin abunda ta fad’ane yasa jikinsa, yin sanyi asanyaye yace.

“Allah ya k’ara sauki, duk hankalinmu ya tashi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login